< Farawa 21 >

1 Ana nan sai Ubangiji ya nuna wa Saratu alheri kamar yadda ya ce, Ubangiji kuma ya yi wa Saratu abin da ya yi alkawari.
Yahweh paid attention to Sarah as he had said he would, and Yahweh did for Sarah just as he had promised.
2 Saratu ta yi ciki, ta kuma haifa wa Ibrahim ɗa a tsufansa; a daidai lokacin da Allah ya yi masa alkawari.
Sarah conceived and bore a son to Abraham in his old age, at the set time of which God had spoken to him.
3 Ibrahim ya sa wa ɗan da Saratu ta haifa masa suna Ishaku.
Abraham named his son, the one who had been born to him, whom Sarah bore to him, Isaac.
4 Sa’ad da ɗansa Ishaku ya kai kwana takwas da haihuwa, sai Ibrahim ya yi masa kaciya, kamar yadda Allah ya umarce shi.
Abraham circumcised his son Isaac when he was eight days old, just as God had commanded him.
5 Ibrahim yana da shekara ɗari, sa’ad da aka haifa masa ɗansa Ishaku.
Abraham was one hundred years old when his son Isaac was born to him.
6 Saratu ta ce, “Allah ya sa na yi dariya, kuma duk wanda ya ji game da wannan, zai yi dariya tare da ni.”
Sarah said, “God has made me laugh; every one who hears will laugh with me.”
7 Ta kuma ƙara da cewa, “Dā, wa zai iya ce wa Ibrahim, Saratu za tă yi renon yara? Duk da haka na haifar masa ɗa cikin tsufansa.”
She also said, “Who would have said to Abraham that Sarah would nurse children, and yet I have borne him a son in his old age!”
8 Yaron ya yi girma, aka kuma yaye shi, a ranar da aka yaye shi kuwa, Ibrahim ya yi babban biki.
The child grew and was weaned, and Abraham made a great feast on the day that Isaac was weaned.
9 Amma Saratu ta ga cewa yaron da Hagar, mutuniyar Masar ta haifa wa Ibrahim yana wa ɗanta Ishaku gori,
Sarah saw the son of Hagar the Egyptian, whom she had borne to Abraham, mocking.
10 sai ta ce wa Ibrahim, “Ka kori baiwan nan tare da ɗanta, saboda ɗan baiwan nan ba zai taɓa raba gādo da ɗana Ishaku ba.”
So she said to Abraham, “Drive out this slave woman and her son, for the son of this slave woman will not be heir with my son, with Isaac.”
11 Al’amarin ya ɓata wa Ibrahim rai sosai domin zancen ya shafi ɗansa.
This thing was very grievous to Abraham because of his son.
12 Amma Allah ya ce wa Ibrahim, “Kada hankalinka yă tashi game da yaron nan da kuma baiwarka. Ka saurari duk abin da Saratu ta faɗa maka, saboda ta wurin Ishaku ne za a lissafta zuriyarka.
But God said to Abraham, “Do not be grieved because of the lad, and because of your servant woman. Listen to her words in all she says to you about this matter, because it is through Isaac that your descendants will be named.
13 Zan ba ɗan baiwan nan al’umma shi ma, domin shi zuriyarka ne.”
I will also make the son of the servant woman into a nation, because he is your descendant.”
14 Kashegari da sassafe sai Ibrahim ya ɗauki abinci da salkar ruwa, ya ba wa Hagar. Ya ɗora su a kafaɗunta, sa’an nan ya sallame ta da yaron. Ta kama hanyarta ta kuma yi ta yawo a cikin jejin Beyersheba.
Abraham rose up early in the morning, took bread and a skin of water, and gave it to Hagar, putting it on her shoulder. He gave her the boy and sent her away. She departed and wandered in the wilderness of Beersheba.
15 Sa’ad da ruwan da yake cikin salkan ya ƙare, sai ta ajiye yaron a ƙarƙashin wani ƙaramin itace.
When the water in the waterskin was gone, she abandoned the child under one of the bushes.
16 Sai ta tafi, ta zauna ɗan nesa da yaron, misalin nisan harbin baka, gama ta yi tunani ta ce, “Ba zan iya kallon yaron yana mutuwa ba.” Da ta zauna nesa da yaron, sai ta fara kuka.
Then she went, and sat down a short distance from him, about the distance of a bowshot away, for she said, “Let me not look upon the death of the child.” As she sat there across from him, she lifted up her voice and wept.
17 Allah kuwa ya ji yaron yana kuka, sai mala’ikan Allah ya kira Hagar daga sama ya ce mata, “Mene ne damuwarki, Hagar? Kada ki ji tsoro, Allah ya ji yaron yana kuka yayinda yake kwance a can.
God heard the voice of the lad, and the angel of God called to Hagar out of heaven, and said to her, “What troubles you, Hagar? Do not be afraid, for God has heard the voice of the lad where he is.
18 Ki ɗaga yaron ki riƙe shi a hannu, gama zan mai da shi al’umma mai girma.”
Get up, raise up the lad, and encourage him; for I will make him into a great nation.”
19 Sa’an nan Allah ya buɗe idanunta ta ga wata rijiyar ruwa. Don haka sai ta tafi ta cika salkan da ruwa, ta kuma ba wa yaron ruwa ya sha.
Then God opened her eyes, and she saw a well of water. She went and filled the skin with water, and gave the lad a drink.
20 Allah ya kasance da yaron, yayinda yake girma. Ya yi zama a jeji, ya kuma zama maharbi.
God was with the lad, and he grew. He lived in the wilderness and became an archer.
21 Yayinda yake zama a Jejin Faran, sai mahaifiyarsa ta samo masa mata daga Masar.
He lived in the wilderness of Paran, and his mother got a wife for him from the land of Egypt.
22 A lokacin nan Abimelek da Fikol, komandan rundunoninsa suka zo suka ce wa Ibrahim, “Allah yana tare da kai a ko mene ne kake yi.
It came about at that time that Abimelech and Phicol the captain of his army spoke to Abraham, saying, “God is with you in all that you do.
23 Yanzu ka rantse mini a nan a gaban Allah cewa, ba za ka yaudare ni ko’ya’yana ko kuma zuriyata ba. Ka nuna mini alheri, kai da ƙasar da kake zama baƙunci kamar yadda na nuna maka.”
Now therefore swear to me here by God that you will not deal falsely with me, nor with my offspring, nor with my descendants. Show to me and to the land in which you have been staying the same covenant faithfulness that I have shown to you.”
24 Ibrahim ya ce, “Na rantse.”
Abraham said, “I swear.”
25 Sa’an nan Ibrahim ya kawo kuka ga Abimelek game da rijiyar ruwan da bayin Abimelek suka ƙwace.
Abraham also complained to Abimelech concerning a well of water that Abimelech's servants had seized from him.
26 Sai Abimelek ya ce, “Ban san wanda ya yi wannan ba. Ba ka faɗa mini ba, ban kuwa taɓa ji ba, sai yau.”
Abimelech said, “I do not know who has done this thing. You did not tell me before now; I have not heard of it until today.”
27 Sai Ibrahim ya kawo tumaki da shanu ya ba wa Abimelek, sai su biyun suka yi yarjejjeniya.
So Abraham took sheep and oxen and gave them to Abimelech, and the two men made a covenant.
28 Ibrahim ya ware’yan raguna bakwai daga cikin garke,
Then Abraham set seven female lambs of the flock by themselves.
29 sai Abimelek ya ce wa Ibrahim, “Mene ne ma’anar’yan raguna bakwai da ka keɓe?”
Abimelech said to Abraham, “What is the meaning of these seven female lambs that you have set by themselves?”
30 Ibrahim ya amsa ya ce, “Ka karɓi waɗannan’yan tumaki bakwai daga hannuna a matsayin shaida cewa ni ne na haƙa wannan rijiya.”
He replied, “These seven female lambs you will receive from my hand, so that it may be a witness for me, that I dug this well.”
31 Saboda haka aka kira wurin Beyersheba, domin a nan ne su biyun suka yi rantsuwa.
So he called that place Beersheba, because there they both swore an oath.
32 Bayan da aka yi yarjejjeniya a Beyersheba, sai Abimelek da Fikol, komandan rundunoninsa suka koma ƙasar Filistiyawa.
They made a covenant at Beersheba, and then Abimelech and Phicol, the captain of his army, returned to the land of the Philistines.
33 Sai Ibrahim ya shuka itacen tsamiya a Beyersheba, a can kuma ya kira bisa sunan Ubangiji, Allah Madawwami.
Abraham planted a tamarisk tree in Beersheba. There he worshiped Yahweh, the eternal God.
34 Ibrahim kuwa ya zauna a ƙasar Filistiyawa na dogon lokaci.
Abraham remained as a foreigner in the land of the Philistines many days.

< Farawa 21 >