< Farawa 23 >
1 Saratu ta yi shekara ɗari da ashirin da bakwai a duniya.
When Sarah was an hundreth twentie and seuen yeere olde (so long liued she).
2 Ta rasu a Kiriyat Arba (wato, Hebron) a ƙasar Kan’ana, Ibrahim kuwa ya tafi ya yi makokin Saratu, yana kuka saboda ita.
Then Sarah dyed in Kiriath-arba: the same is Hebron in the land of Canaan. and Abraham came to mourne for Sarah and to weepe for her.
3 Sai Ibrahim ya tashi daga gefen matarsa da ta mutu, ya yi magana da Hittiyawa. Ya ce,
Then Abraham rose vp from the sight of his corps, and talked with the Hittites, saying,
4 “Ni baƙo ne, kuma baƙo a cikinku. Ku sayar mini da wani wuri yă zama wurin binnewa a nan, domin in binne mataccena.”
I am a stranger, and a forreiner among you, giue me a possession of buriall with you, that I may burie my dead out of my sight.
5 Hittiyawa suka ce wa Ibrahim,
Then the Hittites answered Abraham, saying vnto him,
6 “Ranka yă daɗe, ka saurare mu. Kai babban yerima ne a cikinmu. Ka binne mataccenka a kabari mafi kyau na kaburburanmu. Babu waninmu da zai hana ka kabarinsa don binne mataccenka.”
Heare vs, my lorde: thou art a prince of God among vs: in the chiefest of our sepulchres bury thy dead: none of vs shall forbid thee his sepulchre, but thou mayest bury thy dead therein.
7 Sai Ibrahim ya tashi ya rusuna a gaban mutanen ƙasar, wato, Hittiyawan.
Then Abraham stoode vp, and bowed him selfe before the people of the land of the Hittites.
8 Ya ce musu, “In kuna so in binne mataccena, sai ku ji ni, ku roƙi Efron ɗan Zohar a madadina
And he communed with them, saying, If it be your minde, that I shall bury my dead out of my sight, heare me, and intreate for me to Ephron the sonne of Zohar,
9 domin yă sayar mini da kogon Makfela, wanda yake nasa, wannan da yake a ƙarshen filinsa. Ku ce masa yă sayar mini a cikakken farashi, yă zama mallakata domin makabarta tsakaninku.”
That he would giue me ye caue of Machpelah, which he hath in the ende of his field: that he would giue it me for as much money as it is worth, for a possession to bury in among you.
10 Efron mutumin Hitti yana zaune a cikin mutanensa, sai ya amsa wa Ibrahim a kunnuwan dukan Hittiyawa waɗanda suka zo ƙofar birni.
(For Ephron dwelt among the Hittites) Then Ephron the Hittite answered Abraham in the audience of all the Hittites that went in at the gates of his citie, saying,
11 Ya ce, “A’a, ranka yă daɗe, ka ji ni, na ba ka filin, na kuma ba ka kogon da yake cikinsa. Na ba ka shi a gaban mutanena. Ka binne mataccenka.”
No, my Lord, heare me: the fielde giue I thee, and the caue, that therein is, I giue it thee: euen in the presence of the sonnes of my people giue I it thee, to bury thy dead.
12 Ibrahim ya sāke rusuna a gaban mutanen ƙasar
Then Abraham bowed himselfe before the people of the land,
13 ya ce wa Efron a kunnuwansu, “Ka ji, in ka yarda. Zan biya farashin filin. Ka karɓa daga gare ni don in iya binne mataccena a can.”
And spake vnto Ephron in the audience of the people of the countrey, saying, Seeing thou wilt giue it, I pray thee, heare me, I will giue the price of the fielde: receiue it of me, and I will bury my dead there.
14 Efron ya ce wa Ibrahim,
Ephron then answered Abraham, saying vnto him,
15 “Ka saurare ni, ranka yă daɗe; darajan filin ya kai shekel ɗari huɗu na azurfa, amma mene ne wannan a tsakanina da kai? Ka binne mataccenka.”
My lord, hearken vnto me: ye land is worth foure hundreth shekels of siluer: what is that betweene me and thee? bury therefore thy dead.
16 Ibrahim ya yarda da sharuɗan Efron, sai ya auna masa farashin da ya faɗa a kunnuwan Hittiyawa, shekel ɗari huɗu na azurfa, bisa ga ma’aunin da’yan kasuwa suke amfani da shi a lokacin.
So Abraham hearkened vnto Ephron, and Abraham weyed to Ephron the siluer, which he had named, in the audience of the Hittites, euen foure hundreth siluer shekels of currant money among marchants.
17 Ta haka filin Efron a Makfela kusa da Mamre, wato, filin da kogon a cikinsa, da kuma dukan itatuwan da suke cikin iyakoki filin, aka
So the fielde of Ephron which was in Machpelah, and ouer against Mamre, euen the field and the caue that was therein, and all the trees that were in the fielde, which were in all the borders round about, was made sure
18 ba wa Ibrahim a matsayin mallakarsa a gaban dukan Hittiyawa waɗanda suka zo ƙofar birnin.
Vnto Abraham for a possession, in ye sight of the Hittites, euen of all that went in at the gates of his citie.
19 Bayan wannan Ibrahim ya binne matarsa Saratu a kogon a filin Makfela kusa da Mamre (wanda yake a Hebron) a ƙasar Kan’ana.
And after this, Abraham buried Sarah his wife in the caue of the fielde of Machpelah ouer against Mamre: the same is Hebron in the land of Canaan.
20 Da filin da kuma kogon da yake cikinsa, Hittiyawa suka tabbatar wa Ibrahim a matsayin makabarta.
Thus the fielde and the caue, that is therein, was made sure vnto Abraham for a possession of buriall by the Hittites.