< Farawa 22 >

1 Bayan abubuwan nan suka faru, sai Allah ya gwada Ibrahim. Ya ce masa, “Ibrahim!” Ibrahim ya amsa ya ce, “Ga ni.”
Efter disse Begivenheder satte Gud Abraham paa Prøve og sagde til ham: »Abraham!« Han svarede: »Se, her er jeg!«
2 Sai Allah ya ce, “Ka ɗauki ɗanka, makaɗaicin ɗanka Ishaku, wanda kake ƙauna, ka tafi yankin Moriya, ka miƙa shi hadaya ta ƙonawa a can a kan ɗaya daga cikin duwatsun da zan nuna maka.”
Da sagde han: »Tag din Søn Isak, din eneste, ham, du elsker, og drag hen til Morija Land og bring ham der som Brændoffer paa et af Bjergene, som jeg vil vise dig!«
3 Kashegari da sassafe, Ibrahim ya tashi ya ɗaura wa jakinsa sirdi. Ya ɗauki bayinsa biyu, da ɗansa Ishaku. Bayan ya faskare isashen itace saboda hadaya ta ƙonawa sai ya kama hanya zuwa wurin da Allah ya faɗa masa.
Da sadlede Abraham tidligt næste Morgen sit Æsel, tog to af sine Drenge og sin Søn Isak med sig, og efter at have kløvet Offerbrænde gav han sig paa Vandring; til det Sted, Gud havde sagt ham.
4 A rana ta uku Ibrahim ya ɗaga ido sai ya ga wurin daga nesa.
Da Abraham den tredje Dag saa op, fik han Øje paa Stedet langt borte.
5 Ibrahim ya ce wa bayinsa, “Ku tsaya a nan da jakin, ni da yaron kuwa mu haura can. Za mu yi sujada sa’an nan mu komo wurinku.”
Saa sagde Abraham til sine Drenge: »Bliv her med Æselet, medens jeg og Drengen vandrer derhen for at tilbede; saa kommer vi tilbage til eder.«
6 Ibrahim ya ɗauki itace saboda hadaya ta ƙonawa ya ɗora wa ɗansa Ishaku, shi kuwa ya riƙe wuƙa da wutar. Yayinda su biyun suke tafiya,
Abraham tog da Brændet til Brændofferet og lagde det paa sin Søn Isak; selv tog han Ilden og Offerkniven, og saa gik de to sammen.
7 sai Ishaku ya yi tambaya, ya ce wa mahaifinsa Ibrahim, “Baba?” Ibrahim ya ce masa, “Na’am ɗana!” Ishaku ya ce, “Ga dai wuta, ga kuma itace, amma ina ɗan ragon hadaya ta ƙonawa?”
Da sagde Isak til sin Fader Abraham: »Fader!« Han svarede: »Ja, min Søn!« Da sagde han: »Her er Ilden og Brændet, men hvor er Dyret til Brændofferet?«
8 Ibrahim ya amsa ya ce, “Ɗana, Allah kansa zai tanada ɗan ragon hadayar ƙonawa.” Sai su biyu suka ci gaba da tafiya.
Abraham svarede: »Gud vil selv udse sig Dyret til Brændofferet, min Søn!« Og saa gik de to sammen.
9 Sa’ad da suka isa wurin da Allah ya faɗa masa, sai Ibrahim ya gina bagade a can, ya kuma shisshirya itacen a kai. Ya ɗaura ɗansa Ishaku, ya kwantar da shi a kan itacen, a bisa bagaden.
Da de naaede det Sted, Gud havde sagt ham, byggede Abraham der et Alter og lagde Brændet til Rette; saa bandt han sin Søn Isak og lagde ham paa Alteret oven paa Brændet.
10 Sa’an nan Ibrahim ya miƙa hannunsa ya ɗauki wuƙar don yă yanka ɗansa.
Og Abraham greb Kniven og rakte Haanden ud for at slagte sin Søn.
11 Amma mala’ikan Ubangiji ya kira shi daga sama ya ce, “Ibrahim, Ibrahim!” Sai Ibrahim ya amsa ya ce, “Ga ni.”
Da raabte HERRENS Engel til ham fra Himmelen: »Abraham, Abraham!« Han svarede: »Se, her er jeg!«
12 Mala’ikan ya ce, “Kada ka yi wa yaron nan rauni. Kada kuma ka ji masa ciwo. Yanzu na san cewa kana tsoron Allah, gama ba ka hana ni ɗanka, makaɗaicin ɗanka ba.”
Da sagde Engelen: »Ræk ikke din Haand ud mod Drengen og gør ham ikke noget; thi nu ved jeg, at du frygter Gud og end ikke sparer din Søn, din eneste, for mig!«
13 Ibrahim ya ɗaga ido, ya duba, sai ya ga rago da ƙahoninsa a kafe a wani ɗan kurmi. Sai Ibrahim ya tafi ya kamo ragon ya miƙa shi hadaya ta ƙonawa a maimakon ɗansa.
Og da Abraham nu saa op, fik han bag ved sig Øje paa en Væder, hvis Horn havde viklet sig ind i de tætte Grene; og Abraham gik hen og tog Væderen og ofrede den som Brændoffer i sin Søns Sted.
14 Ibrahim kuwa ya ba wa wurin suna, Ubangiji Zai Tanada. Gama kamar yadda ake ce har yă zuwa yau, “A bisan dutsen Ubangiji, za a tanada.”
Derfor kaldte Abraham dette Sted: HERREN udser sig, eller, som man nu til Dags siger: Bjerget, hvor HERREN viser sig.
15 Mala’ikan Ubangiji ya kira Ibrahim daga sama sau na biyu
Men HERRENS Engel raabte atter til Abraham fra Himmelen:
16 ya ce, “Na rantse da kaina, in ji Ubangiji, domin ka yi wannan, ba ka kuwa hana ni ɗanka, makaɗaicin ɗanka ba,
»Jeg sværger ved mig selv, lyder det fra HERREN: Fordi du har gjort dette og ikke sparet din Søn, din eneste, for mig,
17 tabbatacce zan albarkace ka, zan kuma sa zuriyarka su yi yawa kamar taurari a sararin sama, kamar kuma yashi a bakin teku. Zuriyarka za su mallaki biranen abokan gābansu,
saa vil jeg velsigne dig og gøre dit Afkom talrigt som Himmelens Stjerner og Sandet ved Havets Bred; og dit Afkom skal tage sine Fjenders Porte i Besiddelse;
18 ta wurin zuriyarka kuma dukan al’umman duniya za su sami albarka, domin ka yi mini biyayya.”
og i din Sæd skal alle Jordens Folk velsignes, fordi du adlød mig!«
19 Sa’an nan Ibrahim ya koma wurin bayinsa, suka kuma kama hanya tare zuwa Beyersheba. Ibrahim kuwa ya yi zamansa a Beyersheba.
Derpaa vendte Abraham tilbage til sine Drenge, og de brød op og tog sammen til Be'ersjeba. Og Abraham blev i Be'ersjeba.
20 Bayan wani ɗan lokaci, sai aka faɗa wa Ibrahim cewa, “Ga shi, Milka ita ma ta haifa wa Nahor ɗan’uwanka,’ya’ya maza;
Efter disse Begivenheder meldte man Abraham: »Ogsaa Milka har født din Broder Nakor Sønner:
21 ɗan fari shi ne Uz, ɗan’uwansa kuma Buz, Kemuwel (shi ne mahaifin Aram),
Uz, hans førstefødte, dennes Broder Buz, Kemuel, Arams Fader,
22 Kesed, Hazo, Fildash; Yidlaf, da kuma Betuwel.”
Kesed, Hazo, Pildasj, Jidlaf og Betuel;
23 Betuwel ya haifi Rebeka. Milka ta haifa wa Nahor ɗan’uwan Ibrahim waɗannan’ya’ya maza takwas.
Betuel avlede Rebekka; disse otte har Milka født Abrahams Broder Nakor,
24 Ban da haka ma, ƙwarƙwararsa, mai suna Reyuma, ta haifa masa’ya’ya maza, Teba, Gaham, Tahash da kuma Ma’aka.
og desuden har hans Medhustru Re'uma født Teba, Gaham, Tahasj og Ma'aka.«

< Farawa 22 >