< Farawa 23 >

1 Saratu ta yi shekara ɗari da ashirin da bakwai a duniya.
Duljina Sarina života bila je stotinu dvadeset i sedam godina.
2 Ta rasu a Kiriyat Arba (wato, Hebron) a ƙasar Kan’ana, Ibrahim kuwa ya tafi ya yi makokin Saratu, yana kuka saboda ita.
Sara umrije u Kirjat Arbi, to jest u Hebronu, u zemlji kanaanskoj; i Abraham uđe u žalost za Sarom i naricaše za njom.
3 Sai Ibrahim ya tashi daga gefen matarsa da ta mutu, ya yi magana da Hittiyawa. Ya ce,
Potom se Abraham digne ispred svoje pokojnice te prozbori sinovima Hetovim:
4 “Ni baƙo ne, kuma baƙo a cikinku. Ku sayar mini da wani wuri yă zama wurin binnewa a nan, domin in binne mataccena.”
“Premda sam ja među vama doseljeni stranac, prodajte mi zemljište za grob među vama, tako da mogu iznijeti svoju pokojnicu i sahraniti je.”
5 Hittiyawa suka ce wa Ibrahim,
A sinovi Hetovi odgovore Abrahamu:
6 “Ranka yă daɗe, ka saurare mu. Kai babban yerima ne a cikinmu. Ka binne mataccenka a kabari mafi kyau na kaburburanmu. Babu waninmu da zai hana ka kabarinsa don binne mataccenka.”
“Gospodine, saslušaj nas! Ti si izabranik Božji u našoj sredini. Pokopaj svoju pokojnicu u našem najbiranijem grobu. Nitko ti od nas neće odbiti svoga groba da mogneš sahraniti svoju pokojnicu.”
7 Sai Ibrahim ya tashi ya rusuna a gaban mutanen ƙasar, wato, Hittiyawan.
Nato se Abraham diže pa se mještanima, sinovima Hetovim, duboko pokloni
8 Ya ce musu, “In kuna so in binne mataccena, sai ku ji ni, ku roƙi Efron ɗan Zohar a madadina
te im reče: “Ako se slažete da svoju pokojnicu uklonim i sahranim, čujte me: zauzmite se za me kod Efrona, sina Soharova,
9 domin yă sayar mini da kogon Makfela, wanda yake nasa, wannan da yake a ƙarshen filinsa. Ku ce masa yă sayar mini a cikakken farashi, yă zama mallakata domin makabarta tsakaninku.”
da mi proda spilju Makpelu što njemu pripada a nalazi se na kraju njegova posjeda; neka mi je za punu cijenu, u vašoj nazočnosti, proda u vlasništvo za sahranjivanje.”
10 Efron mutumin Hitti yana zaune a cikin mutanensa, sai ya amsa wa Ibrahim a kunnuwan dukan Hittiyawa waɗanda suka zo ƙofar birni.
A Efron je sjedio sa sinovima Hetovim. Potom Efron, Hetit, odgovori Abrahamu da ga čuju sinovi Hetovi svojim ušima - svi koji su sjedili u vijeću onoga grada:
11 Ya ce, “A’a, ranka yă daɗe, ka ji ni, na ba ka filin, na kuma ba ka kogon da yake cikinsa. Na ba ka shi a gaban mutanena. Ka binne mataccenka.”
“Ne, moj gospodine! Saslušaj mene! Ja tebi dajem poljanu i spilju što je na njoj; darujem ti to pred sinovima svoga naroda. Sahrani svoju pokojnicu.”
12 Ibrahim ya sāke rusuna a gaban mutanen ƙasar
Abraham se duboko nakloni mještanima,
13 ya ce wa Efron a kunnuwansu, “Ka ji, in ka yarda. Zan biya farashin filin. Ka karɓa daga gare ni don in iya binne mataccena a can.”
a onda progovori Efronu da mještani čuju na svoje uši: “Ded me samo poslušaj! Dajem ti cijenu za poljanu; primi je od mene da ondje mogu sahraniti svoju pokojnicu!”
14 Efron ya ce wa Ibrahim,
Efron odgovori Abrahamu:
15 “Ka saurare ni, ranka yă daɗe; darajan filin ya kai shekel ɗari huɗu na azurfa, amma mene ne wannan a tsakanina da kai? Ka binne mataccenka.”
“Čuj me, moj gospodine: zemljište u vrijednosti od četiri stotine srebrnika, što je to tebi i meni! Sahrani, dakle, svoju pokojnicu!”
16 Ibrahim ya yarda da sharuɗan Efron, sai ya auna masa farashin da ya faɗa a kunnuwan Hittiyawa, shekel ɗari huɗu na azurfa, bisa ga ma’aunin da’yan kasuwa suke amfani da shi a lokacin.
Abraham se složi s Efronom; isplati Abraham Efronu novac što ga je spomenuo tako da su na svoje uši čuli sinovi Hetovi - četiri stotine srebrnika trgovačke mjere.
17 Ta haka filin Efron a Makfela kusa da Mamre, wato, filin da kogon a cikinsa, da kuma dukan itatuwan da suke cikin iyakoki filin, aka
I tako Efronova poljana u Makpeli nasuprot Mamri - poljana, spilja i sva stabla što su bila na poljani -
18 ba wa Ibrahim a matsayin mallakarsa a gaban dukan Hittiyawa waɗanda suka zo ƙofar birnin.
prijeđe u vlasništvo Abrahamovo u nazočnosti sinova Hetovih, sviju koji su sjedili u vijeću svoga grada.
19 Bayan wannan Ibrahim ya binne matarsa Saratu a kogon a filin Makfela kusa da Mamre (wanda yake a Hebron) a ƙasar Kan’ana.
A onda Abraham sahrani svoju ženu Saru u spilji na poljani Makpeli nasuprot Mamri - danas Hebronu - u zemlji kanaanskoj.
20 Da filin da kuma kogon da yake cikinsa, Hittiyawa suka tabbatar wa Ibrahim a matsayin makabarta.
Tako je poljana i spilja na njoj prešla od sinova Hetovih u vlasništvo Abrahamovo za sahranjivanje.

< Farawa 23 >