< Farawa 20 >
1 Daga Mamre, Ibrahim ya kama hanya ya nufi wajajen Negeb, ya zauna a tsakanin Kadesh da Shur. Ya zauna a Gerar na ɗan lokaci,
Odande Abraham krene u krajeve Negeba i nastani se između Kadeša i Šura. Dok je boravio kao pridošlica u Geraru,
2 a can ne Ibrahim ya ce game da matarsa Saratu, “Ita’yar’uwata ce.” Sai Abimelek sarkin Gerar ya aiko a kawo masa Saratu.
rekao je Abraham za svoju ženu Saru da mu je sestra. I Abimelek, kralj gerarski, uze Saru sebi.
3 Amma wata rana da dad dare Allah ya zo wa Abimelek a cikin mafarki ya ce masa, “Kai da matacce ɗaya kuke, saboda matar da ka ɗauka. Ita matar aure ce.”
Ali Bog dođe Abimeleku noću u snu te mu reče: “Zbog žene koju si uzeo moraš umrijeti, jer je ona žena udata.”
4 Abimelek dai bai riga ya kusace ta ba tukuna, saboda haka ya ce, “Ya Ubangiji za ka hallaka al’umma marar laifi?
A nije se Abimelek k njoj približavao. Zato reče: “Gospodine, zar ćeš pravednika pogubiti?
5 Ba shi ne ya ce mini, ‘Ita’yar’uwata ba ce,’ ita ma ba tă ce, ‘Shi ɗan’uwana ba ne’? Na yi haka da kyakkyawan nufi da hannuwa masu tsabta.”
Zar mi on nije rekao: 'Ona mi je sestra.' A ona mi je sama rekla: 'On je moj brat.' Čiste sam savjesti i neokaljanih ruku ovo učinio.”
6 Sai Allah ya ce masa a cikin mafarki “I, na san ka yi wannan da kyakkyawan nufi, saboda haka ne na kiyaye ka daga yin mini zunubi. Shi ya sa ban bar ka ka taɓa ta ba.
Bog mu odvrati u snu: “Znam da si to učinio čiste savjesti; i ja sam te zadržavao da protiv mene ne griješiš; i nisam dopuštao da je dotakneš.
7 Yanzu ka komar da matar mutumin, gama shi annabi ne, zai kuma yi maka addu’a, za ka kuwa rayu. In ba ka komar da ita ba fa, ka sani tabbatacce kai da dukan abin da yake naka za ku mutu.”
Sada vrati čovjeku ženu njegovu; prorok je on; molit će se za tebe da ostaneš na životu. Ako je ne vratiš, znaj da ćeš umrijeti, ti i svi tvoji.”
8 Kashegari da sassafe, sai Abimelek ya tara dukan fadawansa, ya faɗa musu duk abin da ya faru, suka ji tsoro ƙwarai da gaske.
Rano ujutro Abimelek ustane, sazove sve svoje sluge i kaže im sve što je bilo, a ljudi se veoma uplaše.
9 Sa’an nan Abimelek ya kira Ibrahim ciki ya ce, “Me ke nan ka yi mana? Ta wace hanya ce na yi maka laifi har da ka kawo irin wannan babban laifi a kaina da kuma masarautata? Ka yi mini abubuwan da bai kamata a yi ba.”
Potom Abimelek dozva Abrahama te mu reče: “Što si nam učinio! Čime sam se ja ogriješio prema tebi da izložiš mene i moje kraljevstvo velikoj grehoti? Ponio si se prema meni kako ne valja.
10 Abimelek ya kuma ce wa Ibrahim, “Me ya sa ka yi wannan?”
Što si, dakle na umu imao”, upita dalje Abimelek, “kad si tako radio?”
11 Ibrahim ya ce, “Na ce a raina, ‘Tabbatacce babu tsoron Allah a wannan wuri, za su kuwa kashe ni saboda matata.’
Abraham uzvrati: “Zbilja sam držao da nema Božjeg straha u ovome mjestu, pa će me ljudi ubiti zbog moje žene.
12 Ban da haka, tabbatacce ita’yar’uwata ce,’yar mahaifina, ko da yake ba daga uwata ba, ta kuma zama matata.
A onda, ona je uistinu moja sestra: kći je moga oca, iako ne i moje majke, pa je pošla za me.
13 Sa’ad da Allah ya sa na tashi daga gidan mahaifina na ce mata, ‘Wannan shi ne yadda za ki nuna mini ƙaunarki. Duk inda muka tafi, ki ce game da ni, “Shi ɗan’uwana ne.”’”
A kad me Bog udaljio od doma očeva, rekoh joj: Ovu mi uslugu učini: kamo god dođemo, reci o meni da sam ti brat.”
14 Sai Abimelek ya kawo awaki da shanu da bayi maza da mata, ya ba wa Ibrahim, ya kuma komar da Saratu matarsa gare shi.
Abimelek uzme ovaca i goveda, sluga i sluškinja pa ih dade Abrahamu; vrati mu i njegovu ženu Saru.
15 Abimelek ya kuma ce, “Ƙasata tana gabanka, ka zauna a duk inda kake so.”
Abimelek zatim reče: “Evo, moja ti je zemlja otvorena. Nastani se gdje ti se svidi!”
16 Ga Saratu kuwa ya ce, “Ina ba wa ɗan’uwanki shekel dubu na azurfa, shaida ce ta tabbatarwa a idanun dukan waɗanda suke tare da ke, da kuma a gaban kowa cewa ba ki da laifi.”
A Sari reče: “Evo tisuću srebrnika što ih dajem tvome bratu: neka ti budu koprenom pred očima sviju što su s tobom. Ti si svakako opravdana.”
17 Sai Ibrahim ya yi addu’a ga Allah, Allah kuma ya warkar da Abimelek, da matarsa da bayinsa mata domin su haihu,
Abraham se pomoli Bogu, i Bog ozdravi Abimeleka, njegovu ženu i njegove sluškinje, tako te opet mogahu rađati.
18 gama Ubangiji ya rufe kowace mahaifa a gidan Abimelek saboda Saratu, matar Ibrahim.
Jer Jahve bijaše zbog Sare, Abrahamove žene, zatvorio svaku utrobu u domu Abimelekovu.