< Farawa 2 >

1 Ta haka aka gama yin sammai da duniya da dukan abubuwan da suke cikinsu.
Thus was heave and erth fynished wyth all their apparell:
2 Kafin kwana ta bakwai, Allah ya gama aikin da yake yi, saboda haka a kwana ta bakwai, ya huta daga dukan aikinsa.
ad i ye seueth daye god ended hys worke which he had made and rested in ye seventh daye fro all his workes which he had made.
3 Allah kuwa ya albarkaci kwana ta bakwai, ya kuma mai da ita mai tsarki, saboda a kanta ne ya huta daga dukan aikin halittar da ya yi.
And God blessed ye seventh daye and sanctyfyed it for in it he rested from all his workes which he had created and made.
4 Wannan shi ne asalin tarihin sammai da duniya sa’ad da aka halicce su. Sa’ad da Ubangiji Allah ya yi duniya da sammai,
These are the generations of heaven and erth when they were created in the tyme when the LORde God created heaven and erth
5 babu tsiro a duniya kuma ganyaye ba su tsira a busasshiyar ƙasa ko ba, gama Ubangiji Allah bai aiko da ruwan sama a kan duniya ba tukuna, babu kuma wani mutumin da zai nome ƙasar,
and all the shrubbes of the felde be fore they were in the erthe. And all the herbes of the felde before they sprange: for the LORde God had yet sent no rayne vpon the erth nether was there yet any man to tylle the erth.
6 amma dai rafuffuka suna ɓullo da ruwa daga ƙasa suna jiƙe ko’ina a fāɗin ƙasa.
But there arose a myste out of the ground and watered all the face of the erth:
7 Sa’an nan Ubangiji Allah ya yi mutum daga turɓayar ƙasa, ya kuma hura numfashin rai cikin hancinsa, mutumin kuwa ya zama rayayyen taliki.
Then the LORde God shope man even of the moulde of the erth and brethed into his face the breth of lyfe. So man was made a lyvynge soule.
8 To, fa, Ubangiji Allah ya yi lambu a gabas, a Eden, a can kuwa ya sa mutumin da ya yi.
The LORde God also planted a garden in Eden from the begynnynge and there he sette man whom he had formed.
9 Ubangiji Allah ya kuma sa kowane irin itace ya tsira daga ƙasa, itace mai kyan gani, mai amfani kuma don abinci. A tsakiyar lambun kuwa akwai itacen rai da kuma itacen sanin abin da yake da kyau da abin da yake mugu.
And the LORde God made to sprynge out of the erth all maner trees bewtyfull to the syghte and pleasant to eate and the tree of lyfe in the middes of the garden: and also the tree of knowlege of good and euell.
10 Akwai wani kogi mai ba da ruwa ga lambun wanda ya gangaro daga Eden, daga nan ya rarrabu, ya zama koguna huɗu.
And there spronge a rever out of Eden to water the garden and thence devided it selfe and grewe in to foure principall waters.
11 Sunan kogi na fari, Fishon. Shi ne yake malala kewaye da dukan ƙasar Hawila, inda akwai zinariya.
The name of the one is Phison he it is that compasseth all the lande of heuila where gold groweth.
12 (Zinariyar wannan ƙasa kuwa tana da kyau, akwai kuma kayan ƙanshi da duwatsun da ake kira onis a can ma.)
And the gold of that contre ys precious there is found bedellion and a stone called Onix.
13 Sunan kogi na biyu, Gihon. Shi ne ya malala kewaye da ƙasar Kush.
The name of the seconde ryver is Gihon which compassyth all the lande of Inde.
14 Sunan kogi na uku Tigris. Wannan ne ya malala ya bi ta gefen gabashin Asshur. Kogi na huɗu kuwa shi ne Yuferites.
And the name of the thyrde river is Hidekell which runneth on the easte syde of the assyryans And the fourth river is Euphrates.
15 Ubangiji Allah ya ɗauko mutumin ya sa shi cikin Lambun Eden domin yă nome shi, yă kuma lura da shi.
And the LORde God toke Adam and put him in the garden of Eden to dresse it and to kepe it:
16 Ubangiji Allah ya umarci mutumin ya ce, “Kana da’yanci ka ci daga kowane itace a cikin lambun,
and the LORde God comaunded Ada saynge: of all the trees of the garde se thou eate.
17 amma kada ka ci daga itacen sanin abin da yake mai kyau da abin da yake mugu, gama a ranar da ka ci shi, lalle za ka mutu.”
But of the tre of knowlege of good and badd se that thou eate not: for even ye same daye thou eatest of it thou shalt surely dye.
18 Ubangiji Allah ya ce, “Bai yi kyau mutumin yă kasance shi kaɗai ba. Zan yi masa mataimakin da ya dace da shi.”
And the LORde God sayd: it is not good that man shulde be alone I will make hym an helper to beare him company:
19 To, Ubangiji Allah ya yi dukan namun jeji da dukan tsuntsayen sama daga ƙasa. Ya kawo su wurin mutumin don yă ga wanda suna zai kira su; kuma duk sunan da mutumin ya kira kowane mai rai, sunansa ke nan.
And after yt the LORde God had make of the erth all maner beastes of the felde and all maner foules of the ayre he brought them vnto Adam to see what he wold call them. And as Ada called all maner livynge beastes: eve so are their names.
20 Saboda haka mutumin ya sa wa dukan dabbobi, da tsuntsayen sama da dukan namun jeji sunaye. Amma ba a sami mataimakin da ya dace da Adamu ba.
And Adam gave names vnto all maner catell and vnto the foules of the ayre and vnto all maner beastes of the felde. But there was no helpe founde vnto Adam to beare him companye
21 Saboda haka Ubangiji Allah ya sa mutumin ya yi barci mai nauyi; yayinda yake barci sai ya ɗauko ɗaya daga cikin haƙarƙarin mutumin, ya kuma rufe wurin da nama.
Then the LORde God cast a slomber on Adam and he slepte. And then he toke out one of his rybbes and in stede ther of he fylled vp the place with flesh.
22 Sa’an nan Ubangiji Allah ya yi mace daga haƙarƙarin da ya ɗauko daga mutumin, ya kuwa kawo ta wurin mutumin.
And the LORde God made of the rybbe which he toke out of Adam a woma and brought her vnto Adam.
23 Sai mutumin ya ce, “Yanzu kam wannan ƙashi ne na ƙasusuwana nama kuma na namana. Za a ce da ita ‘mace,’ gama an ciro ta daga namiji.”
Then sayd Ada this is once bone of my boones and flesh of my flesh. This shall be called woman: because she was take of the man.
24 Wannan ne ya sa mutum yakan bar mahaifinsa da mahaifiyarsa, yă manne wa matarsa, su kuma zama jiki ɗaya.
For this cause shall a man leve father and mother and cleve vnto his wyfe and they shall be one flesh.
25 Mutumin da matarsa, dukansu biyu tsirara suke, ba su kuwa ji kunya ba.
And they were ether of them naked both Adam and hys wyfe ad were not ashamed:

< Farawa 2 >