< Farawa 22 >

1 Bayan abubuwan nan suka faru, sai Allah ya gwada Ibrahim. Ya ce masa, “Ibrahim!” Ibrahim ya amsa ya ce, “Ga ni.”
Depois destas coisas, Deus testou Abraão, e lhe disse: “Abraão!”. Ele disse: “Aqui estou eu”.
2 Sai Allah ya ce, “Ka ɗauki ɗanka, makaɗaicin ɗanka Ishaku, wanda kake ƙauna, ka tafi yankin Moriya, ka miƙa shi hadaya ta ƙonawa a can a kan ɗaya daga cikin duwatsun da zan nuna maka.”
Ele disse: “Agora pegue seu filho, seu único filho, Isaac, a quem você ama, e vá para a terra de Moriah”. Ofereça-o lá como holocausto em uma das montanhas de que lhe falarei”.
3 Kashegari da sassafe, Ibrahim ya tashi ya ɗaura wa jakinsa sirdi. Ya ɗauki bayinsa biyu, da ɗansa Ishaku. Bayan ya faskare isashen itace saboda hadaya ta ƙonawa sai ya kama hanya zuwa wurin da Allah ya faɗa masa.
Abraão levantou-se cedo pela manhã e selou seu burro; e levou consigo dois de seus jovens e Isaac seu filho. Ele dividiu a madeira para o holocausto, levantou-se e foi para o lugar de que Deus lhe dissera.
4 A rana ta uku Ibrahim ya ɗaga ido sai ya ga wurin daga nesa.
No terceiro dia, Abraão levantou os olhos e viu o lugar distante.
5 Ibrahim ya ce wa bayinsa, “Ku tsaya a nan da jakin, ni da yaron kuwa mu haura can. Za mu yi sujada sa’an nan mu komo wurinku.”
Abraão disse a seus jovens: “Fiquem aqui com o burro. O garoto e eu iremos até lá”. Vamos adorar, e voltaremos para você”.
6 Ibrahim ya ɗauki itace saboda hadaya ta ƙonawa ya ɗora wa ɗansa Ishaku, shi kuwa ya riƙe wuƙa da wutar. Yayinda su biyun suke tafiya,
Abraão pegou a madeira do holocausto e a colocou sobre Isaac, seu filho. Ele pegou na mão o fogo e a faca. Os dois foram juntos.
7 sai Ishaku ya yi tambaya, ya ce wa mahaifinsa Ibrahim, “Baba?” Ibrahim ya ce masa, “Na’am ɗana!” Ishaku ya ce, “Ga dai wuta, ga kuma itace, amma ina ɗan ragon hadaya ta ƙonawa?”
Isaac falou com Abraão, seu pai, e disse: “Meu pai...”. Ele disse: “Aqui estou eu, meu filho”. Ele disse: “Aqui está o fogo e a lenha, mas onde está o cordeiro para um holocausto”?
8 Ibrahim ya amsa ya ce, “Ɗana, Allah kansa zai tanada ɗan ragon hadayar ƙonawa.” Sai su biyu suka ci gaba da tafiya.
Abraão disse: “Deus proverá a si mesmo o cordeiro para um holocausto, meu filho”. Então, ambos foram juntos.
9 Sa’ad da suka isa wurin da Allah ya faɗa masa, sai Ibrahim ya gina bagade a can, ya kuma shisshirya itacen a kai. Ya ɗaura ɗansa Ishaku, ya kwantar da shi a kan itacen, a bisa bagaden.
Eles vieram ao lugar de que Deus lhe havia falado. Abraão construiu ali o altar, e colocou a madeira em ordem, amarrou Isaque seu filho, e o colocou sobre o altar, sobre a madeira.
10 Sa’an nan Ibrahim ya miƙa hannunsa ya ɗauki wuƙar don yă yanka ɗansa.
Abraão estendeu sua mão e pegou a faca para matar seu filho.
11 Amma mala’ikan Ubangiji ya kira shi daga sama ya ce, “Ibrahim, Ibrahim!” Sai Ibrahim ya amsa ya ce, “Ga ni.”
O anjo de Javé o chamou do céu, e disse: “Abraão, Abraão!” Ele disse: “Aqui estou eu”.
12 Mala’ikan ya ce, “Kada ka yi wa yaron nan rauni. Kada kuma ka ji masa ciwo. Yanzu na san cewa kana tsoron Allah, gama ba ka hana ni ɗanka, makaɗaicin ɗanka ba.”
Ele disse: “Não coloque sua mão sobre o menino ou faça nada com ele”. Por enquanto sei que você teme a Deus, já que não me escondeu seu filho, seu único filho”.
13 Ibrahim ya ɗaga ido, ya duba, sai ya ga rago da ƙahoninsa a kafe a wani ɗan kurmi. Sai Ibrahim ya tafi ya kamo ragon ya miƙa shi hadaya ta ƙonawa a maimakon ɗansa.
Abraham levantou os olhos, olhou e viu que atrás dele estava um carneiro preso na mata por seus chifres. Abraão foi e pegou o carneiro, e o ofereceu em troca de um holocausto em vez de seu filho.
14 Ibrahim kuwa ya ba wa wurin suna, Ubangiji Zai Tanada. Gama kamar yadda ake ce har yă zuwa yau, “A bisan dutsen Ubangiji, za a tanada.”
Abraão chamou o nome daquele lugar de “Yahweh proverá”. Como é dito até hoje, “Na montanha de Yahweh, será providenciado”.
15 Mala’ikan Ubangiji ya kira Ibrahim daga sama sau na biyu
O anjo de Javé chamou Abraão uma segunda vez do céu,
16 ya ce, “Na rantse da kaina, in ji Ubangiji, domin ka yi wannan, ba ka kuwa hana ni ɗanka, makaɗaicin ɗanka ba,
e disse: “'Jurei por mim mesmo', diz Javé, 'porque você fez esta coisa, e não reteve seu filho, seu único filho,
17 tabbatacce zan albarkace ka, zan kuma sa zuriyarka su yi yawa kamar taurari a sararin sama, kamar kuma yashi a bakin teku. Zuriyarka za su mallaki biranen abokan gābansu,
que eu o abençoarei muito, e multiplicarei seus descendentes como as estrelas dos céus, e como a areia que está na praia. Sua prole possuirá o portão de seus inimigos.
18 ta wurin zuriyarka kuma dukan al’umman duniya za su sami albarka, domin ka yi mini biyayya.”
Todas as nações da terra serão abençoadas por sua descendência, porque você obedeceu à minha voz”.
19 Sa’an nan Ibrahim ya koma wurin bayinsa, suka kuma kama hanya tare zuwa Beyersheba. Ibrahim kuwa ya yi zamansa a Beyersheba.
Então Abraão voltou para seus jovens, e eles se levantaram e foram juntos para Beersheba. Abraão viveu em Beersheba.
20 Bayan wani ɗan lokaci, sai aka faɗa wa Ibrahim cewa, “Ga shi, Milka ita ma ta haifa wa Nahor ɗan’uwanka,’ya’ya maza;
Depois destas coisas, foi dito a Abraão: “Eis Milcah, ela também deu à luz filhos a seu irmão Nahor:
21 ɗan fari shi ne Uz, ɗan’uwansa kuma Buz, Kemuwel (shi ne mahaifin Aram),
Uz seu primogênito, Buz seu irmão, Kemuel o pai de Aram,
22 Kesed, Hazo, Fildash; Yidlaf, da kuma Betuwel.”
Chesed, Hazo, Pildash, Jidlaph, e Bethuel”.
23 Betuwel ya haifi Rebeka. Milka ta haifa wa Nahor ɗan’uwan Ibrahim waɗannan’ya’ya maza takwas.
Bethuel tornou-se o pai de Rebekah. Estes oito Milcah aborreceram Nahor, irmão de Abraham.
24 Ban da haka ma, ƙwarƙwararsa, mai suna Reyuma, ta haifa masa’ya’ya maza, Teba, Gaham, Tahash da kuma Ma’aka.
Sua concubina, cujo nome era Reumah, também deu à luz Tebah, Gaham, Tahash, e Maacah.

< Farawa 22 >