< Farawa 21 >

1 Ana nan sai Ubangiji ya nuna wa Saratu alheri kamar yadda ya ce, Ubangiji kuma ya yi wa Saratu abin da ya yi alkawari.
The lorde visyted Sara as he had sayde and dyd vnto her acordynge as he had spoken.
2 Saratu ta yi ciki, ta kuma haifa wa Ibrahim ɗa a tsufansa; a daidai lokacin da Allah ya yi masa alkawari.
And Sara was with childe and bare Abraha a sonne in his olde age euen the same season which the LORde had appoynted.
3 Ibrahim ya sa wa ɗan da Saratu ta haifa masa suna Ishaku.
And Abraham called his sonnes name that was borne vnto him which Sara bare him Isaac:
4 Sa’ad da ɗansa Ishaku ya kai kwana takwas da haihuwa, sai Ibrahim ya yi masa kaciya, kamar yadda Allah ya umarce shi.
and Abra circucysed Isaac his sone whe he was. viij. dayes olde as God commaunded him
5 Ibrahim yana da shekara ɗari, sa’ad da aka haifa masa ɗansa Ishaku.
And Abraha was an hundred yere olde when his sonne Isaac was borne vnto him.
6 Saratu ta ce, “Allah ya sa na yi dariya, kuma duk wanda ya ji game da wannan, zai yi dariya tare da ni.”
And Sara sayde: God hath made me a laughinge stocke: for all yt heare will laugh at me
7 Ta kuma ƙara da cewa, “Dā, wa zai iya ce wa Ibrahim, Saratu za tă yi renon yara? Duk da haka na haifar masa ɗa cikin tsufansa.”
She sayde also: who wolde haue sayde vnto Abraham that Sara shulde haue geuen childern sucke or yt I shulde haue borne him a sonne in his olde age:
8 Yaron ya yi girma, aka kuma yaye shi, a ranar da aka yaye shi kuwa, Ibrahim ya yi babban biki.
The childe grewe and was wened and Abraham made a great feast the same daye that Isaac was wened.
9 Amma Saratu ta ga cewa yaron da Hagar, mutuniyar Masar ta haifa wa Ibrahim yana wa ɗanta Ishaku gori,
Sara sawe the sonne of Hagar the Egiptian which she had borne vnto Abraham a mockynge.
10 sai ta ce wa Ibrahim, “Ka kori baiwan nan tare da ɗanta, saboda ɗan baiwan nan ba zai taɓa raba gādo da ɗana Ishaku ba.”
Then she sayde vnto Abraham: put awaye this bondemayde and hyr sonne: for the sonne of this bondwoman shall not be heyre with my sonne Isaac:
11 Al’amarin ya ɓata wa Ibrahim rai sosai domin zancen ya shafi ɗansa.
But the wordes semed verey greavous in Abrahams syghte because of his sonne.
12 Amma Allah ya ce wa Ibrahim, “Kada hankalinka yă tashi game da yaron nan da kuma baiwarka. Ka saurari duk abin da Saratu ta faɗa maka, saboda ta wurin Ishaku ne za a lissafta zuriyarka.
Than the LORde sayde vnto Abraham: let it not be greavous vnto the because of the ladd and of thy bondmayde: But in all that Sara hath saide vnto the heare hir voyce for in Isaac shall thy seed be called.
13 Zan ba ɗan baiwan nan al’umma shi ma, domin shi zuriyarka ne.”
Moreouer of the sonne of the Bondwoman will I make a nation because he is thy seed.
14 Kashegari da sassafe sai Ibrahim ya ɗauki abinci da salkar ruwa, ya ba wa Hagar. Ya ɗora su a kafaɗunta, sa’an nan ya sallame ta da yaron. Ta kama hanyarta ta kuma yi ta yawo a cikin jejin Beyersheba.
And Abraham rose vp early in the mornyng and toke brede and a bottell with water and gaue it vnto Hagar puttynge it on hir shulders wyth the lad also and sent her awaye. And she departed and wadred vpp and doune in the wyldernes of Berseba.
15 Sa’ad da ruwan da yake cikin salkan ya ƙare, sai ta ajiye yaron a ƙarƙashin wani ƙaramin itace.
When the water was spent that was in the botell she cast the lad vnder a bush
16 Sai ta tafi, ta zauna ɗan nesa da yaron, misalin nisan harbin baka, gama ta yi tunani ta ce, “Ba zan iya kallon yaron yana mutuwa ba.” Da ta zauna nesa da yaron, sai ta fara kuka.
and went and satt her out of syghte a great waye as it were a bowshote off: For she sayde: I will not se the lad dye. And she satt doune out of syghte and lyfte vp hyr voyce and wepte.
17 Allah kuwa ya ji yaron yana kuka, sai mala’ikan Allah ya kira Hagar daga sama ya ce mata, “Mene ne damuwarki, Hagar? Kada ki ji tsoro, Allah ya ji yaron yana kuka yayinda yake kwance a can.
And God herde the voyce of the childe. And the angell of God called Hagar out of heaven and sayde vnto her: What ayleth the Hagar? Feare not for God hath herde the voyce of the childe where he lyeth.
18 Ki ɗaga yaron ki riƙe shi a hannu, gama zan mai da shi al’umma mai girma.”
Aryse and lyfte vp the lad and take hym in thy hande for I will make off him a greate people.
19 Sa’an nan Allah ya buɗe idanunta ta ga wata rijiyar ruwa. Don haka sai ta tafi ta cika salkan da ruwa, ta kuma ba wa yaron ruwa ya sha.
And God opened hir eyes and she sawe a well of water. And she went and fylled the bottell with water and gaue the boye drynke.
20 Allah ya kasance da yaron, yayinda yake girma. Ya yi zama a jeji, ya kuma zama maharbi.
And God was wyth the lad and he grewe and dweld in the wildernesse and became an archer.
21 Yayinda yake zama a Jejin Faran, sai mahaifiyarsa ta samo masa mata daga Masar.
And he dweld in the wyldernesse of Pharan. And hys mother gott him a wyfe out of the land of Egypte.
22 A lokacin nan Abimelek da Fikol, komandan rundunoninsa suka zo suka ce wa Ibrahim, “Allah yana tare da kai a ko mene ne kake yi.
And it chaunced the same season that Abimelech and Phicoll his chefe captayne spake vnto Abraham saynge: God is wyth the in all that thou doist.
23 Yanzu ka rantse mini a nan a gaban Allah cewa, ba za ka yaudare ni ko’ya’yana ko kuma zuriyata ba. Ka nuna mini alheri, kai da ƙasar da kake zama baƙunci kamar yadda na nuna maka.”
Now therfore swere vnto me even here by God that thou wylt not hurt me nor my childern nor my childerns childern. But that thou shalt deale with me and the contre where thou art a straunger acordynge vnto the kyndnesse that I haue shewed the.
24 Ibrahim ya ce, “Na rantse.”
Then sayde Abraham: I wyll swere.
25 Sa’an nan Ibrahim ya kawo kuka ga Abimelek game da rijiyar ruwan da bayin Abimelek suka ƙwace.
And Abraham rebuked Abimelech for a well of water which Abimelech servauntes had taken awaye.
26 Sai Abimelek ya ce, “Ban san wanda ya yi wannan ba. Ba ka faɗa mini ba, ban kuwa taɓa ji ba, sai yau.”
And Abimelech answered I wyst not who dyd it: Also thou toldest me not nether herde I of it but this daye.
27 Sai Ibrahim ya kawo tumaki da shanu ya ba wa Abimelek, sai su biyun suka yi yarjejjeniya.
And Abraham toke shepe and oxen and gaue them vnto Abimelech. And they made both of them a bonde together.
28 Ibrahim ya ware’yan raguna bakwai daga cikin garke,
And Abraham sett vij. lambes by them selues.
29 sai Abimelek ya ce wa Ibrahim, “Mene ne ma’anar’yan raguna bakwai da ka keɓe?”
And Abimelech sayde vnto Abraham: what meane these. vij. lamdes which thou hast sett by them selues.
30 Ibrahim ya amsa ya ce, “Ka karɓi waɗannan’yan tumaki bakwai daga hannuna a matsayin shaida cewa ni ne na haƙa wannan rijiya.”
And he answered: vij. lambes shalt thou take of my hande that it maye be a wytnesse vnto me that I haue dygged this well:
31 Saboda haka aka kira wurin Beyersheba, domin a nan ne su biyun suka yi rantsuwa.
Wherfore the place is called Berseba because they sware both of them.
32 Bayan da aka yi yarjejjeniya a Beyersheba, sai Abimelek da Fikol, komandan rundunoninsa suka koma ƙasar Filistiyawa.
Thus made they a bonde to gether at Berseba. Than Abimelech and Phicoll his chefe captayne rose vp and turned agayne vnto the lande of the Philistines.
33 Sai Ibrahim ya shuka itacen tsamiya a Beyersheba, a can kuma ya kira bisa sunan Ubangiji, Allah Madawwami.
And Abraham planted a wodd in Berseba and called there on the name of the LORde the everlastynge God:
34 Ibrahim kuwa ya zauna a ƙasar Filistiyawa na dogon lokaci.
and dwelt in the Phelistinlade alonge season

< Farawa 21 >