< Farawa 2 >

1 Ta haka aka gama yin sammai da duniya da dukan abubuwan da suke cikinsu.
Les cieux, la terre et toute leur étendue furent achevés.
2 Kafin kwana ta bakwai, Allah ya gama aikin da yake yi, saboda haka a kwana ta bakwai, ya huta daga dukan aikinsa.
Le septième jour, Dieu acheva l'œuvre qu'il avait faite, et il se reposa au septième jour de toute son œuvre.
3 Allah kuwa ya albarkaci kwana ta bakwai, ya kuma mai da ita mai tsarki, saboda a kanta ne ya huta daga dukan aikin halittar da ya yi.
Dieu bénit le septième jour et le sanctifia, parce qu'il se reposa en ce jour de toute l'œuvre de la création qu'il avait faite.
4 Wannan shi ne asalin tarihin sammai da duniya sa’ad da aka halicce su. Sa’ad da Ubangiji Allah ya yi duniya da sammai,
Voici l'histoire des générations des cieux et de la terre, quand ils furent créés, au jour où Yahvé Dieu fit la terre et les cieux.
5 babu tsiro a duniya kuma ganyaye ba su tsira a busasshiyar ƙasa ko ba, gama Ubangiji Allah bai aiko da ruwan sama a kan duniya ba tukuna, babu kuma wani mutumin da zai nome ƙasar,
Aucune plante des champs n'était encore sur la terre, et aucune herbe des champs n'avait encore poussé, car Yahvé Dieu n'avait pas fait pleuvoir sur la terre. Il n'y avait pas d'homme pour cultiver la terre,
6 amma dai rafuffuka suna ɓullo da ruwa daga ƙasa suna jiƙe ko’ina a fāɗin ƙasa.
mais une brume montait de la terre et arrosait toute la surface du sol.
7 Sa’an nan Ubangiji Allah ya yi mutum daga turɓayar ƙasa, ya kuma hura numfashin rai cikin hancinsa, mutumin kuwa ya zama rayayyen taliki.
Yahvé Dieu forma l'homme de la poussière de la terre, il souffla dans ses narines une haleine de vie, et l'homme devint un être vivant.
8 To, fa, Ubangiji Allah ya yi lambu a gabas, a Eden, a can kuwa ya sa mutumin da ya yi.
Yahvé Dieu planta un jardin à l'orient, en Éden, et il y mit l'homme qu'il avait formé.
9 Ubangiji Allah ya kuma sa kowane irin itace ya tsira daga ƙasa, itace mai kyan gani, mai amfani kuma don abinci. A tsakiyar lambun kuwa akwai itacen rai da kuma itacen sanin abin da yake da kyau da abin da yake mugu.
Yahvé Dieu fit pousser du sol tous les arbres agréables à la vue et bons à manger, y compris l'arbre de vie au milieu du jardin et l'arbre de la connaissance du bien et du mal.
10 Akwai wani kogi mai ba da ruwa ga lambun wanda ya gangaro daga Eden, daga nan ya rarrabu, ya zama koguna huɗu.
Un fleuve sortait d'Eden pour arroser le jardin; de là, il se divisait et devenait la source de quatre fleuves.
11 Sunan kogi na fari, Fishon. Shi ne yake malala kewaye da dukan ƙasar Hawila, inda akwai zinariya.
Le nom du premier est Pishon; il coule dans tout le pays de Havila, où il y a de l'or;
12 (Zinariyar wannan ƙasa kuwa tana da kyau, akwai kuma kayan ƙanshi da duwatsun da ake kira onis a can ma.)
et l'or de ce pays est bon. On y trouve aussi du bdellium et de la pierre d'onyx.
13 Sunan kogi na biyu, Gihon. Shi ne ya malala kewaye da ƙasar Kush.
Le nom du second fleuve est Gihon. C'est le même fleuve qui coule dans tout le pays de Cusch.
14 Sunan kogi na uku Tigris. Wannan ne ya malala ya bi ta gefen gabashin Asshur. Kogi na huɗu kuwa shi ne Yuferites.
Le nom du troisième fleuve est Hiddékel. C'est celui qui coule devant l'Assyrie. Le quatrième fleuve est l'Euphrate.
15 Ubangiji Allah ya ɗauko mutumin ya sa shi cikin Lambun Eden domin yă nome shi, yă kuma lura da shi.
Yahvé Dieu prit l'homme et le plaça dans le jardin d'Eden pour le cultiver et le garder.
16 Ubangiji Allah ya umarci mutumin ya ce, “Kana da’yanci ka ci daga kowane itace a cikin lambun,
Yahvé Dieu donna cet ordre à l'homme: « Tu peux manger librement de tous les arbres du jardin;
17 amma kada ka ci daga itacen sanin abin da yake mai kyau da abin da yake mugu, gama a ranar da ka ci shi, lalle za ka mutu.”
mais tu ne mangeras pas de l'arbre de la connaissance du bien et du mal, car le jour où tu en mangeras, tu mourras. »
18 Ubangiji Allah ya ce, “Bai yi kyau mutumin yă kasance shi kaɗai ba. Zan yi masa mataimakin da ya dace da shi.”
Yahvé Dieu dit: « Il n'est pas bon que l'homme soit seul. Je vais lui faire une aide qui lui soit comparable. »
19 To, Ubangiji Allah ya yi dukan namun jeji da dukan tsuntsayen sama daga ƙasa. Ya kawo su wurin mutumin don yă ga wanda suna zai kira su; kuma duk sunan da mutumin ya kira kowane mai rai, sunansa ke nan.
Yahvé Dieu forma de la terre tous les animaux des champs et tous les oiseaux du ciel, et il les amena à l'homme pour voir comment il les appellerait. Le nom que l'homme donna à chaque être vivant devint son nom.
20 Saboda haka mutumin ya sa wa dukan dabbobi, da tsuntsayen sama da dukan namun jeji sunaye. Amma ba a sami mataimakin da ya dace da Adamu ba.
L'homme donna des noms à tout le bétail, aux oiseaux du ciel et à tous les animaux des champs; mais il ne fut pas trouvé pour l'homme un auxiliaire comparable à lui.
21 Saboda haka Ubangiji Allah ya sa mutumin ya yi barci mai nauyi; yayinda yake barci sai ya ɗauko ɗaya daga cikin haƙarƙarin mutumin, ya kuma rufe wurin da nama.
Yahvé Dieu fit tomber l'homme dans un profond sommeil. Comme l'homme dormait, il prit une de ses côtes et referma la chair à sa place.
22 Sa’an nan Ubangiji Allah ya yi mace daga haƙarƙarin da ya ɗauko daga mutumin, ya kuwa kawo ta wurin mutumin.
Yahvé Dieu fit une femme de la côte qu'il avait prise à l'homme, et il l'amena à l'homme.
23 Sai mutumin ya ce, “Yanzu kam wannan ƙashi ne na ƙasusuwana nama kuma na namana. Za a ce da ita ‘mace,’ gama an ciro ta daga namiji.”
L'homme dit: « Voici l'os de mes os et la chair de ma chair. On l'appellera femme, parce qu'elle est sortie de l'homme ».
24 Wannan ne ya sa mutum yakan bar mahaifinsa da mahaifiyarsa, yă manne wa matarsa, su kuma zama jiki ɗaya.
C'est pourquoi l'homme quittera son père et sa mère, et s'attachera à sa femme, et ils seront une seule chair.
25 Mutumin da matarsa, dukansu biyu tsirara suke, ba su kuwa ji kunya ba.
L'homme et sa femme étaient tous deux nus, et ils n'ont pas eu honte.

< Farawa 2 >