< Farawa 22 >
1 Bayan abubuwan nan suka faru, sai Allah ya gwada Ibrahim. Ya ce masa, “Ibrahim!” Ibrahim ya amsa ya ce, “Ga ni.”
And it came to pass after these things, that God tested Abraham, and said to him, Abraham: and he said, Behold, here I am.
2 Sai Allah ya ce, “Ka ɗauki ɗanka, makaɗaicin ɗanka Ishaku, wanda kake ƙauna, ka tafi yankin Moriya, ka miƙa shi hadaya ta ƙonawa a can a kan ɗaya daga cikin duwatsun da zan nuna maka.”
And he said, Take now thy son, thy only son Isaac, whom thou lovest, and go into the land of Moriah; and offer him there for a burnt offering upon one of the mountains which I will tell thee of.
3 Kashegari da sassafe, Ibrahim ya tashi ya ɗaura wa jakinsa sirdi. Ya ɗauki bayinsa biyu, da ɗansa Ishaku. Bayan ya faskare isashen itace saboda hadaya ta ƙonawa sai ya kama hanya zuwa wurin da Allah ya faɗa masa.
And Abraham rose early in the morning, and saddled his donkey, and took two of his young men with him, and Isaac his son, and cut up the wood for the burnt offering, and rose, and went to the place which God had told him.
4 A rana ta uku Ibrahim ya ɗaga ido sai ya ga wurin daga nesa.
Then on the third day Abraham lifted up his eyes, and saw the place afar off.
5 Ibrahim ya ce wa bayinsa, “Ku tsaya a nan da jakin, ni da yaron kuwa mu haura can. Za mu yi sujada sa’an nan mu komo wurinku.”
And Abraham said to his young men, Abide ye here with the donkey; and I and the lad will go yonder and worship, and return to you.
6 Ibrahim ya ɗauki itace saboda hadaya ta ƙonawa ya ɗora wa ɗansa Ishaku, shi kuwa ya riƙe wuƙa da wutar. Yayinda su biyun suke tafiya,
And Abraham took the wood of the burnt offering, and laid it upon Isaac his son; and he took the fire in his hand, and a knife; and they went both of them together.
7 sai Ishaku ya yi tambaya, ya ce wa mahaifinsa Ibrahim, “Baba?” Ibrahim ya ce masa, “Na’am ɗana!” Ishaku ya ce, “Ga dai wuta, ga kuma itace, amma ina ɗan ragon hadaya ta ƙonawa?”
And Isaac spoke to Abraham his father, and said, My father: and he said, Here am I, my son. And he said, Behold the fire and the wood: but where is the lamb for a burnt offering?
8 Ibrahim ya amsa ya ce, “Ɗana, Allah kansa zai tanada ɗan ragon hadayar ƙonawa.” Sai su biyu suka ci gaba da tafiya.
And Abraham said, My son, God will provide himself a lamb for a burnt offering: so they went both of them together.
9 Sa’ad da suka isa wurin da Allah ya faɗa masa, sai Ibrahim ya gina bagade a can, ya kuma shisshirya itacen a kai. Ya ɗaura ɗansa Ishaku, ya kwantar da shi a kan itacen, a bisa bagaden.
And they came to the place which God had told him of; and Abraham built an altar there, and laid the wood in order, and bound Isaac his son, and laid him on the altar upon the wood.
10 Sa’an nan Ibrahim ya miƙa hannunsa ya ɗauki wuƙar don yă yanka ɗansa.
And Abraham stretched forth his hand, and took the knife to slay his son.
11 Amma mala’ikan Ubangiji ya kira shi daga sama ya ce, “Ibrahim, Ibrahim!” Sai Ibrahim ya amsa ya ce, “Ga ni.”
And the angel of the LORD called to him from heaven, and said, Abraham, Abraham: and he said, Here am I.
12 Mala’ikan ya ce, “Kada ka yi wa yaron nan rauni. Kada kuma ka ji masa ciwo. Yanzu na san cewa kana tsoron Allah, gama ba ka hana ni ɗanka, makaɗaicin ɗanka ba.”
And he said, Lay not thy hand upon the lad, neither do thou any thing to him: for now I know that thou fearest God, seeing thou hast not withheld from me thy son, thy only son.
13 Ibrahim ya ɗaga ido, ya duba, sai ya ga rago da ƙahoninsa a kafe a wani ɗan kurmi. Sai Ibrahim ya tafi ya kamo ragon ya miƙa shi hadaya ta ƙonawa a maimakon ɗansa.
And Abraham lifted up his eyes, and looked, and behold behind him a ram caught in a thicket by his horns: and Abraham went and took the ram, and offered him for a burnt offering in the stead of his son.
14 Ibrahim kuwa ya ba wa wurin suna, Ubangiji Zai Tanada. Gama kamar yadda ake ce har yă zuwa yau, “A bisan dutsen Ubangiji, za a tanada.”
And Abraham called the name of that place Jehovahjireh: as it is said to this day, In the mount of the LORD it shall be seen.
15 Mala’ikan Ubangiji ya kira Ibrahim daga sama sau na biyu
And the angel of the LORD called to Abraham from heaven the second time,
16 ya ce, “Na rantse da kaina, in ji Ubangiji, domin ka yi wannan, ba ka kuwa hana ni ɗanka, makaɗaicin ɗanka ba,
And said, By myself have I sworn, saith the LORD, for because thou hast done this thing, and hast not withheld thy son, thy only son:
17 tabbatacce zan albarkace ka, zan kuma sa zuriyarka su yi yawa kamar taurari a sararin sama, kamar kuma yashi a bakin teku. Zuriyarka za su mallaki biranen abokan gābansu,
That in blessing I will bless thee, and in multiplying I will multiply thy seed as the stars of heaven, and as the sand which is on the sea shore; and thy seed shall possess the gate of his enemies;
18 ta wurin zuriyarka kuma dukan al’umman duniya za su sami albarka, domin ka yi mini biyayya.”
And in thy seed shall all the nations of the earth be blessed; because thou hast obeyed my voice.
19 Sa’an nan Ibrahim ya koma wurin bayinsa, suka kuma kama hanya tare zuwa Beyersheba. Ibrahim kuwa ya yi zamansa a Beyersheba.
So Abraham returned to his young men, and they rose and went together to Beersheba; and Abraham dwelt at Beersheba.
20 Bayan wani ɗan lokaci, sai aka faɗa wa Ibrahim cewa, “Ga shi, Milka ita ma ta haifa wa Nahor ɗan’uwanka,’ya’ya maza;
And it came to pass after these things, that it was told to Abraham, saying, Behold, Milcah, she hath also borne children to thy brother Nahor;
21 ɗan fari shi ne Uz, ɗan’uwansa kuma Buz, Kemuwel (shi ne mahaifin Aram),
Huz his firstborn, and Buz his brother, and Kemuel the father of Aram,
22 Kesed, Hazo, Fildash; Yidlaf, da kuma Betuwel.”
And Chesed, and Hazo, and Pildash, and Jidlaph, and Bethuel.
23 Betuwel ya haifi Rebeka. Milka ta haifa wa Nahor ɗan’uwan Ibrahim waɗannan’ya’ya maza takwas.
And Bethuel begat Rebekah: these eight Milcah bore to Nahor, Abraham’s brother.
24 Ban da haka ma, ƙwarƙwararsa, mai suna Reyuma, ta haifa masa’ya’ya maza, Teba, Gaham, Tahash da kuma Ma’aka.
And his concubine, whose name was Reumah, she bore also Tebah, and Gaham, and Thahash, and Maachah.