< Farawa 20 >

1 Daga Mamre, Ibrahim ya kama hanya ya nufi wajajen Negeb, ya zauna a tsakanin Kadesh da Shur. Ya zauna a Gerar na ɗan lokaci,
Parti de là pour la terre australe, Abraham habita entre Cadès et Sur, et demeura comme étranger à Gérara.
2 a can ne Ibrahim ya ce game da matarsa Saratu, “Ita’yar’uwata ce.” Sai Abimelek sarkin Gerar ya aiko a kawo masa Saratu.
Or il dit de Sara sa femme: C’est ma sœur. Abimélech, roi de Gérara, envoya donc vers lui et la fit enlever.
3 Amma wata rana da dad dare Allah ya zo wa Abimelek a cikin mafarki ya ce masa, “Kai da matacce ɗaya kuke, saboda matar da ka ɗauka. Ita matar aure ce.”
Mais Dieu vint vers Abimélech dans un songe pendant la nuit, et lui dit: Voilà que tu mourras, à cause de la femme que tu as enlevée; car elle a un mari.
4 Abimelek dai bai riga ya kusace ta ba tukuna, saboda haka ya ce, “Ya Ubangiji za ka hallaka al’umma marar laifi?
Or Abimélech ne l’avait pas touchée, et il dit: Seigneur, perdrez-vous une nation qui est dans l’ignorance, et innocente?
5 Ba shi ne ya ce mini, ‘Ita’yar’uwata ba ce,’ ita ma ba tă ce, ‘Shi ɗan’uwana ba ne’? Na yi haka da kyakkyawan nufi da hannuwa masu tsabta.”
Lui-même ne m’a-t-il pas dit: C’est ma sœur? Et elle-même n’a-t-elle pas dit: C’est mon frère? C’est dans la simplicité de mon cœur et dans la pureté de mes mains que je l’ai fait.
6 Sai Allah ya ce masa a cikin mafarki “I, na san ka yi wannan da kyakkyawan nufi, saboda haka ne na kiyaye ka daga yin mini zunubi. Shi ya sa ban bar ka ka taɓa ta ba.
Et Dieu lui dit: Et moi aussi je sais que c’est avec un cœur simple que tu l’as fait; et c’est pour cela que je t’ai gardé, afin que tu ne péchasses pas contre moi, et que je n’ai pas permis que tu la touchasses.
7 Yanzu ka komar da matar mutumin, gama shi annabi ne, zai kuma yi maka addu’a, za ka kuwa rayu. In ba ka komar da ita ba fa, ka sani tabbatacce kai da dukan abin da yake naka za ku mutu.”
Maintenant donc rends à son mari cette femme; parce que c’est un prophète, et il priera pour toi, et tu vivras; mais si tu ne la rends pas, sache que tu mourras de mort, toi et tout ce qui est à toi.
8 Kashegari da sassafe, sai Abimelek ya tara dukan fadawansa, ya faɗa musu duk abin da ya faru, suka ji tsoro ƙwarai da gaske.
Aussitôt, se levant de nuit, Abimélech appela tous ses serviteurs, et fit entendre toutes ces paroles à leurs oreilles; et tous ces hommes furent saisis d une grande crainte.
9 Sa’an nan Abimelek ya kira Ibrahim ciki ya ce, “Me ke nan ka yi mana? Ta wace hanya ce na yi maka laifi har da ka kawo irin wannan babban laifi a kaina da kuma masarautata? Ka yi mini abubuwan da bai kamata a yi ba.”
Puis Abimélech appela aussi Abraham et lui dit: Que nous as-tu fait? et en quoi t’avons-nous offensé, pour que tu aies attiré sur moi et sur mon royaume un si grand péché? ce que tu ne devais pas faire, tu nous l’as fait.
10 Abimelek ya kuma ce wa Ibrahim, “Me ya sa ka yi wannan?”
Et de nouveau se plaignant, il dit: Qu’as-tu vu, pour agir ainsi?
11 Ibrahim ya ce, “Na ce a raina, ‘Tabbatacce babu tsoron Allah a wannan wuri, za su kuwa kashe ni saboda matata.’
Abraham répondit: J’ai pensé en moi-même, disant: Peut-être n’y a-t-il point la crainte de Dieu en ce lieu-ci, et ils me feront mourir à cause de ma femme.
12 Ban da haka, tabbatacce ita’yar’uwata ce,’yar mahaifina, ko da yake ba daga uwata ba, ta kuma zama matata.
D’ailleurs elle est vraiment aussi ma sœur, étant fille de mon père, quoiqu’elle ne soit pas fille de ma mère; et je l’ai prise pour femme.
13 Sa’ad da Allah ya sa na tashi daga gidan mahaifina na ce mata, ‘Wannan shi ne yadda za ki nuna mini ƙaunarki. Duk inda muka tafi, ki ce game da ni, “Shi ɗan’uwana ne.”’”
Or quand Dieu me fit sortir de la maison de mon père, je dis à Sara: Tu me feras cette grâce: dans tous les lieux où nous irons, tu diras que je suis ton frère.
14 Sai Abimelek ya kawo awaki da shanu da bayi maza da mata, ya ba wa Ibrahim, ya kuma komar da Saratu matarsa gare shi.
Abimélech prit donc des brebis, des bœufs, des serviteurs et des servantes, et il les donna à Abraham; et il lui rendit Sara sa femme.
15 Abimelek ya kuma ce, “Ƙasata tana gabanka, ka zauna a duk inda kake so.”
Et il dit: La terre est devant vous; partout où il te plaira, habites-y.
16 Ga Saratu kuwa ya ce, “Ina ba wa ɗan’uwanki shekel dubu na azurfa, shaida ce ta tabbatarwa a idanun dukan waɗanda suke tare da ke, da kuma a gaban kowa cewa ba ki da laifi.”
Mais à Sara il dit: Voilà que j’ai donné à ton frère mille pièces d’argent, pour que tu aies un voile sur les yeux devant tous ceux qui seront avec toi, et en quelque lieu que tu ailles: et souviens-toi que tu as été enlevée.
17 Sai Ibrahim ya yi addu’a ga Allah, Allah kuma ya warkar da Abimelek, da matarsa da bayinsa mata domin su haihu,
Mais Abraham ayant prié, Dieu guérit Abimélech, sa femme et ses servantes, et elles enfantèrent;
18 gama Ubangiji ya rufe kowace mahaifa a gidan Abimelek saboda Saratu, matar Ibrahim.
Car le Seigneur avait frappé de stérilité toute la maison d’Abimélech, à cause de Sara femme d’Abraham.

< Farawa 20 >