< Farawa 21 >
1 Ana nan sai Ubangiji ya nuna wa Saratu alheri kamar yadda ya ce, Ubangiji kuma ya yi wa Saratu abin da ya yi alkawari.
Koro Jehova Nyasaye notimo ngʼwono ne Sara kaka nosewacho kendo Jehova Nyasaye nochopo kare singruok mane osenyiso Sara.
2 Saratu ta yi ciki, ta kuma haifa wa Ibrahim ɗa a tsufansa; a daidai lokacin da Allah ya yi masa alkawari.
Sara nomako ich kendo nonywolone Ibrahim wuowi ka Ibrahim hike oniangʼ, mana e kinde mane Nyasaye osingore.
3 Ibrahim ya sa wa ɗan da Saratu ta haifa masa suna Ishaku.
Ibrahim nochako wuowi mane Sara onywolone ni Isaka.
4 Sa’ad da ɗansa Ishaku ya kai kwana takwas da haihuwa, sai Ibrahim ya yi masa kaciya, kamar yadda Allah ya umarce shi.
Kane wuode Isaka nigi ndalo aboro, Ibrahim notere nyangu kaka Nyasaye nochike.
5 Ibrahim yana da shekara ɗari, sa’ad da aka haifa masa ɗansa Ishaku.
Ibrahim ne ja-higni mia achiel kane onywol Isaka wuode.
6 Saratu ta ce, “Allah ya sa na yi dariya, kuma duk wanda ya ji game da wannan, zai yi dariya tare da ni.”
Sara nowacho niya, “Nyasaye osekelona mor kendo ji duto mowinjo ma biro bedo mamor koda.”
7 Ta kuma ƙara da cewa, “Dā, wa zai iya ce wa Ibrahim, Saratu za tă yi renon yara? Duk da haka na haifar masa ɗa cikin tsufansa.”
Kendo nomedo wacho niya, “Ngʼama dine nyis Ibrahim ni Sara didhodh nyathi? To koro asenywolone wuowi ka en ngʼama oti.”
8 Yaron ya yi girma, aka kuma yaye shi, a ranar da aka yaye shi kuwa, Ibrahim ya yi babban biki.
Nyathino nodongo kendo nowe dhoth, kendo chiengʼ mane Isaka oweyoe dhoth Ibrahim notimo nyasi maduongʼ.
9 Amma Saratu ta ga cewa yaron da Hagar, mutuniyar Masar ta haifa wa Ibrahim yana wa ɗanta Ishaku gori,
Chiengʼ moro Sara noneno ka Ishmael mane Hagar nyar Misri onywolo ne Ibrahim ka jotugo gi Isaka kendo jare.
10 sai ta ce wa Ibrahim, “Ka kori baiwan nan tare da ɗanta, saboda ɗan baiwan nan ba zai taɓa raba gādo da ɗana Ishaku ba.”
Omiyo Sara nowacho ne Ibrahim niya, “Riemb dhako ma misumbani kod wuode, nimar wuod dhako ma misumbani ok nobed jacham girkeni kaachiel gi wuoda Isaka.”
11 Al’amarin ya ɓata wa Ibrahim rai sosai domin zancen ya shafi ɗansa.
Gino nochwanyo Ibrahim ahinya nikech wachno neni kuom wuode.
12 Amma Allah ya ce wa Ibrahim, “Kada hankalinka yă tashi game da yaron nan da kuma baiwarka. Ka saurari duk abin da Saratu ta faɗa maka, saboda ta wurin Ishaku ne za a lissafta zuriyarka.
To Nyasaye nowacho ne Ibrahim niya, “Kik chunyi bed gi chwanyruok nikech wuodi Ishmael kod jatichni madhako, Hagar. Winj gimoro amora ma Sara jaodi wachoni; nikech kuom wuodi Isaka ema kothi duto nowuogie.
13 Zan ba ɗan baiwan nan al’umma shi ma, domin shi zuriyarka ne.”
Abiro miyo wuod jatichni madhako bed oganda maduongʼ nikech en bende en rembi.”
14 Kashegari da sassafe sai Ibrahim ya ɗauki abinci da salkar ruwa, ya ba wa Hagar. Ya ɗora su a kafaɗunta, sa’an nan ya sallame ta da yaron. Ta kama hanyarta ta kuma yi ta yawo a cikin jejin Beyersheba.
Kinyne gokinyi mangʼich Ibrahim nokawo chiemo kod puga mar pi kendo nomiyo Hagar. Noketonegi e goke kendo ogole odhi gi wuode. Hagar nowuok modhi kendo nobayo abaya e thim mar Bersheba.
15 Sa’ad da ruwan da yake cikin salkan ya ƙare, sai ta ajiye yaron a ƙarƙashin wani ƙaramin itace.
Ka pi mane ni e puga norumo, noketo nyathi e tiend bungu.
16 Sai ta tafi, ta zauna ɗan nesa da yaron, misalin nisan harbin baka, gama ta yi tunani ta ce, “Ba zan iya kallon yaron yana mutuwa ba.” Da ta zauna nesa da yaron, sai ta fara kuka.
Eka nowuotho odhi nyime kama dirom fut adek kendo nobedo piny kanyo, mi nowacho e chunye niya, “Ok anyal rango nyathi katho.” Kendo kane obet machiegni kanyo, nyathi nochako ywak.
17 Allah kuwa ya ji yaron yana kuka, sai mala’ikan Allah ya kira Hagar daga sama ya ce mata, “Mene ne damuwarki, Hagar? Kada ki ji tsoro, Allah ya ji yaron yana kuka yayinda yake kwance a can.
Nyasaye nowinjo nyathi kaywak kendo malaika mar Nyasaye noluongo Hagar gie polo kendo owachone niya, “Angʼo marach, Hagar? Kik iluor; Nyasaye osewinjo nyathi kaywak kama onindeno.
18 Ki ɗaga yaron ki riƙe shi a hannu, gama zan mai da shi al’umma mai girma.”
Kaw nyathi kendo itingʼe, nikech anami nyikwaye obed oganda maduongʼ.”
19 Sa’an nan Allah ya buɗe idanunta ta ga wata rijiyar ruwa. Don haka sai ta tafi ta cika salkan da ruwa, ta kuma ba wa yaron ruwa ya sha.
Eka Nyasaye noyawo wengene kendo oneno soko mar pi. Kuom mano nodhi mopongʼo puga gi pi kendo nomiyo nyathi omodho.
20 Allah ya kasance da yaron, yayinda yake girma. Ya yi zama a jeji, ya kuma zama maharbi.
Nyasaye ne ni kod wuowino kane odongo kendo nodak e thim mobedo jadwar molony.
21 Yayinda yake zama a Jejin Faran, sai mahaifiyarsa ta samo masa mata daga Masar.
Kane odak e thim mar Paran, min mare noyudone nyako mokendo koa e piny Misri.
22 A lokacin nan Abimelek da Fikol, komandan rundunoninsa suka zo suka ce wa Ibrahim, “Allah yana tare da kai a ko mene ne kake yi.
E kindeno Abimelek kod Fikol jatend jolweny mar Abimelek nowacho ne Ibrahim niya, “Nyasaye ni kodi e gimoro amora mitimo.
23 Yanzu ka rantse mini a nan a gaban Allah cewa, ba za ka yaudare ni ko’ya’yana ko kuma zuriyata ba. Ka nuna mini alheri, kai da ƙasar da kake zama baƙunci kamar yadda na nuna maka.”
Koro kwongʼrina e nyim Nyasaye kawuono ni ok nitimna gimoro marach kata ne nyithinda kata ne nyikwaya. Emomiyo koro timna ngʼwono kaachiel gi pinyni ma intie kaka jadak mana kaka an bende ne atimoni maber.”
24 Ibrahim ya ce, “Na rantse.”
Ibrahim nodwoke niya, “Asingora ni anatim kamano.”
25 Sa’an nan Ibrahim ya kawo kuka ga Abimelek game da rijiyar ruwan da bayin Abimelek suka ƙwace.
Ibrahim nonyiso Abimelek chandruok mar soko mar pi ma jotich Abimelek nomaye githuon.
26 Sai Abimelek ya ce, “Ban san wanda ya yi wannan ba. Ba ka faɗa mini ba, ban kuwa taɓa ji ba, sai yau.”
To Abimelek nowacho niya, “Ok angʼeyo ngʼama osetimo mae. Ne ok inyisa, ma kawuono ema akwongo winje.”
27 Sai Ibrahim ya kawo tumaki da shanu ya ba wa Abimelek, sai su biyun suka yi yarjejjeniya.
Kuom mano Ibrahim nokelo rombe kod dhok mi omiyogi Abimelek, kendo ji ariyogi notimo singruok.
28 Ibrahim ya ware’yan raguna bakwai daga cikin garke,
Ibrahim nowalo rombe ma sibini abiriyo mag kwethge,
29 sai Abimelek ya ce wa Ibrahim, “Mene ne ma’anar’yan raguna bakwai da ka keɓe?”
kendo Abimelek nopenjo Ibrahim niya, “Ere tiend rombe ma sibini abiriyo ma isewalogi?”
30 Ibrahim ya amsa ya ce, “Ka karɓi waɗannan’yan tumaki bakwai daga hannuna a matsayin shaida cewa ni ne na haƙa wannan rijiya.”
Ibrahim nodwoke niya, “Kaw nyirombe abiriyogi kaka ranyisi ni nakunyo sokoni.”
31 Saboda haka aka kira wurin Beyersheba, domin a nan ne su biyun suka yi rantsuwa.
Mano emomiyo kanyo iluongo ni Bersheba nikech ji ariyogo notimo singruok kanyo.
32 Bayan da aka yi yarjejjeniya a Beyersheba, sai Abimelek da Fikol, komandan rundunoninsa suka koma ƙasar Filistiyawa.
Bangʼ ka winjruok nosetim Bersheba, Abimelek kod Fikol ma jatend jolwenje nodok e piny jo-Filistia.
33 Sai Ibrahim ya shuka itacen tsamiya a Beyersheba, a can kuma ya kira bisa sunan Ubangiji, Allah Madawwami.
Ibrahim nopidho yien moro Bersheba, kendo kanyo noluongo nying Jehova Nyasaye, Nyasaye manyaka chiengʼ.
34 Ibrahim kuwa ya zauna a ƙasar Filistiyawa na dogon lokaci.
Kendo Ibrahim nodak e piny jo-Filistia kuom kinde mangʼeny.