< Farawa 23 >

1 Saratu ta yi shekara ɗari da ashirin da bakwai a duniya.
And the life of Sarah came to be, a hundred and twenty-seven years, —the years of the life of Sarah.
2 Ta rasu a Kiriyat Arba (wato, Hebron) a ƙasar Kan’ana, Ibrahim kuwa ya tafi ya yi makokin Saratu, yana kuka saboda ita.
And Sarah died in Kiriath-arba, the same, is Hebron in the land of Canaan, —and Abraham went in to wail for Sarah and to weep for her.
3 Sai Ibrahim ya tashi daga gefen matarsa da ta mutu, ya yi magana da Hittiyawa. Ya ce,
And Abraham rose up from over the face of his dead, —and spake unto the sons of Heth, saying;
4 “Ni baƙo ne, kuma baƙo a cikinku. Ku sayar mini da wani wuri yă zama wurin binnewa a nan, domin in binne mataccena.”
A sojourner and settler, am I with you, —Give me a possession of a buryingplace with you, That I may bury my dead, from before me.
5 Hittiyawa suka ce wa Ibrahim,
And the sons of Heth answered Abraham, saying to him:
6 “Ranka yă daɗe, ka saurare mu. Kai babban yerima ne a cikinmu. Ka binne mataccenka a kabari mafi kyau na kaburburanmu. Babu waninmu da zai hana ka kabarinsa don binne mataccenka.”
Hear us, my lord! A prince of God, art thou in our midst, In the choice of our buryingplaces, bury thy dead, —Not, a man from among us his, burying-place, will withhold from thee, from burying thy dead.
7 Sai Ibrahim ya tashi ya rusuna a gaban mutanen ƙasar, wato, Hittiyawan.
And Abraham rose up, and bowed himself down to the people of the land, to the sons of Heth;
8 Ya ce musu, “In kuna so in binne mataccena, sai ku ji ni, ku roƙi Efron ɗan Zohar a madadina
and spake with them, saying, —If it is with the consent of your minds that I should bury my dead from before me, hear me, and intercede for me, with Ephron son of Zohar:
9 domin yă sayar mini da kogon Makfela, wanda yake nasa, wannan da yake a ƙarshen filinsa. Ku ce masa yă sayar mini a cikakken farashi, yă zama mallakata domin makabarta tsakaninku.”
That he would give me, the cave of Machpelah, which pertaineth unto him, which is within the bounds of his field, —For full silver, let him give it me in your midst, For a possession of a buryingplace.
10 Efron mutumin Hitti yana zaune a cikin mutanensa, sai ya amsa wa Ibrahim a kunnuwan dukan Hittiyawa waɗanda suka zo ƙofar birni.
Now, Ephron, was sitting in the midst of the sons of Heth, —so Ephron the Hittite responded to Abraham, in the ears of the sons of Heth, even all that were entering the gate of his city, saying:
11 Ya ce, “A’a, ranka yă daɗe, ka ji ni, na ba ka filin, na kuma ba ka kogon da yake cikinsa. Na ba ka shi a gaban mutanena. Ka binne mataccenka.”
Nay, my lord, hear me, The field, have I given to thee And, the cave that is therein, to thee, have I given it, —In the eyes of the sons of my people, have I given it thee Bury thy dead.
12 Ibrahim ya sāke rusuna a gaban mutanen ƙasar
So Abraham boweth himself down, before the people of the land:
13 ya ce wa Efron a kunnuwansu, “Ka ji, in ka yarda. Zan biya farashin filin. Ka karɓa daga gare ni don in iya binne mataccena a can.”
and spake unto Ephron in the ears of the people of the land saying, Only if, thou, wouldst, hear me, —I have given the silver of the field Take it of me, That I may bury my dead here.
14 Efron ya ce wa Ibrahim,
And Ephron responded to Abraham, saying to him,
15 “Ka saurare ni, ranka yă daɗe; darajan filin ya kai shekel ɗari huɗu na azurfa, amma mene ne wannan a tsakanina da kai? Ka binne mataccenka.”
My lord, hear me, —Land worth four hundred shekels of silver—betwixt me and thee, what is that? And thy dead., bury thou.
16 Ibrahim ya yarda da sharuɗan Efron, sai ya auna masa farashin da ya faɗa a kunnuwan Hittiyawa, shekel ɗari huɗu na azurfa, bisa ga ma’aunin da’yan kasuwa suke amfani da shi a lokacin.
And Abraham hearkened unto Ephron, and Abraham weighed out to Ephron the silver of which he had spoken in the ears of the sons of Heth, —four hundred shekels of silver, current with the merchant,
17 Ta haka filin Efron a Makfela kusa da Mamre, wato, filin da kogon a cikinsa, da kuma dukan itatuwan da suke cikin iyakoki filin, aka
So was confirmed the field of Ephron, which is in Machpelah, which is before Mamre, —the field and the cave which is therein, and all the timber which was in the field, which was in all the boundary thereof round about,
18 ba wa Ibrahim a matsayin mallakarsa a gaban dukan Hittiyawa waɗanda suka zo ƙofar birnin.
to Abraham as a purchase in the eyes of the sons of Heth, —with all who were entering the gate of his city.
19 Bayan wannan Ibrahim ya binne matarsa Saratu a kogon a filin Makfela kusa da Mamre (wanda yake a Hebron) a ƙasar Kan’ana.
And after this, did Abraham bury Sarah his wife, within the cave of the field of Machpelah, over against Mamre, the same, is Hebron, —in the land of Canaan.
20 Da filin da kuma kogon da yake cikinsa, Hittiyawa suka tabbatar wa Ibrahim a matsayin makabarta.
So was confirmed the field with the cave which was therein to Abraham, for a possession of a buryingplace, —from the sons of Heth.

< Farawa 23 >