< Farawa 22 >

1 Bayan abubuwan nan suka faru, sai Allah ya gwada Ibrahim. Ya ce masa, “Ibrahim!” Ibrahim ya amsa ya ce, “Ga ni.”
Poslije toga šæaše Bog okušati Avrama, pa mu reèe: Avrame! A on odgovori: evo me.
2 Sai Allah ya ce, “Ka ɗauki ɗanka, makaɗaicin ɗanka Ishaku, wanda kake ƙauna, ka tafi yankin Moriya, ka miƙa shi hadaya ta ƙonawa a can a kan ɗaya daga cikin duwatsun da zan nuna maka.”
I reèe mu Bog: uzmi sada sina svojega, jedinca svojega miloga, Isaka, pa idi u zemlju Moriju, i spali ga na žrtvu tamo na brdu gdje æu ti kazati.
3 Kashegari da sassafe, Ibrahim ya tashi ya ɗaura wa jakinsa sirdi. Ya ɗauki bayinsa biyu, da ɗansa Ishaku. Bayan ya faskare isashen itace saboda hadaya ta ƙonawa sai ya kama hanya zuwa wurin da Allah ya faɗa masa.
I sjutradan rano ustavši Avram osamari magarca svojega, i uze sa sobom dva momka i Isaka sina svojega; i nacijepavši drva za žrtvu podiže se i poðe na mjesto koje mu kaza Bog.
4 A rana ta uku Ibrahim ya ɗaga ido sai ya ga wurin daga nesa.
Treæi dan podigavši oèi svoje Avram ugleda mjesto izdaleka.
5 Ibrahim ya ce wa bayinsa, “Ku tsaya a nan da jakin, ni da yaron kuwa mu haura can. Za mu yi sujada sa’an nan mu komo wurinku.”
I reèe Avram momcima svojim: ostanite vi ovdje s magarcem, a ja i dijete idemo onamo, pa kad se pomolimo Bogu, vratiæemo se k vama.
6 Ibrahim ya ɗauki itace saboda hadaya ta ƙonawa ya ɗora wa ɗansa Ishaku, shi kuwa ya riƙe wuƙa da wutar. Yayinda su biyun suke tafiya,
I uzevši Avram drva za žrtvu naprti Isaku sinu svojemu, a sam uze u svoje ruke ognja i nož; pa otidoše obojica zajedno.
7 sai Ishaku ya yi tambaya, ya ce wa mahaifinsa Ibrahim, “Baba?” Ibrahim ya ce masa, “Na’am ɗana!” Ishaku ya ce, “Ga dai wuta, ga kuma itace, amma ina ɗan ragon hadaya ta ƙonawa?”
Tada reèe Isak Avramu ocu svojemu: oèe! A on reèe: što, sine! I reèe Isak: eto ognja i drva, a gdje je jagnje za žrtvu?
8 Ibrahim ya amsa ya ce, “Ɗana, Allah kansa zai tanada ɗan ragon hadayar ƙonawa.” Sai su biyu suka ci gaba da tafiya.
A Avram odgovori: Bog æe se, sinko, postarati za jagnje sebi na žrtvu. I iðahu obojica zajedno.
9 Sa’ad da suka isa wurin da Allah ya faɗa masa, sai Ibrahim ya gina bagade a can, ya kuma shisshirya itacen a kai. Ya ɗaura ɗansa Ishaku, ya kwantar da shi a kan itacen, a bisa bagaden.
A kad doðoše na mjesto koje mu Bog kaza, Avram naèini ondje žrtvenik, i metnu drva na nj, i svezavši Isaka sina svojega metnu ga na žrtvenik vrh drva;
10 Sa’an nan Ibrahim ya miƙa hannunsa ya ɗauki wuƙar don yă yanka ɗansa.
I izmahnu Avram rukom svojom i uze nož da zakolje sina svojega.
11 Amma mala’ikan Ubangiji ya kira shi daga sama ya ce, “Ibrahim, Ibrahim!” Sai Ibrahim ya amsa ya ce, “Ga ni.”
Ali anðeo Gospodnji viknu ga s neba, i reèe: Avrame! Avrame! A on reèe: evo me.
12 Mala’ikan ya ce, “Kada ka yi wa yaron nan rauni. Kada kuma ka ji masa ciwo. Yanzu na san cewa kana tsoron Allah, gama ba ka hana ni ɗanka, makaɗaicin ɗanka ba.”
A anðeo reèe: ne diži ruke svoje na dijete, i ne èini mu ništa; jer sada poznah da se bojiš Boga, kad nijesi požalio sina svojega, jedinca svojega, mene radi.
13 Ibrahim ya ɗaga ido, ya duba, sai ya ga rago da ƙahoninsa a kafe a wani ɗan kurmi. Sai Ibrahim ya tafi ya kamo ragon ya miƙa shi hadaya ta ƙonawa a maimakon ɗansa.
I Avram podigavši oèi svoje pogleda; i gle, ovan iza njega zapleo se u èesti rogovima; i otišavši Avram uze ovna i spali ga na žrtvu mjesto sina svojega.
14 Ibrahim kuwa ya ba wa wurin suna, Ubangiji Zai Tanada. Gama kamar yadda ake ce har yă zuwa yau, “A bisan dutsen Ubangiji, za a tanada.”
I nazva Avram ono mjesto: Gospod æe se postarati. Zato se i danas kaže: na brdu, gdje æe se Gospod postarati.
15 Mala’ikan Ubangiji ya kira Ibrahim daga sama sau na biyu
I anðeo Gospodnji opet viknu s neba Avrama.
16 ya ce, “Na rantse da kaina, in ji Ubangiji, domin ka yi wannan, ba ka kuwa hana ni ɗanka, makaɗaicin ɗanka ba,
I reèe: sobom se zakleh, veli Gospod: kad si tako uèinio, i nijesi požalio sina svojega, jedinca svojega,
17 tabbatacce zan albarkace ka, zan kuma sa zuriyarka su yi yawa kamar taurari a sararin sama, kamar kuma yashi a bakin teku. Zuriyarka za su mallaki biranen abokan gābansu,
Zaista æu te blagosloviti i sjeme tvoje veoma umnožiti, da ga bude kao zvijezda na nebu i kao pijeska na brijegu morskom; i naslijediæe sjeme tvoje vrata neprijatelja svojih.
18 ta wurin zuriyarka kuma dukan al’umman duniya za su sami albarka, domin ka yi mini biyayya.”
I blagosloviæe se u sjemenu tvojem svi narodi na zemlji, kad si poslušao glas moj.
19 Sa’an nan Ibrahim ya koma wurin bayinsa, suka kuma kama hanya tare zuwa Beyersheba. Ibrahim kuwa ya yi zamansa a Beyersheba.
Tada se Avram vrati k momcima svojim, te se digoše, i otidoše zajedno u Virsaveju, jer Avram življaše u Virsaveji.
20 Bayan wani ɗan lokaci, sai aka faɗa wa Ibrahim cewa, “Ga shi, Milka ita ma ta haifa wa Nahor ɗan’uwanka,’ya’ya maza;
Poslije toga javiše Avramu govoreæi: gle, i Melha rodi sinove bratu tvojemu Nahoru:
21 ɗan fari shi ne Uz, ɗan’uwansa kuma Buz, Kemuwel (shi ne mahaifin Aram),
Uza prvenca i Vuza brata mu, i Kamuila, oca Avramova,
22 Kesed, Hazo, Fildash; Yidlaf, da kuma Betuwel.”
I Hazada i Azava i Faldesa i Jeldafa i Vatuila.
23 Betuwel ya haifi Rebeka. Milka ta haifa wa Nahor ɗan’uwan Ibrahim waɗannan’ya’ya maza takwas.
A Vatuilo rodi Reveku. Osam ih rodi Melha Nahoru bratu Avramovu.
24 Ban da haka ma, ƙwarƙwararsa, mai suna Reyuma, ta haifa masa’ya’ya maza, Teba, Gaham, Tahash da kuma Ma’aka.
A inoèa njegova, po imenu Revma, rodi i ona Taveka i Gama i Tohosa i Moha.

< Farawa 22 >