< Farawa 23 >

1 Saratu ta yi shekara ɗari da ashirin da bakwai a duniya.
Sara levede 127 År, så mange var Saras Leveår.
2 Ta rasu a Kiriyat Arba (wato, Hebron) a ƙasar Kan’ana, Ibrahim kuwa ya tafi ya yi makokin Saratu, yana kuka saboda ita.
Sara døde i Kirjat Arba, det er Hebron, i Kana'ans Land. Så gik Abraham hen og holdt Klage over Sara og begræd hende.
3 Sai Ibrahim ya tashi daga gefen matarsa da ta mutu, ya yi magana da Hittiyawa. Ya ce,
Og da han havde rejst sig fra sin døde, talte han således til Hetiterne:
4 “Ni baƙo ne, kuma baƙo a cikinku. Ku sayar mini da wani wuri yă zama wurin binnewa a nan, domin in binne mataccena.”
"Jeg er Gæst og fremmed hos eder; men giv mig et Gravsted hos eder, så jeg kan jorde min døde og bringe hende bort fra mit Ansigt!"
5 Hittiyawa suka ce wa Ibrahim,
Da svarede Hetiterne Abraham:
6 “Ranka yă daɗe, ka saurare mu. Kai babban yerima ne a cikinmu. Ka binne mataccenka a kabari mafi kyau na kaburburanmu. Babu waninmu da zai hana ka kabarinsa don binne mataccenka.”
"Hør os, Herre! En Guds Fyrste er du jo iblandt os; jord du din døde i en af vore bedste Grave! Ikke en af os vil nægte dig sin Grav og hindre dig i at jorde din døde."
7 Sai Ibrahim ya tashi ya rusuna a gaban mutanen ƙasar, wato, Hittiyawan.
Men Abraham stod op og bøjede sig for Hetiterne, Folkene der på Stedet,
8 Ya ce musu, “In kuna so in binne mataccena, sai ku ji ni, ku roƙi Efron ɗan Zohar a madadina
og sagde til dem: "Hvis I samtykker i, at jeg jorder min døde og bringer hende bort fra mit Ansigt, så føj mig i at lægge et godt Ord ind for mig hos Efron, Zohars Søn,
9 domin yă sayar mini da kogon Makfela, wanda yake nasa, wannan da yake a ƙarshen filinsa. Ku ce masa yă sayar mini a cikakken farashi, yă zama mallakata domin makabarta tsakaninku.”
så han giver mig sin Klippehule i Makpela ved Udkanten af sin Mark; for fuld Betaling skal han i eders Nærværelse give mig den til Gravsted!"
10 Efron mutumin Hitti yana zaune a cikin mutanensa, sai ya amsa wa Ibrahim a kunnuwan dukan Hittiyawa waɗanda suka zo ƙofar birni.
Men Efron sad blandt Hetiterne; og Hetiten Efron svarede Abraham i Hetiternes Påhør, så mange som gik ind gennem hans Bys Port:
11 Ya ce, “A’a, ranka yă daɗe, ka ji ni, na ba ka filin, na kuma ba ka kogon da yake cikinsa. Na ba ka shi a gaban mutanena. Ka binne mataccenka.”
"Gid min Herre vilde høre mig! Marken giver jeg dig, og Hulen derpå giver jeg dig; i mit Folks Nærværelse giver jeg dig den; jord du kun din døde!"
12 Ibrahim ya sāke rusuna a gaban mutanen ƙasar
Da bøjede Abraham sig for Folkene der på Stedet
13 ya ce wa Efron a kunnuwansu, “Ka ji, in ka yarda. Zan biya farashin filin. Ka karɓa daga gare ni don in iya binne mataccena a can.”
og sagde til Efron i deres Påhør: "Om du blot - gid du dog vilde høre mig! Jeg giver dig, hvad Marken er værd; modtag det dog af mig, så jeg kan jorde min døde der."
14 Efron ya ce wa Ibrahim,
Da sagde Efron til Abraham:
15 “Ka saurare ni, ranka yă daɗe; darajan filin ya kai shekel ɗari huɗu na azurfa, amma mene ne wannan a tsakanina da kai? Ka binne mataccenka.”
"Gid min Herre vilde høre mig! Et Stykke Land til 400 Sekel Sølv, hvad har det at sige mellem mig og dig? Jord du kun din døde!"
16 Ibrahim ya yarda da sharuɗan Efron, sai ya auna masa farashin da ya faɗa a kunnuwan Hittiyawa, shekel ɗari huɗu na azurfa, bisa ga ma’aunin da’yan kasuwa suke amfani da shi a lokacin.
Og Abraham forstod Efron og tilvejede ham den Sum, han havde nævnet i Hetiternes Påhør, 400 Sekel Sølv i gangbar Mønt.
17 Ta haka filin Efron a Makfela kusa da Mamre, wato, filin da kogon a cikinsa, da kuma dukan itatuwan da suke cikin iyakoki filin, aka
Således gik Efrons Mark i Makpela over for Mamre i hele sin Udstrækning tillige med Klippehulen og alle Træerne på Marken
18 ba wa Ibrahim a matsayin mallakarsa a gaban dukan Hittiyawa waɗanda suka zo ƙofar birnin.
over i Abrahams Eje i Hetiternes Næværelse, så mange som gik ind gennem hans Bys Port.
19 Bayan wannan Ibrahim ya binne matarsa Saratu a kogon a filin Makfela kusa da Mamre (wanda yake a Hebron) a ƙasar Kan’ana.
Derefter jordede Abraham sin Hustru Sara i Klippehulen på Makpelas Mark over for Mamre, det er Hebron, i Kana'ans Land.
20 Da filin da kuma kogon da yake cikinsa, Hittiyawa suka tabbatar wa Ibrahim a matsayin makabarta.
Og Marken med Klippehulen derpå gik fra Hetiterne over til Abraham som Gravsted.

< Farawa 23 >