< Farawa 23 >

1 Saratu ta yi shekara ɗari da ashirin da bakwai a duniya.
Sarah lived to be 127,
2 Ta rasu a Kiriyat Arba (wato, Hebron) a ƙasar Kan’ana, Ibrahim kuwa ya tafi ya yi makokin Saratu, yana kuka saboda ita.
and then she died at Kiriath-arba (or Hebron) in the land of Canaan. Abraham went in to mourn her death and to weep over her.
3 Sai Ibrahim ya tashi daga gefen matarsa da ta mutu, ya yi magana da Hittiyawa. Ya ce,
Then Abraham got up from beside his wife's body and went to talk with the leaders of the Hittites.
4 “Ni baƙo ne, kuma baƙo a cikinku. Ku sayar mini da wani wuri yă zama wurin binnewa a nan, domin in binne mataccena.”
“I am a foreigner, a stranger living among you,” he said. “Please let me buy a burial site so I can bury my dead wife.”
5 Hittiyawa suka ce wa Ibrahim,
The Hittites answered Abraham, telling him,
6 “Ranka yă daɗe, ka saurare mu. Kai babban yerima ne a cikinmu. Ka binne mataccenka a kabari mafi kyau na kaburburanmu. Babu waninmu da zai hana ka kabarinsa don binne mataccenka.”
“Listen, my lord, you are a highly-respected prince among us. Choose the very best of our burial sites to bury your dead. None of us will say no to you.”
7 Sai Ibrahim ya tashi ya rusuna a gaban mutanen ƙasar, wato, Hittiyawan.
Abraham got up and bowed low before the Hittites, the local people,
8 Ya ce musu, “In kuna so in binne mataccena, sai ku ji ni, ku roƙi Efron ɗan Zohar a madadina
and said to them, “If you agree to help me bury my dead, listen to my proposal. Could you please ask Ephron, son of Zohar,
9 domin yă sayar mini da kogon Makfela, wanda yake nasa, wannan da yake a ƙarshen filinsa. Ku ce masa yă sayar mini a cikakken farashi, yă zama mallakata domin makabarta tsakaninku.”
to sell me the cave of Machpelah that belongs to him, down at the end of his field. I'm willing to pay him the full price here in your presence so I can have my own burial site.”
10 Efron mutumin Hitti yana zaune a cikin mutanensa, sai ya amsa wa Ibrahim a kunnuwan dukan Hittiyawa waɗanda suka zo ƙofar birni.
Ephron the Hittite was sitting there among his people. He replied to Abraham in the presence of the Hittites who were there at the town gate.
11 Ya ce, “A’a, ranka yă daɗe, ka ji ni, na ba ka filin, na kuma ba ka kogon da yake cikinsa. Na ba ka shi a gaban mutanena. Ka binne mataccenka.”
“No, my lord,” he said. “Please listen to me. I give you the field and the cave that is there. I give it to you and my people are my witnesses. Please go and bury your dead.”
12 Ibrahim ya sāke rusuna a gaban mutanen ƙasar
Abraham bowed low before the local people,
13 ya ce wa Efron a kunnuwansu, “Ka ji, in ka yarda. Zan biya farashin filin. Ka karɓa daga gare ni don in iya binne mataccena a can.”
and said to Ephron so everyone could hear, “Please listen to me. I will pay the price for the field. Take the money and let me go and bury my dead there.”
14 Efron ya ce wa Ibrahim,
Ephron replied to Abraham, telling him,
15 “Ka saurare ni, ranka yă daɗe; darajan filin ya kai shekel ɗari huɗu na azurfa, amma mene ne wannan a tsakanina da kai? Ka binne mataccenka.”
“My lord, please listen to me. The land is worth four hundred pieces of silver. But what's that between us? Go and bury your dead.”
16 Ibrahim ya yarda da sharuɗan Efron, sai ya auna masa farashin da ya faɗa a kunnuwan Hittiyawa, shekel ɗari huɗu na azurfa, bisa ga ma’aunin da’yan kasuwa suke amfani da shi a lokacin.
Abraham accepted Ephron's offer. Abraham weighed out and gave to Ephron the four hundred pieces of silver he'd mentioned, using the standard weights used by merchants, and with the Hittites acting as witnesses.
17 Ta haka filin Efron a Makfela kusa da Mamre, wato, filin da kogon a cikinsa, da kuma dukan itatuwan da suke cikin iyakoki filin, aka
So the property was legally transferred. It comprised Ephron's field in Machpelah near Mamre, both the field and the cave there, as well as all the trees in the field, and all the area up to the existing boundaries.
18 ba wa Ibrahim a matsayin mallakarsa a gaban dukan Hittiyawa waɗanda suka zo ƙofar birnin.
This all became Abraham's property, and the transaction was witnessed by the Hittites who were there at the town gate.
19 Bayan wannan Ibrahim ya binne matarsa Saratu a kogon a filin Makfela kusa da Mamre (wanda yake a Hebron) a ƙasar Kan’ana.
Then Abraham went and buried Sarah his wife in the cave in the field at Machpelah near Mamre (or Hebron) in the land of Canaan.
20 Da filin da kuma kogon da yake cikinsa, Hittiyawa suka tabbatar wa Ibrahim a matsayin makabarta.
Ownership of the field and the cave there was transferred from the Hittites to Abraham to serve as his burial place.

< Farawa 23 >