< Farawa 21 >
1 Ana nan sai Ubangiji ya nuna wa Saratu alheri kamar yadda ya ce, Ubangiji kuma ya yi wa Saratu abin da ya yi alkawari.
And Jehovah visited Sarah as he had said, and Jehovah did to Sarah as he had spoken.
2 Saratu ta yi ciki, ta kuma haifa wa Ibrahim ɗa a tsufansa; a daidai lokacin da Allah ya yi masa alkawari.
And Sarah conceived, and bore Abraham a son in his old age, at the set time of which God had spoken to him.
3 Ibrahim ya sa wa ɗan da Saratu ta haifa masa suna Ishaku.
And Abraham called the name of his son who was born to him, whom Sarah bore to him, Isaac.
4 Sa’ad da ɗansa Ishaku ya kai kwana takwas da haihuwa, sai Ibrahim ya yi masa kaciya, kamar yadda Allah ya umarce shi.
And Abraham circumcised his son Isaac when he was eight days old, as God had commanded him.
5 Ibrahim yana da shekara ɗari, sa’ad da aka haifa masa ɗansa Ishaku.
And Abraham was a hundred years old, when his son Isaac was born to him.
6 Saratu ta ce, “Allah ya sa na yi dariya, kuma duk wanda ya ji game da wannan, zai yi dariya tare da ni.”
And Sarah said, God has made me to laugh. Everyone who hears will laugh with me.
7 Ta kuma ƙara da cewa, “Dā, wa zai iya ce wa Ibrahim, Saratu za tă yi renon yara? Duk da haka na haifar masa ɗa cikin tsufansa.”
And she said, Who would have said to Abraham, that Sarah should give sons suck? For I have borne him a son in his old age.
8 Yaron ya yi girma, aka kuma yaye shi, a ranar da aka yaye shi kuwa, Ibrahim ya yi babban biki.
And the child grew, and was weaned. And Abraham made a great feast on the day that Isaac was weaned.
9 Amma Saratu ta ga cewa yaron da Hagar, mutuniyar Masar ta haifa wa Ibrahim yana wa ɗanta Ishaku gori,
And Sarah saw the son of Hagar the Egyptian, whom she had borne to Abraham, mocking.
10 sai ta ce wa Ibrahim, “Ka kori baiwan nan tare da ɗanta, saboda ɗan baiwan nan ba zai taɓa raba gādo da ɗana Ishaku ba.”
Therefore she said to Abraham, Cast out this handmaid and her son. For the son of this handmaid shall not be heir with my son, even with Isaac.
11 Al’amarin ya ɓata wa Ibrahim rai sosai domin zancen ya shafi ɗansa.
And the thing was very grievous in Abraham's sight on account of his son.
12 Amma Allah ya ce wa Ibrahim, “Kada hankalinka yă tashi game da yaron nan da kuma baiwarka. Ka saurari duk abin da Saratu ta faɗa maka, saboda ta wurin Ishaku ne za a lissafta zuriyarka.
And God said to Abraham, Let it not be grievous in thy sight because of the lad, and because of thy handmaid. In all that Sarah says to thee, hearken to her voice. For in Isaac shall thy seed be called.
13 Zan ba ɗan baiwan nan al’umma shi ma, domin shi zuriyarka ne.”
And also I will make a nation of the son of the handmaid, because he is thy seed.
14 Kashegari da sassafe sai Ibrahim ya ɗauki abinci da salkar ruwa, ya ba wa Hagar. Ya ɗora su a kafaɗunta, sa’an nan ya sallame ta da yaron. Ta kama hanyarta ta kuma yi ta yawo a cikin jejin Beyersheba.
And Abraham rose up early in the morning, and took bread and a bottle of water, and gave it to Hagar, putting it on her shoulder, and the child, and sent her away. And she departed, and wandered in the wilderness of Beersheba.
15 Sa’ad da ruwan da yake cikin salkan ya ƙare, sai ta ajiye yaron a ƙarƙashin wani ƙaramin itace.
And the water in the bottle was spent, and she cast the child under one of the shrubs.
16 Sai ta tafi, ta zauna ɗan nesa da yaron, misalin nisan harbin baka, gama ta yi tunani ta ce, “Ba zan iya kallon yaron yana mutuwa ba.” Da ta zauna nesa da yaron, sai ta fara kuka.
And she went, and sat herself down opposite him a good way off, as it were a bowshot. For she said, Let me not look upon the death of the child. And she sat opposite him, and lifted up her voice, and wept.
17 Allah kuwa ya ji yaron yana kuka, sai mala’ikan Allah ya kira Hagar daga sama ya ce mata, “Mene ne damuwarki, Hagar? Kada ki ji tsoro, Allah ya ji yaron yana kuka yayinda yake kwance a can.
And God heard the voice of the lad. And the agent of God called to Hagar out of heaven, and said to her, What troubles thee, Hagar? Fear not, for God has heard the voice of the lad where he is.
18 Ki ɗaga yaron ki riƙe shi a hannu, gama zan mai da shi al’umma mai girma.”
Arise, lift up the lad, and hold him in thy hand, for I will make him a great nation.
19 Sa’an nan Allah ya buɗe idanunta ta ga wata rijiyar ruwa. Don haka sai ta tafi ta cika salkan da ruwa, ta kuma ba wa yaron ruwa ya sha.
And God opened her eyes, and she saw a well of water. And she went, and filled the bottle with water, and gave the lad drink.
20 Allah ya kasance da yaron, yayinda yake girma. Ya yi zama a jeji, ya kuma zama maharbi.
And God was with the lad, and he grew. And he dwelt in the wilderness, and became, as he grew up, an archer.
21 Yayinda yake zama a Jejin Faran, sai mahaifiyarsa ta samo masa mata daga Masar.
And he dwelt in the wilderness of Paran. And his mother took for him a wife out of the land of Egypt.
22 A lokacin nan Abimelek da Fikol, komandan rundunoninsa suka zo suka ce wa Ibrahim, “Allah yana tare da kai a ko mene ne kake yi.
And it came to pass at that time, that Abimelech and Phicol the captain of his army spoke to Abraham, saying, God is with thee in all that thou do.
23 Yanzu ka rantse mini a nan a gaban Allah cewa, ba za ka yaudare ni ko’ya’yana ko kuma zuriyata ba. Ka nuna mini alheri, kai da ƙasar da kake zama baƙunci kamar yadda na nuna maka.”
Now therefore swear to me here by God that thou will not deal falsely with me, nor with my son, nor with my son's son. But according to the kindness that I have done to thee, thou shall do to me, and to the land in which thou have sojourned.
24 Ibrahim ya ce, “Na rantse.”
And Abraham said, I will swear.
25 Sa’an nan Ibrahim ya kawo kuka ga Abimelek game da rijiyar ruwan da bayin Abimelek suka ƙwace.
And Abraham reproved Abimelech because of the well of water which Abimelech's servants had taken away violently.
26 Sai Abimelek ya ce, “Ban san wanda ya yi wannan ba. Ba ka faɗa mini ba, ban kuwa taɓa ji ba, sai yau.”
And Abimelech said, I know not who has done this thing, neither did thou tell me, nor yet did I hear of it, but today.
27 Sai Ibrahim ya kawo tumaki da shanu ya ba wa Abimelek, sai su biyun suka yi yarjejjeniya.
And Abraham took sheep and oxen, and gave them to Abimelech. And the two made a covenant.
28 Ibrahim ya ware’yan raguna bakwai daga cikin garke,
And Abraham set seven ewe lambs of the flock by themselves.
29 sai Abimelek ya ce wa Ibrahim, “Mene ne ma’anar’yan raguna bakwai da ka keɓe?”
And Abimelech said to Abraham, What do these seven ewe lambs mean which thou have set by themselves?
30 Ibrahim ya amsa ya ce, “Ka karɓi waɗannan’yan tumaki bakwai daga hannuna a matsayin shaida cewa ni ne na haƙa wannan rijiya.”
And he said, These seven ewe lambs thou shall take from my hand, that it may be a witness to me, that I have dug this well.
31 Saboda haka aka kira wurin Beyersheba, domin a nan ne su biyun suka yi rantsuwa.
Therefore he called that place Beersheba, because there they swore both of them.
32 Bayan da aka yi yarjejjeniya a Beyersheba, sai Abimelek da Fikol, komandan rundunoninsa suka koma ƙasar Filistiyawa.
So they made a covenant at Beersheba. And Abimelech rose up, and Phicol the captain of his army, and they returned into the land of the Philistines.
33 Sai Ibrahim ya shuka itacen tsamiya a Beyersheba, a can kuma ya kira bisa sunan Ubangiji, Allah Madawwami.
And Abraham planted a tamarisk tree in Beersheba, and there called on the name of Jehovah, the Everlasting God.
34 Ibrahim kuwa ya zauna a ƙasar Filistiyawa na dogon lokaci.
And Abraham sojourned in the land of the Philistines many days.