< Farawa 22 >
1 Bayan abubuwan nan suka faru, sai Allah ya gwada Ibrahim. Ya ce masa, “Ibrahim!” Ibrahim ya amsa ya ce, “Ga ni.”
And it comes to pass after these things that God has tried Abraham and says to him, “Abraham”; and he says, “Here I [am].”
2 Sai Allah ya ce, “Ka ɗauki ɗanka, makaɗaicin ɗanka Ishaku, wanda kake ƙauna, ka tafi yankin Moriya, ka miƙa shi hadaya ta ƙonawa a can a kan ɗaya daga cikin duwatsun da zan nuna maka.”
And He says, “Now take your son, your only one, whom you have loved, even Isaac, and go for yourself to the land of Moriah, and cause him to ascend there for a burnt-offering on one of the mountains of which I speak to you.”
3 Kashegari da sassafe, Ibrahim ya tashi ya ɗaura wa jakinsa sirdi. Ya ɗauki bayinsa biyu, da ɗansa Ishaku. Bayan ya faskare isashen itace saboda hadaya ta ƙonawa sai ya kama hanya zuwa wurin da Allah ya faɗa masa.
And Abraham rises early in the morning, and saddles his donkey, and takes two of his young men with him, and his son Isaac, and he cleaves the wood of the burnt-offering, and rises and goes to the place of which God has spoken to him.
4 A rana ta uku Ibrahim ya ɗaga ido sai ya ga wurin daga nesa.
On the third day—Abraham lifts up his eyes, and sees the place from afar;
5 Ibrahim ya ce wa bayinsa, “Ku tsaya a nan da jakin, ni da yaron kuwa mu haura can. Za mu yi sujada sa’an nan mu komo wurinku.”
and Abraham says to his young men, “Remain by yourselves here with the donkey, and I and the youth go over there and worship, and return to you.”
6 Ibrahim ya ɗauki itace saboda hadaya ta ƙonawa ya ɗora wa ɗansa Ishaku, shi kuwa ya riƙe wuƙa da wutar. Yayinda su biyun suke tafiya,
And Abraham takes the wood of the burnt-offering, and places on his son Isaac, and he takes in his hand the fire, and the knife; and they go on both of them together.
7 sai Ishaku ya yi tambaya, ya ce wa mahaifinsa Ibrahim, “Baba?” Ibrahim ya ce masa, “Na’am ɗana!” Ishaku ya ce, “Ga dai wuta, ga kuma itace, amma ina ɗan ragon hadaya ta ƙonawa?”
And Isaac speaks to his father Abraham and says, “My father,” and he says, “Here I [am], my son.” And he says, “Behold, the fire and the wood, and where the lamb for a burnt-offering?”
8 Ibrahim ya amsa ya ce, “Ɗana, Allah kansa zai tanada ɗan ragon hadayar ƙonawa.” Sai su biyu suka ci gaba da tafiya.
And Abraham says, “God provides for Himself the lamb for a burnt-offering, my son”; and they go on both of them together.
9 Sa’ad da suka isa wurin da Allah ya faɗa masa, sai Ibrahim ya gina bagade a can, ya kuma shisshirya itacen a kai. Ya ɗaura ɗansa Ishaku, ya kwantar da shi a kan itacen, a bisa bagaden.
And they come to the place of which God has spoken to him, and there Abraham builds the altar, and arranges the wood, and binds his son Isaac, and places him on the altar above the wood;
10 Sa’an nan Ibrahim ya miƙa hannunsa ya ɗauki wuƙar don yă yanka ɗansa.
and Abraham puts forth his hand, and takes the knife—to slaughter his son.
11 Amma mala’ikan Ubangiji ya kira shi daga sama ya ce, “Ibrahim, Ibrahim!” Sai Ibrahim ya amsa ya ce, “Ga ni.”
And the Messenger of YHWH calls to him from the heavens and says, “Abraham, Abraham”; and he says, “Here I [am]”;
12 Mala’ikan ya ce, “Kada ka yi wa yaron nan rauni. Kada kuma ka ji masa ciwo. Yanzu na san cewa kana tsoron Allah, gama ba ka hana ni ɗanka, makaɗaicin ɗanka ba.”
and He says, “Do not put forth your hand to the youth, nor do anything to him, for now I have known that you are fearing God, and have not withheld your son, your only one, from Me.”
13 Ibrahim ya ɗaga ido, ya duba, sai ya ga rago da ƙahoninsa a kafe a wani ɗan kurmi. Sai Ibrahim ya tafi ya kamo ragon ya miƙa shi hadaya ta ƙonawa a maimakon ɗansa.
And Abraham lifts up his eyes, and looks, and behold, a ram behind, seized in a thicket by its horns; and Abraham goes, and takes the ram, and causes it to ascend for a burnt-offering instead of his son;
14 Ibrahim kuwa ya ba wa wurin suna, Ubangiji Zai Tanada. Gama kamar yadda ake ce har yă zuwa yau, “A bisan dutsen Ubangiji, za a tanada.”
and Abraham calls the name of that place “YHWH-Jireh,” because it is said this day in the mountain, “YHWH provides.”
15 Mala’ikan Ubangiji ya kira Ibrahim daga sama sau na biyu
And the Messenger of YHWH calls to Abraham a second time from the heavens,
16 ya ce, “Na rantse da kaina, in ji Ubangiji, domin ka yi wannan, ba ka kuwa hana ni ɗanka, makaɗaicin ɗanka ba,
and says, “I have sworn by Myself—a declaration of YHWH—that because you have done this thing, and have not withheld your son, your only one,
17 tabbatacce zan albarkace ka, zan kuma sa zuriyarka su yi yawa kamar taurari a sararin sama, kamar kuma yashi a bakin teku. Zuriyarka za su mallaki biranen abokan gābansu,
that blessing I bless you, and multiplying I multiply your seed as stars of the heavens, and as sand which [is] on the seashore; and your Seed possesses the gate of His enemies;
18 ta wurin zuriyarka kuma dukan al’umman duniya za su sami albarka, domin ka yi mini biyayya.”
and all nations of the earth have blessed themselves in your Seed, because you have listened to My voice.”
19 Sa’an nan Ibrahim ya koma wurin bayinsa, suka kuma kama hanya tare zuwa Beyersheba. Ibrahim kuwa ya yi zamansa a Beyersheba.
And Abraham turns back to his young men, and they rise and go together to Beer-Sheba; and Abraham dwells in Beer-Sheba.
20 Bayan wani ɗan lokaci, sai aka faɗa wa Ibrahim cewa, “Ga shi, Milka ita ma ta haifa wa Nahor ɗan’uwanka,’ya’ya maza;
And it comes to pass after these things that it is declared to Abraham, saying, “Behold, Milcah has borne, even she, sons to your brother Nahor:
21 ɗan fari shi ne Uz, ɗan’uwansa kuma Buz, Kemuwel (shi ne mahaifin Aram),
his firstborn Huz, and his brother Buz; and Kemuel father of Aram,
22 Kesed, Hazo, Fildash; Yidlaf, da kuma Betuwel.”
and Chesed, and Hazo, and Pildash, and Jidlaph, and Bethuel;
23 Betuwel ya haifi Rebeka. Milka ta haifa wa Nahor ɗan’uwan Ibrahim waɗannan’ya’ya maza takwas.
and Bethuel has begotten Rebekah”; Milcah has borne these eight to Nahor, Abraham’s brother;
24 Ban da haka ma, ƙwarƙwararsa, mai suna Reyuma, ta haifa masa’ya’ya maza, Teba, Gaham, Tahash da kuma Ma’aka.
and his concubine, whose name [is] Reumah, she also has borne Tebah, and Gaham, and Tahash, and Maachah.