< Farawa 21 >

1 Ana nan sai Ubangiji ya nuna wa Saratu alheri kamar yadda ya ce, Ubangiji kuma ya yi wa Saratu abin da ya yi alkawari.
Forsothe God visitide Sare, as he bihiyte, and fillide tho thingis, that he spak.
2 Saratu ta yi ciki, ta kuma haifa wa Ibrahim ɗa a tsufansa; a daidai lokacin da Allah ya yi masa alkawari.
And sche conseyuede, and childide a sone in hir eeld, in the tyme wherynne God biforseide to hir.
3 Ibrahim ya sa wa ɗan da Saratu ta haifa masa suna Ishaku.
And Abraham clepide the name of his sone, whom Sare childide to him, Ysaac.
4 Sa’ad da ɗansa Ishaku ya kai kwana takwas da haihuwa, sai Ibrahim ya yi masa kaciya, kamar yadda Allah ya umarce shi.
And Abraham circumcidide hym in the eiyte dai, as God comaundide to him,
5 Ibrahim yana da shekara ɗari, sa’ad da aka haifa masa ɗansa Ishaku.
whanne he was of an hundrid yeer; for Ysaac was borun in this age of the fadir.
6 Saratu ta ce, “Allah ya sa na yi dariya, kuma duk wanda ya ji game da wannan, zai yi dariya tare da ni.”
And Sare seide, The Lord made leiyynge to me, and who euer schal here schal leiye with me.
7 Ta kuma ƙara da cewa, “Dā, wa zai iya ce wa Ibrahim, Saratu za tă yi renon yara? Duk da haka na haifar masa ɗa cikin tsufansa.”
And eft sche seide, Who schulde here, and bileue to Abraham, that Sare schulde yyue soukyng to a sone, whom sche childide to him now an eld man?
8 Yaron ya yi girma, aka kuma yaye shi, a ranar da aka yaye shi kuwa, Ibrahim ya yi babban biki.
Therfor the child encreesside, and was wenyd; and Abraham made a greet feeste in the dai of his wenyng.
9 Amma Saratu ta ga cewa yaron da Hagar, mutuniyar Masar ta haifa wa Ibrahim yana wa ɗanta Ishaku gori,
And whanne Sare seiy the sone of Agar Egipcian pleiynge with Ysaac hir sone, sche seide to Abraham,
10 sai ta ce wa Ibrahim, “Ka kori baiwan nan tare da ɗanta, saboda ɗan baiwan nan ba zai taɓa raba gādo da ɗana Ishaku ba.”
Cast thou out the handmayde and hir sone; for the sone of the handmayde schal not be eir with my sone Ysaac.
11 Al’amarin ya ɓata wa Ibrahim rai sosai domin zancen ya shafi ɗansa.
Abraham took this heuyli for his sone;
12 Amma Allah ya ce wa Ibrahim, “Kada hankalinka yă tashi game da yaron nan da kuma baiwarka. Ka saurari duk abin da Saratu ta faɗa maka, saboda ta wurin Ishaku ne za a lissafta zuriyarka.
and God seide to hym, Be it not seyn scharp to thee on the child, and on thin handmayde; alle thingis whiche Sare seith to thee, here thou hir vois, for in Isaac seed schal be clepid to thee;
13 Zan ba ɗan baiwan nan al’umma shi ma, domin shi zuriyarka ne.”
but also I schal make the sone of the handmaid in to a greet folk, for he is thi seed.
14 Kashegari da sassafe sai Ibrahim ya ɗauki abinci da salkar ruwa, ya ba wa Hagar. Ya ɗora su a kafaɗunta, sa’an nan ya sallame ta da yaron. Ta kama hanyarta ta kuma yi ta yawo a cikin jejin Beyersheba.
And so Abraham roos eerli, and took breed, and a botel of watir, and puttide on hir schuldre, and bitook the child, and lefte hir; and whanne sche hadde go, sche yede out of the weie in the wildirnesse of Bersabee.
15 Sa’ad da ruwan da yake cikin salkan ya ƙare, sai ta ajiye yaron a ƙarƙashin wani ƙaramin itace.
And whanne the watir in the botel was endid, sche castide awei the child vndur a tre that was there;
16 Sai ta tafi, ta zauna ɗan nesa da yaron, misalin nisan harbin baka, gama ta yi tunani ta ce, “Ba zan iya kallon yaron yana mutuwa ba.” Da ta zauna nesa da yaron, sai ta fara kuka.
and sche yede awei, and sche sat euene ayens as fer as a bowe may caste; for sche seide, Y schal not se the child diynge; and sche sat ayens, and reiside hir vois, and wepte.
17 Allah kuwa ya ji yaron yana kuka, sai mala’ikan Allah ya kira Hagar daga sama ya ce mata, “Mene ne damuwarki, Hagar? Kada ki ji tsoro, Allah ya ji yaron yana kuka yayinda yake kwance a can.
Forsothe the Lord herde the vois of the child, and the aungel of the Lord clepide Agar fro heuene, and seide, What doist thou, Agar? nyle thou drede, for God hath herd the vois of the child fro the place where ynne he is.
18 Ki ɗaga yaron ki riƙe shi a hannu, gama zan mai da shi al’umma mai girma.”
Rise thou, and take the child, and holde his hoond; for Y schal make hym in to a greet folc.
19 Sa’an nan Allah ya buɗe idanunta ta ga wata rijiyar ruwa. Don haka sai ta tafi ta cika salkan da ruwa, ta kuma ba wa yaron ruwa ya sha.
And God openyde hir iyen, and sche seiy a pit of watir, and sche yede, and fillide the botel, and sche yaf drynk to the child;
20 Allah ya kasance da yaron, yayinda yake girma. Ya yi zama a jeji, ya kuma zama maharbi.
and was with him, and he encresside, and dwellide in wildernesse, and he was maad a yong man an archer,
21 Yayinda yake zama a Jejin Faran, sai mahaifiyarsa ta samo masa mata daga Masar.
and dwellide in the deseert of Faran; and his modir took to him a wijf of the lond of Egipt.
22 A lokacin nan Abimelek da Fikol, komandan rundunoninsa suka zo suka ce wa Ibrahim, “Allah yana tare da kai a ko mene ne kake yi.
In the same tyme Abymelech, and Ficol, prince of his oost, seide to Abraham, God is with thee in alle thingis whiche thou doist;
23 Yanzu ka rantse mini a nan a gaban Allah cewa, ba za ka yaudare ni ko’ya’yana ko kuma zuriyata ba. Ka nuna mini alheri, kai da ƙasar da kake zama baƙunci kamar yadda na nuna maka.”
therfore swere thou bi God that thou noye not me, and myn eiris, and my kynrede; but bi the mersi whych Y dide to thee, do thou to me, and to the lond in which thou lyuedist a comelyng.
24 Ibrahim ya ce, “Na rantse.”
And Abraham seide, Y schal swere.
25 Sa’an nan Ibrahim ya kawo kuka ga Abimelek game da rijiyar ruwan da bayin Abimelek suka ƙwace.
And he blamyde Abymelech for the pit of watir, which hise seruauntis token awey bi violence.
26 Sai Abimelek ya ce, “Ban san wanda ya yi wannan ba. Ba ka faɗa mini ba, ban kuwa taɓa ji ba, sai yau.”
And Abymelech answerde, I wiste not who dide this thing, but also thou schewidist not to me, and Y herde not outakun to dai.
27 Sai Ibrahim ya kawo tumaki da shanu ya ba wa Abimelek, sai su biyun suka yi yarjejjeniya.
And so Abraham took scheep and oxun, and yaf to Abymalech, and bothe smyten a boond of pees.
28 Ibrahim ya ware’yan raguna bakwai daga cikin garke,
And Abraham settide seuene ewe lambren of the flok asidis half.
29 sai Abimelek ya ce wa Ibrahim, “Mene ne ma’anar’yan raguna bakwai da ka keɓe?”
And Abymelech seide to hym, What wolen these seuene ewe lambren to hem silf, whiche thou madist stonde asidis half?
30 Ibrahim ya amsa ya ce, “Ka karɓi waɗannan’yan tumaki bakwai daga hannuna a matsayin shaida cewa ni ne na haƙa wannan rijiya.”
And he seide, Thou schalt take of myn hond seuene ewe lambren, that tho be in to witnessyng to me, for Y diggide this pit.
31 Saboda haka aka kira wurin Beyersheba, domin a nan ne su biyun suka yi rantsuwa.
Therfor thilke place was clepid Bersabee, for euere eithir swore there;
32 Bayan da aka yi yarjejjeniya a Beyersheba, sai Abimelek da Fikol, komandan rundunoninsa suka koma ƙasar Filistiyawa.
and thei maden boond of pees for the pit of an ooth.
33 Sai Ibrahim ya shuka itacen tsamiya a Beyersheba, a can kuma ya kira bisa sunan Ubangiji, Allah Madawwami.
Forsothe Abymelech roos, and Ficol, prince of his chyualrie, and thei turneden ayen in to the lond of Palestyns. Sotheli Abraham plauntide a wode in Bersabee, and inwardli clepide there the name of euerlastinge God;
34 Ibrahim kuwa ya zauna a ƙasar Filistiyawa na dogon lokaci.
and he was an erthetiliere ether a comelynge of the lond of Palestynes in many dayes.

< Farawa 21 >