< Farawa 23 >

1 Saratu ta yi shekara ɗari da ashirin da bakwai a duniya.
Sela da ode 127 esalu.
2 Ta rasu a Kiriyat Arba (wato, Hebron) a ƙasar Kan’ana, Ibrahim kuwa ya tafi ya yi makokin Saratu, yana kuka saboda ita.
Amalalu, e da Hibalone moilai bai bagade, Ga: ina: ne soge ganodini, amoga bogoi. A: ibalaha: me da amoga ea udama asigiba: le, dimusa: asi.
3 Sai Ibrahim ya tashi daga gefen matarsa da ta mutu, ya yi magana da Hittiyawa. Ya ce,
Amalalu, A:ibalaha: me da ea uda bogoi da: i hodo amoga ouesalu, wa: legadole Hidaide dunuma asili, amane sia: i,
4 “Ni baƙo ne, kuma baƙo a cikinku. Ku sayar mini da wani wuri yă zama wurin binnewa a nan, domin in binne mataccena.”
“Na da dilia fi amo ganodini ga fi dunu esala. Na uda bogoi uli dogoma: ne, soge fonobahadi nama bidi lama.”
5 Hittiyawa suka ce wa Ibrahim,
Hidaide dunu da A: ibalaha: mema bu adole i,
6 “Ranka yă daɗe, ka saurare mu. Kai babban yerima ne a cikinmu. Ka binne mataccenka a kabari mafi kyau na kaburburanmu. Babu waninmu da zai hana ka kabarinsa don binne mataccenka.”
“Ada! Ninia sia: nabima! Di da ninima gasa bagade ouligisu dunu agoane. Ninia bogoi uli dogoi sogebiga, uli dogoi noga: idafa lama. Ninia huluane da baligili noga: idafa uli dogoi dima imunu hame higamu.”
7 Sai Ibrahim ya tashi ya rusuna a gaban mutanen ƙasar, wato, Hittiyawan.
Amalalu, A:ibalaha: me da wa: legadole, amo soge esalebe dunu amo Hidaide, ilima begudui.
8 Ya ce musu, “In kuna so in binne mataccena, sai ku ji ni, ku roƙi Efron ɗan Zohar a madadina
E da ilima amane sia: i, “Dilia da na bogoi uli dogomusa: hahawane ba: i galea, defea, dilia Ifalone (Souha ea mano) amoma na fidima: ne adole ba: ma.
9 domin yă sayar mini da kogon Makfela, wanda yake nasa, wannan da yake a ƙarshen filinsa. Ku ce masa yă sayar mini a cikakken farashi, yă zama mallakata domin makabarta tsakaninku.”
Ea soge la: idi ganodini da Ma: gafila gele gelabo. Amo e da gaguiba: le, e da amo ea muni defei na da dilia fi amo ganodini na bogoi uli dogomusa: bidi lama: ne, dilia ema adole ba: ma.”
10 Efron mutumin Hitti yana zaune a cikin mutanensa, sai ya amsa wa Ibrahim a kunnuwan dukan Hittiyawa waɗanda suka zo ƙofar birni.
Ifalone e da amo Hidaide fi dunu ea fi ganodini esalebe ba: i. Ilia huluane da moilai logo holeiga gilisi. E da Hidaide dunu huluane nabima: ne, A:ibalaha: mema amane adole i,
11 Ya ce, “A’a, ranka yă daɗe, ka ji ni, na ba ka filin, na kuma ba ka kogon da yake cikinsa. Na ba ka shi a gaban mutanena. Ka binne mataccenka.”
“Hame mabu ada! Na sia: nabima! Amo soge amola gele gelabo amo ganodini diala, na da udigili dima imunu. Na dunu huluane ba: ma: ne, na da dima iaha. Dia bogoi amoga uli dogoma!”
12 Ibrahim ya sāke rusuna a gaban mutanen ƙasar
A: ibalaha: me da amo soge fi dunu ilima bu begudui,
13 ya ce wa Efron a kunnuwansu, “Ka ji, in ka yarda. Zan biya farashin filin. Ka karɓa daga gare ni don in iya binne mataccena a can.”
Ilia huluane nabima: ne, e da Ifalonema amane sia: i, “Na da dilima na sia: nabima: ne edegesa. Na da amo soge huluane ea ilegei amo defele bidi lamu. Amo muni lama. Na da na bogoi amoga uli dogomu galebe.”
14 Efron ya ce wa Ibrahim,
Ifalone da A: ibalaha: mema bu adole i,
15 “Ka saurare ni, ranka yă daɗe; darajan filin ya kai shekel ɗari huɗu na azurfa, amma mene ne wannan a tsakanina da kai? Ka binne mataccenka.”
“Ada! Nabima! Amo soge bidi lamu defei da silifa fage 400 fawane. Amo muni da anima hamedei liligi. Dia bogoi uli dogoma!”
16 Ibrahim ya yarda da sharuɗan Efron, sai ya auna masa farashin da ya faɗa a kunnuwan Hittiyawa, shekel ɗari huɗu na azurfa, bisa ga ma’aunin da’yan kasuwa suke amfani da shi a lokacin.
A: ibalaha: me da Ifalone ea sia: i hahawane ba: i. E da Hidaide dunu huluane ba: ma: ne, muni ea sia: i defele Ifalonema i. Defei da silifa fage 400 amo ea dioi ilegei defele da bidiga lasu dunu ilia hou defele i.
17 Ta haka filin Efron a Makfela kusa da Mamre, wato, filin da kogon a cikinsa, da kuma dukan itatuwan da suke cikin iyakoki filin, aka
Amaiba: le, Ifalone ea sogebi amo da Ma: gafila soge ganodini Ma: melei soge gadenene, - sogebi, gele gelabo amo ganodini dialu amola ifa huluane amo sogebi ganodini, huluane A: ibalaha: me da lai dagoi.
18 ba wa Ibrahim a matsayin mallakarsa a gaban dukan Hittiyawa waɗanda suka zo ƙofar birnin.
Hidaide dunu huluane logo holeiga gilisi da amo hou ba: beba: le, amo soge da wali A: ibalaha: me ea soge ilegei.
19 Bayan wannan Ibrahim ya binne matarsa Saratu a kogon a filin Makfela kusa da Mamre (wanda yake a Hebron) a ƙasar Kan’ana.
Amalalu, A:ibalaha: me da ea uda Sela amo gele gelabo Ma: gafila sogebi ganodini (Ga: ina: ne soge ganodini) uli dogone sali.
20 Da filin da kuma kogon da yake cikinsa, Hittiyawa suka tabbatar wa Ibrahim a matsayin makabarta.
Amola Ma: gafila sogebi amola gele gelabo amo ganodini gala musa: da Hidaide dunu da gagui, amo A: ibalaha: me ea fi bogoi uli dogomusa: bidi lai dagoi.

< Farawa 23 >