< Farawa 20 >
1 Daga Mamre, Ibrahim ya kama hanya ya nufi wajajen Negeb, ya zauna a tsakanin Kadesh da Shur. Ya zauna a Gerar na ɗan lokaci,
And he set out from there Abraham [the] land of towards the Negev and he dwelt between Kadesh and between Shur and he sojourned in Gerar.
2 a can ne Ibrahim ya ce game da matarsa Saratu, “Ita’yar’uwata ce.” Sai Abimelek sarkin Gerar ya aiko a kawo masa Saratu.
And he said Abraham concerning Sarah wife his [is] sister my she and he sent Abimelech [the] king of Gerar and he took Sarah.
3 Amma wata rana da dad dare Allah ya zo wa Abimelek a cikin mafarki ya ce masa, “Kai da matacce ɗaya kuke, saboda matar da ka ɗauka. Ita matar aure ce.”
And he came God to Abimelech in a dream the night and he said to him here you [are] about to die on the woman whom you have taken and she [is] married of a husband.
4 Abimelek dai bai riga ya kusace ta ba tukuna, saboda haka ya ce, “Ya Ubangiji za ka hallaka al’umma marar laifi?
And Abimelech not he had drawn near to her and he said O Lord ¿ a nation also righteous will you kill.
5 Ba shi ne ya ce mini, ‘Ita’yar’uwata ba ce,’ ita ma ba tă ce, ‘Shi ɗan’uwana ba ne’? Na yi haka da kyakkyawan nufi da hannuwa masu tsabta.”
¿ Not he did he say to me [is] sister my she and she also she she said [is] brother my he in [the] integrity of heart my and in [the] innocence of hands my I have done this.
6 Sai Allah ya ce masa a cikin mafarki “I, na san ka yi wannan da kyakkyawan nufi, saboda haka ne na kiyaye ka daga yin mini zunubi. Shi ya sa ban bar ka ka taɓa ta ba.
And he said to him God in a dream also I I know that in [the] integrity of heart your you did this and I have restrained also I you from sinning to me there-fore not I have permitted you to touch her.
7 Yanzu ka komar da matar mutumin, gama shi annabi ne, zai kuma yi maka addu’a, za ka kuwa rayu. In ba ka komar da ita ba fa, ka sani tabbatacce kai da dukan abin da yake naka za ku mutu.”
And therefore return [the] wife of the man for [is] a prophet he so he may pray for you and live and if not [are] you returning [her] know that certainly you will die you and all who [belong] to you.
8 Kashegari da sassafe, sai Abimelek ya tara dukan fadawansa, ya faɗa musu duk abin da ya faru, suka ji tsoro ƙwarai da gaske.
And he rose early Abimelech in the morning and he summoned all servants his and he spoke all the words these in ears their and they were afraid the men exceedingly.
9 Sa’an nan Abimelek ya kira Ibrahim ciki ya ce, “Me ke nan ka yi mana? Ta wace hanya ce na yi maka laifi har da ka kawo irin wannan babban laifi a kaina da kuma masarautata? Ka yi mini abubuwan da bai kamata a yi ba.”
And he summoned Abimelech Abraham and he said to him what? have you done to us and what? have I sinned to you for you have brought on me and on kingdom my a sin great deeds which not they will be done you have done with me.
10 Abimelek ya kuma ce wa Ibrahim, “Me ya sa ka yi wannan?”
And he said Abimelech to Abraham what? did you see that you have done the thing this.
11 Ibrahim ya ce, “Na ce a raina, ‘Tabbatacce babu tsoron Allah a wannan wuri, za su kuwa kashe ni saboda matata.’
And he said Abraham that I said certainly there not [is] [the] fear of God in the place this and they will kill me on [the] matter of wife my.
12 Ban da haka, tabbatacce ita’yar’uwata ce,’yar mahaifina, ko da yake ba daga uwata ba, ta kuma zama matata.
And also truly [is] sister my [the] daughter of father my she only not [the] daughter of mother my and she became of me a wife.
13 Sa’ad da Allah ya sa na tashi daga gidan mahaifina na ce mata, ‘Wannan shi ne yadda za ki nuna mini ƙaunarki. Duk inda muka tafi, ki ce game da ni, “Shi ɗan’uwana ne.”’”
And it was just as they caused to wander me God from [the] household of father my and I said to her this [is] loyalty your which you will do with me to every place where we will go there towards say of me [is] brother my he.
14 Sai Abimelek ya kawo awaki da shanu da bayi maza da mata, ya ba wa Ibrahim, ya kuma komar da Saratu matarsa gare shi.
And he took Abimelech sheep and cattle and [male] servants and female servants and he gave [them] to Abraham and he restored to him Sarah wife his.
15 Abimelek ya kuma ce, “Ƙasata tana gabanka, ka zauna a duk inda kake so.”
And he said Abimelech there! land my [is] before you in the [place] good in view your dwell.
16 Ga Saratu kuwa ya ce, “Ina ba wa ɗan’uwanki shekel dubu na azurfa, shaida ce ta tabbatarwa a idanun dukan waɗanda suke tare da ke, da kuma a gaban kowa cewa ba ki da laifi.”
And to Sarah he said here! I give a thousand silver to brother your there! it for you [is] a covering of eyes to all who [are] with you and with everyone [you are] vindicated.
17 Sai Ibrahim ya yi addu’a ga Allah, Allah kuma ya warkar da Abimelek, da matarsa da bayinsa mata domin su haihu,
And he prayed Abraham to God and he healed God Abimelech and wife his and female slaves his and they bore children.
18 gama Ubangiji ya rufe kowace mahaifa a gidan Abimelek saboda Saratu, matar Ibrahim.
For certainly had shut up Yahweh behind every womb of [the] household of Abimelech on [the] matter of Sarah [the] wife of Abraham.