< Farawa 22 >

1 Bayan abubuwan nan suka faru, sai Allah ya gwada Ibrahim. Ya ce masa, “Ibrahim!” Ibrahim ya amsa ya ce, “Ga ni.”
Después de estas cosas, Dios puso a prueba a Abraham, y le dijo: ¡Abraham! y él dijo: Heme aquí.
2 Sai Allah ya ce, “Ka ɗauki ɗanka, makaɗaicin ɗanka Ishaku, wanda kake ƙauna, ka tafi yankin Moriya, ka miƙa shi hadaya ta ƙonawa a can a kan ɗaya daga cikin duwatsun da zan nuna maka.”
Y él le dijo: Toma a tu hijo, tu único y amado hijo Isaac, y ve a la tierra de Moriah, y ofrécelo como holocausto en uno de los montes, del cual yo te daré conocimiento.
3 Kashegari da sassafe, Ibrahim ya tashi ya ɗaura wa jakinsa sirdi. Ya ɗauki bayinsa biyu, da ɗansa Ishaku. Bayan ya faskare isashen itace saboda hadaya ta ƙonawa sai ya kama hanya zuwa wurin da Allah ya faɗa masa.
Y Abraham se levantó temprano en la mañana, y preparó su asno, y tomó consigo dos de sus jóvenes e Isaac, su hijo, y después de que se había cortado el leño para la ofrenda quemada, se fue en su camino al lugar del cual Dios le había dado la palabra.
4 A rana ta uku Ibrahim ya ɗaga ido sai ya ga wurin daga nesa.
Y al tercer día, Abraham, alzando sus ojos, vio el lugar de lejos.
5 Ibrahim ya ce wa bayinsa, “Ku tsaya a nan da jakin, ni da yaron kuwa mu haura can. Za mu yi sujada sa’an nan mu komo wurinku.”
Entonces dijo a sus jóvenes: Quédate aquí con el asno; y yo y el niño continuaremos y rendiremos culto y regresaremos a ti.
6 Ibrahim ya ɗauki itace saboda hadaya ta ƙonawa ya ɗora wa ɗansa Ishaku, shi kuwa ya riƙe wuƙa da wutar. Yayinda su biyun suke tafiya,
Y Abraham puso la leña para la ofrenda quemada en la espalda de su hijo, y él mismo tomó el fuego y él cuchillo en su mano, y los dos siguieron juntos.
7 sai Ishaku ya yi tambaya, ya ce wa mahaifinsa Ibrahim, “Baba?” Ibrahim ya ce masa, “Na’am ɗana!” Ishaku ya ce, “Ga dai wuta, ga kuma itace, amma ina ɗan ragon hadaya ta ƙonawa?”
Entonces Isaac dijo a Abraham: Mi padre; y él dijo: Heme aquí, mi hijo. Y él dijo: Aquí tenemos leña y fuego, pero ¿dónde está el cordero para la ofrenda quemada?
8 Ibrahim ya amsa ya ce, “Ɗana, Allah kansa zai tanada ɗan ragon hadayar ƙonawa.” Sai su biyu suka ci gaba da tafiya.
Y Abraham dijo: Dios mismo dará el cordero para el holocausto; y así continuaron juntos.
9 Sa’ad da suka isa wurin da Allah ya faɗa masa, sai Ibrahim ya gina bagade a can, ya kuma shisshirya itacen a kai. Ya ɗaura ɗansa Ishaku, ya kwantar da shi a kan itacen, a bisa bagaden.
Y vinieron al lugar del cual Dios le había dado conocimiento; y allí hizo Abraham el altar, y puso la leña en su lugar, y cerrando las ataduras alrededor de su hijo Isaac, lo puso sobre la leña sobre el altar.
10 Sa’an nan Ibrahim ya miƙa hannunsa ya ɗauki wuƙar don yă yanka ɗansa.
Y extendiendo su mano, Abraham tomó el cuchillo para matar a su hijo.
11 Amma mala’ikan Ubangiji ya kira shi daga sama ya ce, “Ibrahim, Ibrahim!” Sai Ibrahim ya amsa ya ce, “Ga ni.”
Pero la voz del ángel del Señor vino del cielo, diciendo: Abraham, Abraham, y él dijo: Heme aquí.
12 Mala’ikan ya ce, “Kada ka yi wa yaron nan rauni. Kada kuma ka ji masa ciwo. Yanzu na san cewa kana tsoron Allah, gama ba ka hana ni ɗanka, makaɗaicin ɗanka ba.”
Y él dijo: No se extienda tu mano contra el niño para hacerle nada; por ahora estoy seguro de que el temor de Dios está en tu corazón, porque no has retenido a tu hijo, tu único hijo, de mí.
13 Ibrahim ya ɗaga ido, ya duba, sai ya ga rago da ƙahoninsa a kafe a wani ɗan kurmi. Sai Ibrahim ya tafi ya kamo ragon ya miƙa shi hadaya ta ƙonawa a maimakon ɗansa.
Y alzando sus ojos, Abraham vio una oveja fijada por los cuernos en la maleza: y Abraham tomó las ovejas e hizo una ofrenda quemada en lugar de su hijo.
14 Ibrahim kuwa ya ba wa wurin suna, Ubangiji Zai Tanada. Gama kamar yadda ake ce har yă zuwa yau, “A bisan dutsen Ubangiji, za a tanada.”
Y dio Abraham aquel lugar el nombre del Señor proveerá, y dijo: Como se dice hasta hoy, en el monte del Señor se proveerá.
15 Mala’ikan Ubangiji ya kira Ibrahim daga sama sau na biyu
Y la voz del ángel del Señor vino a Abraham una segunda vez desde el cielo,
16 ya ce, “Na rantse da kaina, in ji Ubangiji, domin ka yi wannan, ba ka kuwa hana ni ɗanka, makaɗaicin ɗanka ba,
Diciendo: He jurado por mi nombre, dice el Señor, porque has hecho esto y no has apartado de mí a tu único hijo amado,
17 tabbatacce zan albarkace ka, zan kuma sa zuriyarka su yi yawa kamar taurari a sararin sama, kamar kuma yashi a bakin teku. Zuriyarka za su mallaki biranen abokan gābansu,
que ciertamente te daré mi bendición, y tu simiente será aumentada como las estrellas del cielo y la arena a la orilla del mar; tu simiente tomará la tierra de los que están en contra de ellos;
18 ta wurin zuriyarka kuma dukan al’umman duniya za su sami albarka, domin ka yi mini biyayya.”
Y tu descendencia será bendición para todas las naciones de la tierra, porque has hecho lo que te ordené que hicieras.
19 Sa’an nan Ibrahim ya koma wurin bayinsa, suka kuma kama hanya tare zuwa Beyersheba. Ibrahim kuwa ya yi zamansa a Beyersheba.
Entonces Abraham regresó con sus jóvenes y se fueron juntos a Beerseba, el lugar donde Abraham vivía.
20 Bayan wani ɗan lokaci, sai aka faɗa wa Ibrahim cewa, “Ga shi, Milka ita ma ta haifa wa Nahor ɗan’uwanka,’ya’ya maza;
Después de estas cosas, Abraham tuvo noticias de que Milca, la esposa de su hermano Nacor, había dado a luz a niños;
21 ɗan fari shi ne Uz, ɗan’uwansa kuma Buz, Kemuwel (shi ne mahaifin Aram),
Uz el mayor, y Buz su hermano, y Kemuel, padre de Aram,
22 Kesed, Hazo, Fildash; Yidlaf, da kuma Betuwel.”
Y Quesed, Hazo, Pildas, Jidlaf, Betuel.
23 Betuwel ya haifi Rebeka. Milka ta haifa wa Nahor ɗan’uwan Ibrahim waɗannan’ya’ya maza takwas.
Betuel fue el padre de Rebeca; estos ocho fueron los hijos de Milca y Nacor, hermano de Abraham.
24 Ban da haka ma, ƙwarƙwararsa, mai suna Reyuma, ta haifa masa’ya’ya maza, Teba, Gaham, Tahash da kuma Ma’aka.
Y su concubina Reúma dio a luz a Teba, Gaham, Tahas y Maaca.

< Farawa 22 >