< Farawa 22 >
1 Bayan abubuwan nan suka faru, sai Allah ya gwada Ibrahim. Ya ce masa, “Ibrahim!” Ibrahim ya amsa ya ce, “Ga ni.”
and to be after [the] word: thing [the] these and [the] God to test [obj] Abraham and to say to(wards) him Abraham and to say behold I
2 Sai Allah ya ce, “Ka ɗauki ɗanka, makaɗaicin ɗanka Ishaku, wanda kake ƙauna, ka tafi yankin Moriya, ka miƙa shi hadaya ta ƙonawa a can a kan ɗaya daga cikin duwatsun da zan nuna maka.”
and to say to take: take please [obj] (son: child your *LA(bh)*) [obj] only your which to love: lover [obj] Isaac and to go: went to/for you to(wards) land: country/planet [the] (Mount) Moriah and to ascend: offer up him there to/for burnt offering upon one [the] mountain: mount which to say to(wards) you
3 Kashegari da sassafe, Ibrahim ya tashi ya ɗaura wa jakinsa sirdi. Ya ɗauki bayinsa biyu, da ɗansa Ishaku. Bayan ya faskare isashen itace saboda hadaya ta ƙonawa sai ya kama hanya zuwa wurin da Allah ya faɗa masa.
and to rise Abraham in/on/with morning and to saddle/tie [obj] donkey his and to take: take [obj] two youth his with him and [obj] Isaac son: child his and to break up/open tree: wood burnt offering and to arise: rise and to go: went to(wards) [the] place which to say to/for him [the] God
4 A rana ta uku Ibrahim ya ɗaga ido sai ya ga wurin daga nesa.
in/on/with day [the] third and to lift: look Abraham [obj] eye his and to see: see [obj] [the] place from distant
5 Ibrahim ya ce wa bayinsa, “Ku tsaya a nan da jakin, ni da yaron kuwa mu haura can. Za mu yi sujada sa’an nan mu komo wurinku.”
and to say Abraham to(wards) youth his to dwell to/for you here with [the] donkey and I and [the] youth to go: went till thus and to bow and to return: again to(wards) you
6 Ibrahim ya ɗauki itace saboda hadaya ta ƙonawa ya ɗora wa ɗansa Ishaku, shi kuwa ya riƙe wuƙa da wutar. Yayinda su biyun suke tafiya,
and to take: take Abraham [obj] tree: wood [the] burnt offering and to set: put upon Isaac son: child his and to take: take in/on/with hand his [obj] [the] fire and [obj] [the] knife and to go: went two their together
7 sai Ishaku ya yi tambaya, ya ce wa mahaifinsa Ibrahim, “Baba?” Ibrahim ya ce masa, “Na’am ɗana!” Ishaku ya ce, “Ga dai wuta, ga kuma itace, amma ina ɗan ragon hadaya ta ƙonawa?”
and to say Isaac to(wards) Abraham father his and to say father my and to say behold I son: child my and to say behold [the] fire and [the] tree: wood and where? [the] sheep to/for burnt offering
8 Ibrahim ya amsa ya ce, “Ɗana, Allah kansa zai tanada ɗan ragon hadayar ƙonawa.” Sai su biyu suka ci gaba da tafiya.
and to say Abraham God to see: select to/for him [the] sheep to/for burnt offering son: child my and to go: went two their together
9 Sa’ad da suka isa wurin da Allah ya faɗa masa, sai Ibrahim ya gina bagade a can, ya kuma shisshirya itacen a kai. Ya ɗaura ɗansa Ishaku, ya kwantar da shi a kan itacen, a bisa bagaden.
and to come (in): come to(wards) [the] place which to say to/for him [the] God and to build there Abraham [obj] [the] altar and to arrange [obj] [the] tree: wood and to bind [obj] Isaac son: child his and to set: put [obj] him upon [the] altar from above to/for tree: wood
10 Sa’an nan Ibrahim ya miƙa hannunsa ya ɗauki wuƙar don yă yanka ɗansa.
and to send: reach Abraham [obj] hand his and to take: take [obj] [the] knife to/for to slaughter [obj] son: child his
11 Amma mala’ikan Ubangiji ya kira shi daga sama ya ce, “Ibrahim, Ibrahim!” Sai Ibrahim ya amsa ya ce, “Ga ni.”
and to call: call to to(wards) him messenger: angel LORD from [the] heaven and to say Abraham Abraham and to say behold I
12 Mala’ikan ya ce, “Kada ka yi wa yaron nan rauni. Kada kuma ka ji masa ciwo. Yanzu na san cewa kana tsoron Allah, gama ba ka hana ni ɗanka, makaɗaicin ɗanka ba.”
and to say not to send: reach hand your to(wards) [the] youth and not to make: do to/for him anything for now to know for afraid God you(m. s.) and not to withhold [obj] son: child your [obj] only your from me
13 Ibrahim ya ɗaga ido, ya duba, sai ya ga rago da ƙahoninsa a kafe a wani ɗan kurmi. Sai Ibrahim ya tafi ya kamo ragon ya miƙa shi hadaya ta ƙonawa a maimakon ɗansa.
and to lift: look Abraham [obj] eye his and to see: see and behold ram after to grasp in/on/with thicket in/on/with horn his and to go: went Abraham and to take: take [obj] [the] ram and to ascend: offer up him to/for burnt offering underneath: instead son: child his
14 Ibrahim kuwa ya ba wa wurin suna, Ubangiji Zai Tanada. Gama kamar yadda ake ce har yă zuwa yau, “A bisan dutsen Ubangiji, za a tanada.”
and to call: call by Abraham name [the] place [the] he/she/it LORD Provider which to say [the] day: today in/on/with mountain: mount LORD to see: see
15 Mala’ikan Ubangiji ya kira Ibrahim daga sama sau na biyu
and to call: call to messenger: angel LORD to(wards) Abraham second from [the] heaven
16 ya ce, “Na rantse da kaina, in ji Ubangiji, domin ka yi wannan, ba ka kuwa hana ni ɗanka, makaɗaicin ɗanka ba,
and to say in/on/with me to swear utterance LORD for because which to make: do [obj] [the] word: thing [the] this and not to withhold [obj] son: child your [obj] only your
17 tabbatacce zan albarkace ka, zan kuma sa zuriyarka su yi yawa kamar taurari a sararin sama, kamar kuma yashi a bakin teku. Zuriyarka za su mallaki biranen abokan gābansu,
for to bless to bless you and to multiply to multiply [obj] seed: children your like/as star [the] heaven and like/as sand which upon lip: shore [the] sea and to possess: take seed: children your [obj] gate enemy his
18 ta wurin zuriyarka kuma dukan al’umman duniya za su sami albarka, domin ka yi mini biyayya.”
and to bless in/on/with seed: children your all nation [the] land: country/planet consequence which to hear: obey in/on/with voice my
19 Sa’an nan Ibrahim ya koma wurin bayinsa, suka kuma kama hanya tare zuwa Beyersheba. Ibrahim kuwa ya yi zamansa a Beyersheba.
and to return: return Abraham to(wards) youth his and to arise: rise and to go: went together to(wards) Beersheba Beersheba and to dwell Abraham in/on/with Beersheba Beersheba
20 Bayan wani ɗan lokaci, sai aka faɗa wa Ibrahim cewa, “Ga shi, Milka ita ma ta haifa wa Nahor ɗan’uwanka,’ya’ya maza;
and to be after [the] word: thing [the] these and to tell to/for Abraham to/for to say behold to beget Milcah also he/she/it son: child to/for Nahor brother: male-sibling your
21 ɗan fari shi ne Uz, ɗan’uwansa kuma Buz, Kemuwel (shi ne mahaifin Aram),
[obj] Uz firstborn his and [obj] Buz brother: male-sibling his and [obj] Kemuel father Aram
22 Kesed, Hazo, Fildash; Yidlaf, da kuma Betuwel.”
and [obj] Chesed and [obj] Hazo and [obj] Pildash and [obj] Jidlaph and [obj] Bethuel
23 Betuwel ya haifi Rebeka. Milka ta haifa wa Nahor ɗan’uwan Ibrahim waɗannan’ya’ya maza takwas.
and Bethuel to beget [obj] Rebekah eight these to beget Milcah to/for Nahor brother: male-sibling Abraham
24 Ban da haka ma, ƙwarƙwararsa, mai suna Reyuma, ta haifa masa’ya’ya maza, Teba, Gaham, Tahash da kuma Ma’aka.
and concubine his and name her Reumah and to beget also he/she/it [obj] Tebah and [obj] Gaham and [obj] Tahash and [obj] Maacah