< Farawa 19 >

1 Mala’ikun nan biyu suka iso Sodom da yamma. Lot kuwa yana zama a hanyar shiga birnin. Da ya gan su, sai ya tashi don yă tarye su, ya kuma rusuna da fuskarsa har ƙasa.
غروب همان روز وقتی که آن دو فرشته به دروازهٔ شهر سدوم رسیدند، لوط در آنجا نشسته بود. به محض مشاهدهٔ آنها، از جا برخاست و به استقبالشان شتافت و روی بر زمین نهاده، گفت:
2 Ya ce, “Ranku yă daɗe, ina roƙonku ku ratsa zuwa gidan bawanku. Ku wanke ƙafafunku, ku kwana, sa’an nan ku kama hanyarku da sassafe.” Suka ce, “A’a, za mu kwana a dandali.”
«ای سَروَرانم، امشب به منزل من بیایید و پاهایتان را بشویید و میهمان من باشید. فردا صبحِ زود هر وقت بخواهید، می‌توانید حرکت کنید.» ولی آنها گفتند: «در میدان شهر شب را به سر خواهیم برد.»
3 Amma ya nace musu ƙwarai, sai suka tafi tare da shi, suka kuma shiga gidansa. Ya shirya musu abinci, ya gasa burodi marasa yisti, suka ci.
اما لوط آنقدر اصرار نمود تا اینکه آنها راضی شدند و به خانهٔ وی رفتند. او نان فطیر پخت و شام مفصلی تهیه دید و به ایشان داد که خوردند.
4 Kafin suka shiga barci, sai ga dukan mutane, ƙanana da manya daga kowane ɓangare na birnin Sodom, suka kewaye gidan.
سپس در حالی که آماده می‌شدند که بخوابند، مردان شهر سدوم، پیر و جوان، از گوشه و کنار شهر، منزل لوط را محاصره کرده،
5 Suka kira Lot, suka ce, “Ina mutanen da suka zo wurinka a daren nan? Fito mana da su waje domin mu kwana da su.”
فریاد زدند: «ای لوط، آن دو مرد را که امشب میهمان تو هستند، پیش ما بیرون بیاور تا آنها را بشناسیم.»
6 Lot ya fita daga cikin gida, ya rufe ƙofar a bayansa. Ya je wurin mutanen
لوط از منزل خارج شد تا با آنها صحبت کند و در را پشت سر خود بست.
7 ya ce musu, “A’a, abokaina kada ku yi wannan mummunan abu.
او به ایشان گفت: «نه، ای برادران من، خواهش می‌کنم چنین کار زشتی نکنید.
8 Duba, ina da’ya’ya mata biyu waɗanda ba su taɓa sanin namiji ba, bari in kawo muku su ku yi kome da kuke so da su. Amma kada ku taɓa waɗannan mutane, gama su baƙina ne kuma dole in tsare su.”
ببینید، من دو دختر باکره دارم. آنها را به شما می‌دهم. هر کاری که دلتان می‌خواهد با آنها بکنید؛ اما با این دو مرد کاری نداشته باشید، چون آنها در پناه من هستند.»
9 Sai mutanen birnin suka amsa, “Ba mu wuri! Wannan mutum ya zo nan kamar baƙo, ga shi yanzu yana so yă zama alƙali! Za mu wulaƙanta ka fiye da su.” Suka ci gaba da matsa wa Lot lamba, suka matsa kusa domin su fasa ƙofar.
مردان شهر جواب دادند: «از سر راه ما کنار برو! ما اجازه دادیم در شهر ما ساکن شوی و حالا به ما امر و نهی می‌کنی. الان با تو بدتر از آن کاری که می‌خواستیم با آنها بکنیم، خواهیم کرد.» آنگاه به طرف لوط حمله برده، شروع به شکستن در خانهٔ او نمودند.
10 Amma mutanen da suke ciki suka miƙa hannunsu, suka ja Lot zuwa cikin gida, suka rufe ƙofar.
اما آن دو مرد دست خود را دراز کرده، لوط را به داخل خانه کشیدند و در را بستند،
11 Sai suka bugi mutanen da suke a bakin ƙofar gidan da makanta, ƙanana da manya duka, har suka gajiyar da kansu, suna lalluba inda ƙofar take.
و چشمان تمام مردانی را که در بیرون خانه بودند، کور کردند تا نتوانند درِ خانه را پیدا کنند.
12 Mutanen nan biyun suka ce wa Lot, “Kana da wani a nan, ko surukai, ko’ya’ya maza ko mata, ko kuwa wani dai a cikin birni wanda yake naka? Ka fitar da su daga nan,
آن دو مرد از لوط پرسیدند: «در این شهر چند نفر قوم و خویش داری؟ پسران و دختران و دامادان و هر کسی را که داری از این شهر بیرون ببر.
13 gama za mu hallaka wannan wuri. Kukan da aka yi ga Ubangiji game da mutanen birnin nan ya yi yawa sosai, ya sa har ya aiko mu domin mu hallaka birnin.”
زیرا می‌خواهیم این شهر را نابود کنیم. فریاد علیه ظلمِ مردمِ این شهر به حضور خداوند رسیده و او ما را فرستاده است تا آن را ویران کنیم.»
14 Saboda haka Lot ya tafi ya yi magana da surukansa waɗanda suka yi alkawari za su aure’ya’yansa mata. Ya ce, “Ku yi sauri ku fita daga wannan wuri, gama Ubangiji yana gab da hallaka birnin.” Amma surukansa suka ɗauka wasa yake yi.
پس لوط با شتاب رفت و به نامزدان دخترانش گفت: «عجله کنید! از شهر بگریزید، چون خداوند می‌خواهد آن را ویران کند!» ولی این حرف به نظر آنها مسخره آمد.
15 Gari na wayewa, sai mala’ikun nan suka ƙarfafa Lot suna cewa, “Yi sauri! Ka ɗauki matarka da’ya’yanka biyu mata waɗanda suke a nan, don kada a shafe ku sa’ad da ake hukunta birnin.”
سپیده دم روز بعد، آن دو فرشته به لوط گفتند: «عجله کن! همسر و دو دخترت را که اینجا هستند بردار و تا دیر نشده فرار کن وگرنه شما هم با مردمِ گناهکار این شهر هلاک خواهید شد.»
16 Da yana jan jiki, sai mutanen suka kama hannunsa da hannuwan matarsa da na’ya’yansa biyu mata, suka kai su bayan birni, gama Ubangiji ya nuna musu jinƙai.
در حالی که لوط درنگ می‌کرد آن دو مرد دستهای او و زن و دو دخترش را گرفته، به جای امنی در خارج از شهر بردند، چون خداوند بر آنها رحم کرده بود.
17 Da suka fitar da su, sai ɗaya daga cikin mala’ikun ya ce, “Ku gudu domin ranku; kada ku duba baya, kada kuma ku tsaya ko’ina cikin kwarin! Ku gudu zuwa cikin duwatsu, don kada a hallaka ku!”
یکی از آن دو مرد به لوط گفت: «برای نجات جان خود فرار کنید و به پشت سر هم نگاه نکنید. به کوهستان بروید، چون اگر در دشت بمانید مرگتان حتمی است.»
18 Amma Lot ya ce musu, “A’a, ranka yă daɗe, ka yi haƙuri!
لوط جواب داد: «ای سَروَرم، تمنا می‌کنم از ما نخواهید چنین کاری بکنیم.
19 Bawanku ya riga ya sami tagomashi daga gare ku, kun kuma nuna mini alheri mai yawa. Ba zan iya in gudu zuwa duwatsu ba, wannan masifa za tă same ni, zan kuma mutu.
تو در حق من خوبی کرده، جانم را نجات داده‌ای، و محبت بزرگی در حق من کرده‌ای. اما من نمی‌توانم به کوهستان فرار کنم، زیرا می‌ترسم قبل از رسیدن به آنجا این بلا دامنگیر من بشود و بمیرم.
20 Ga ɗan gari can ya fi kusa inda zan gudu in fake. Bari in gudu zuwa can, in tsirar da raina.”
ببینید این دهکده چقدر نزدیک و کوچک است! اینطور نیست؟ پس بگذارید به آنجا بروم و در امان باشم.»
21 Sai ya ce masa, “Na yarda da abin da ka ce, ba zan hallakar da garin da ka ambata ba.
او گفت: «بسیار خوب، خواهش تو را می‌پذیرم و آن دهکده را خراب نخواهم کرد.
22 Gaggauta, ka gudu zuwa can, ba zan yi kome ba sai ka isa can.” (Domin haka ne ake kira garin Zowar.)
پس عجله کن! زیرا تا وقتی به آنجا نرسیده‌ای، نمی‌توانم کاری انجام دهم.» (به این دلیل آن دهکده را صوغر یعنی «کوچک» نام نهادند.)
23 A lokacin da Lot ya isa Zowar, rana ta hau.
آفتاب داشت طلوع می‌کرد که لوط وارد صوغر شد.
24 Sai Ubangiji ya yi ta zuba kibiritu a bisa Sodom da Gomorra daga sama.
آنگاه خداوند از آسمان گوگرد مشتعل بر سدوم و عموره بارانید
25 Haka ya hallakar da waɗannan birane da kuma kwarinsu gaba ɗaya, haɗe da dukan waɗanda suke zama a biranen, da kuma dukan shuke-shuke da suke cikin ƙasar.
و آن دو شهر را با همهٔ شهرها و دهات آن دشت و تمام سکنه و نباتات آن به کلی نابود کرد.
26 Amma matar Lot ta waiwaya baya, ta kuma zama ginshiƙin gishiri.
اما زن لوط به پشت سر نگاه کرد و به ستونی از نمک مبدل گردید.
27 Da sassafe kashegari, Ibrahim ya tashi ya koma wurin da dā ya tsaya a gaban Ubangiji.
ابراهیم صبح زود برخاست و به سوی همان مکانی که در آن به حضور خداوند ایستاده بود، شتافت.
28 Ya duba ta wajen Sodom da Gomorra, da wajen dukan filayen ƙasar, sai ya ga hayaƙi baƙin ƙirin yana tashi daga ƙasar kamar hayaƙi daga matoya.
او به سوی شهرهای سدوم و عموره و آن دشت نظر انداخت و دید که اینک دود از آن شهرها چون دود کوره بالا می‌رود.
29 Saboda haka sa’ad da Allah ya hallaka waɗannan biranen kwarin, ya tuna da Ibrahim, ya kuma fitar da Lot daga masifar da ta hallaka biranen da Lot ya zauna.
هنگامی که خدا شهرهای دشتی را که لوط در آن ساکن بود نابود می‌کرد، دعای ابراهیم را اجابت فرمود و لوط را از گرداب مرگ که آن شهرها را به کام خود کشیده بود، رهانید.
30 Lot da’ya’yansa biyu mata suka bar Zowar suka kuma zauna a cikin duwatsu, gama ya ji tsoro yă zauna a Zowar. Shi da’ya’yansa biyu mata suka zauna a ciki wani kogo.
اما لوط ترسید در صوغر بماند. پس آنجا را ترک نموده، با دو دختر خود به کوهستان رفت و در غاری ساکن شد.
31 Wata rana’yarsa babba ta ce wa ƙanuwarta, “Mahaifinmu ya tsufa, kuma babu wani mutum kusa a nan da zai yi mana ciki mu haifi’ya’ya; yadda al’ada take a ko’ina a duniya.
روزی دختر بزرگ لوط به خواهرش گفت: «در تمامی این ناحیه مردی یافت نمی‌شود تا با ما ازدواج کند. پدر ما هم به‌زودی پیر خواهد شد و دیگر نخواهد توانست نسلی از خود باقی گذارد.
32 Bari mu sa mahaifinmu yă sha ruwan inabi, sa’an nan sai mu kwana da shi, don kada zuriyar mahaifinmu ta ƙare.”
پس بیا به او شراب بنوشانیم و با وی همبستر شویم و به این طریق نسل پدرمان را حفظ کنیم.»
33 A wannan dare, suka sa mahaifinsu ya sha ruwan inabi,’yar farin ta shiga ta kwana da shi. Shi kuwa bai san sa’ad da ta kwanta ko sa’ad da ta tashi ba.
پس همان شب او را مست کردند و دختر بزرگتر با پدرش همبستر شد. اما لوط از خوابیدن و برخاستن دخترش آگاه نشد.
34 Kashegari,’yar farin ta ce wa ƙanuwar, “Jiya da dare na kwana da mahaifina. Bari mu sa yă sha ruwan inabi kuma yau da dare, ke ma ki shiga ki kwana da shi, domin kada zuriyar mahaifinmu ta ƙare.”
صبح روز بعد، دختر بزرگتر به خواهر کوچک خود گفت: «من دیشب با پدرم همبستر شدم. بیا تا امشب هم دوباره به او شراب بنوشانیم و این دفعه تو برو و با او همبستر شو تا بدین وسیله نسلی از پدرمان نگه داریم.»
35 Sai suka sa mahaifinsu ya sha ruwan inabi, a wannan dare ma, ƙanuwar ta shiga ta kwana da shi. Bai kuwa san sa’ad da ta kwanta ko sa’ad da ta tashi ba.
پس آن شب دوباره او را مست کردند و دختر کوچکتر با او همبستر شد. این بار هم لوط مثل دفعهٔ پیش چیزی نفهمید.
36 Ta haka’ya’yan Lot biyu mata duk suka yi ciki daga mahaifinsu.
بدین طریق آن دو دختر از پدر خود حامله شدند.
37 ’Yar farin ta haifi ɗa, ta kuma ba shi suna Mowab, shi ne mahaifin Mowabawa a yau.
دختر بزرگتر پسری زایید و او را موآب نامید. (قبیلهٔ موآب از او به وجود آمد.)
38 ’Yar ƙaramar ma ta haifi ɗa, ta kuwa ba shi suna Ben-Ammi, shi ne mahaifin Ammonawa a yau.
دختر کوچکتر نیز پسری زایید و نام او را بِن‌عمّی گذاشت. (قبیله عمون از او به وجود آمد.)

< Farawa 19 >