< Farawa 19 >

1 Mala’ikun nan biyu suka iso Sodom da yamma. Lot kuwa yana zama a hanyar shiga birnin. Da ya gan su, sai ya tashi don yă tarye su, ya kuma rusuna da fuskarsa har ƙasa.
And tweyne aungels camen to Sodom in the euentide, while Loth sat in the yatis of the citee. And whanne he hadde seyn hem, he roos, and yede ayens hem, and worschipide lowe to erthe,
2 Ya ce, “Ranku yă daɗe, ina roƙonku ku ratsa zuwa gidan bawanku. Ku wanke ƙafafunku, ku kwana, sa’an nan ku kama hanyarku da sassafe.” Suka ce, “A’a, za mu kwana a dandali.”
and seide, My lordis, Y biseche, bowe ye in to the hous of youre child, and dwelle ye there; waische ye youre feet, and in the morewtid ye schulen go in to youre weie. Whiche seiden, Nay, but we schulen dwelle in the street.
3 Amma ya nace musu ƙwarai, sai suka tafi tare da shi, suka kuma shiga gidansa. Ya shirya musu abinci, ya gasa burodi marasa yisti, suka ci.
He constreynede hem greetli, that thei schulden turne to hym. And whanne thei weren entrid in to his hous, he made a feeste, he bakide therf breed, and thei eten.
4 Kafin suka shiga barci, sai ga dukan mutane, ƙanana da manya daga kowane ɓangare na birnin Sodom, suka kewaye gidan.
Forsothe bifore that thei yeden to sleepe, men of the citee compassiden his hows, fro a child `til to an eld man, al the puple togidre;
5 Suka kira Lot, suka ce, “Ina mutanen da suka zo wurinka a daren nan? Fito mana da su waje domin mu kwana da su.”
and thei clepiden Loth, and seiden to him, Where ben the men that entriden to thee to nyyt? brynge hem out hidur, that we `knowe hem.
6 Lot ya fita daga cikin gida, ya rufe ƙofar a bayansa. Ya je wurin mutanen
And Loth yede out to hem `bihynde the bak, and closide the dore,
7 ya ce musu, “A’a, abokaina kada ku yi wannan mummunan abu.
and seide, Y biseche, nyle ye, my britheren, nyle ye do this yuel.
8 Duba, ina da’ya’ya mata biyu waɗanda ba su taɓa sanin namiji ba, bari in kawo muku su ku yi kome da kuke so da su. Amma kada ku taɓa waɗannan mutane, gama su baƙina ne kuma dole in tsare su.”
Y haue twey douytris, that knewen not yit man; Y schal lede out hem to you, and mys vse ye hem as it plesith you, so that ye doon noon yuel to these men, for thei entriden vndur the schadewe of my roof.
9 Sai mutanen birnin suka amsa, “Ba mu wuri! Wannan mutum ya zo nan kamar baƙo, ga shi yanzu yana so yă zama alƙali! Za mu wulaƙanta ka fiye da su.” Suka ci gaba da matsa wa Lot lamba, suka matsa kusa domin su fasa ƙofar.
And thei seiden, Go thou fro hennus. And eft thei seiden, Thou entridist as a comelyng; wher that thou deme? therfor we schulen turment thee more than these. And thei diden violentli to Loth ful greetli. Thanne it was nyy that thei wolden breke the doris; and lo!
10 Amma mutanen da suke ciki suka miƙa hannunsu, suka ja Lot zuwa cikin gida, suka rufe ƙofar.
the men puttiden hoond, and ledden in Loth to hem, and thei closiden the dore.
11 Sai suka bugi mutanen da suke a bakin ƙofar gidan da makanta, ƙanana da manya duka, har suka gajiyar da kansu, suna lalluba inda ƙofar take.
And thei smyten with blyndenesse hem that weren withoutforth, fro the leest til to the moost; so that thei myyten not fynde the dore.
12 Mutanen nan biyun suka ce wa Lot, “Kana da wani a nan, ko surukai, ko’ya’ya maza ko mata, ko kuwa wani dai a cikin birni wanda yake naka? Ka fitar da su daga nan,
Forsothe thei seiden to Loth, Hast thou here ony man of thine, hosebonde of thi douyter, ethir sones, ethir douytris; lede thou out of this citee alle men that ben thine,
13 gama za mu hallaka wannan wuri. Kukan da aka yi ga Ubangiji game da mutanen birnin nan ya yi yawa sosai, ya sa har ya aiko mu domin mu hallaka birnin.”
for we schulen do a wey this place, for the cry of hem encreesside bifor the Lord, which sente vs that we leese hem.
14 Saboda haka Lot ya tafi ya yi magana da surukansa waɗanda suka yi alkawari za su aure’ya’yansa mata. Ya ce, “Ku yi sauri ku fita daga wannan wuri, gama Ubangiji yana gab da hallaka birnin.” Amma surukansa suka ɗauka wasa yake yi.
And so Loth yede out, and spak to the hosebondys of his douytris, that schulden take hise douytris, and seide, Rise ye, and go ye out of this place; for the Lord schal do awey this citee. And he was seyn to hem to speke as pleiynge.
15 Gari na wayewa, sai mala’ikun nan suka ƙarfafa Lot suna cewa, “Yi sauri! Ka ɗauki matarka da’ya’yanka biyu mata waɗanda suke a nan, don kada a shafe ku sa’ad da ake hukunta birnin.”
And whanne the morewtid was, the aungels constreyneden hym, and seiden, Rise thou, and take thi wijf, and thi twey douytris whiche thou hast, lest also thou perische to gidere in the synne of the citee.
16 Da yana jan jiki, sai mutanen suka kama hannunsa da hannuwan matarsa da na’ya’yansa biyu mata, suka kai su bayan birni, gama Ubangiji ya nuna musu jinƙai.
While he dissymelide, thei token his hond, and the hond of his wijf, and of his twey doutris; for the Lord sparide hym.
17 Da suka fitar da su, sai ɗaya daga cikin mala’ikun ya ce, “Ku gudu domin ranku; kada ku duba baya, kada kuma ku tsaya ko’ina cikin kwarin! Ku gudu zuwa cikin duwatsu, don kada a hallaka ku!”
And thei ledden out hym, and settiden with out the citee. There thei spaken to him, and seiden, Saue thou thi lijf; nyle thou biholde bihynde thi bac, nether stond thou in al the cuntre aboute, but make thee saaf in the hil; lest also thou perische togidere.
18 Amma Lot ya ce musu, “A’a, ranka yă daɗe, ka yi haƙuri!
And Loth seide to hem, My lord, Y biseche,
19 Bawanku ya riga ya sami tagomashi daga gare ku, kun kuma nuna mini alheri mai yawa. Ba zan iya in gudu zuwa duwatsu ba, wannan masifa za tă same ni, zan kuma mutu.
for thi seruaunt hath founde grace bifore thee, and thou hast magnyfied thi grace and mercy, which thou hast do with me, that thou schuldist saue my lijf; Y may not be saued in the hil, lest perauenture yuel take me, and Y die;
20 Ga ɗan gari can ya fi kusa inda zan gudu in fake. Bari in gudu zuwa can, in tsirar da raina.”
a litil citee is here bisidis, to which Y may fle, and Y schal be saued ther ynne; where it is not a litil citee? and my soule schal lyue ther ynne.
21 Sai ya ce masa, “Na yarda da abin da ka ce, ba zan hallakar da garin da ka ambata ba.
And he seide to Loth, Lo! also in this Y haue resseyued thi preieris, that Y distrye not the citee, for which thou hast spoke;
22 Gaggauta, ka gudu zuwa can, ba zan yi kome ba sai ka isa can.” (Domin haka ne ake kira garin Zowar.)
haste thou, and be thou saued there, for Y may not do ony thing til thou entre thidur. Therfor the name of that citee was clepid Segor.
23 A lokacin da Lot ya isa Zowar, rana ta hau.
The sunne roos on erthe, and Loth entride in to Segor.
24 Sai Ubangiji ya yi ta zuba kibiritu a bisa Sodom da Gomorra daga sama.
Therfor the Lord reynede on Sodom and Gomorre brynston and fier, fro the Lord fro heuene,
25 Haka ya hallakar da waɗannan birane da kuma kwarinsu gaba ɗaya, haɗe da dukan waɗanda suke zama a biranen, da kuma dukan shuke-shuke da suke cikin ƙasar.
and distriede these citees, and al the cuntrey aboute; he destriede alle enhabiters of citees, and all grene thingis of erthe.
26 Amma matar Lot ta waiwaya baya, ta kuma zama ginshiƙin gishiri.
And his wijf lokide abac, and was turned in to an ymage of salt.
27 Da sassafe kashegari, Ibrahim ya tashi ya koma wurin da dā ya tsaya a gaban Ubangiji.
Forsothe Abraham risynge eerly, where he stood bifore with the Lord,
28 Ya duba ta wajen Sodom da Gomorra, da wajen dukan filayen ƙasar, sai ya ga hayaƙi baƙin ƙirin yana tashi daga ƙasar kamar hayaƙi daga matoya.
bihelde Sodom and Gomorre, and al the lond of that cuntrey; and he seiy a deed sparcle stiynge fro erthe, as the smoke of a furneis.
29 Saboda haka sa’ad da Allah ya hallaka waɗannan biranen kwarin, ya tuna da Ibrahim, ya kuma fitar da Lot daga masifar da ta hallaka biranen da Lot ya zauna.
For whanne God distriede the citees of that cuntrey, he hadde mynde of Abraham, and delyuerede Loth fro destriynge of the citees in whiche he dwellide.
30 Lot da’ya’yansa biyu mata suka bar Zowar suka kuma zauna a cikin duwatsu, gama ya ji tsoro yă zauna a Zowar. Shi da’ya’yansa biyu mata suka zauna a ciki wani kogo.
And Loth stiede fro Segor, and dwellide in the hil, and hise twey douytris with him, for he dredde to dwelle in Segor; and he dwellide in a denne, he and his twey douytris with hym.
31 Wata rana’yarsa babba ta ce wa ƙanuwarta, “Mahaifinmu ya tsufa, kuma babu wani mutum kusa a nan da zai yi mana ciki mu haifi’ya’ya; yadda al’ada take a ko’ina a duniya.
And the more douytre seide to the lasse, Oure fadre is eld, and no man is left in erthe, that may entre to vs, bi the custom of al erthe;
32 Bari mu sa mahaifinmu yă sha ruwan inabi, sa’an nan sai mu kwana da shi, don kada zuriyar mahaifinmu ta ƙare.”
come thou, make we him drunkun of wyn, and slepe we with him, that we moun kepe seed of oure fadir.
33 A wannan dare, suka sa mahaifinsu ya sha ruwan inabi,’yar farin ta shiga ta kwana da shi. Shi kuwa bai san sa’ad da ta kwanta ko sa’ad da ta tashi ba.
And so thei yauen to her fadir to drynke wyn in that nyyt, and the more douyter entrede, and slepte with hir fadir; and he feelide not, nethir whanne the douytir lay doun, nether whanne sche roos.
34 Kashegari,’yar farin ta ce wa ƙanuwar, “Jiya da dare na kwana da mahaifina. Bari mu sa yă sha ruwan inabi kuma yau da dare, ke ma ki shiga ki kwana da shi, domin kada zuriyar mahaifinmu ta ƙare.”
And in the tothir dai the more douytir seide to the lasse, Lo! Y slepte yistirdai with my fadir, yyue we to hym to drynk wyn also in this nyyt; and thou schalt slepe with hym, that we saue seed of oure fadir.
35 Sai suka sa mahaifinsu ya sha ruwan inabi, a wannan dare ma, ƙanuwar ta shiga ta kwana da shi. Bai kuwa san sa’ad da ta kwanta ko sa’ad da ta tashi ba.
And thei yauen to her fadir also in that nyyt to drynke wyn, and the lesse douytir entride, and slepte with him; and sotheli he feelide not thanne whanne sche lay doun, nether whanne sche roos.
36 Ta haka’ya’yan Lot biyu mata duk suka yi ciki daga mahaifinsu.
Therfor the twei douytris of Loth conseyuede of hir fadir.
37 ’Yar farin ta haifi ɗa, ta kuma ba shi suna Mowab, shi ne mahaifin Mowabawa a yau.
And the more douytre childide a sone, and clepide his name Moab; he is the fadir of men of Moab `til in to present dai.
38 ’Yar ƙaramar ma ta haifi ɗa, ta kuwa ba shi suna Ben-Ammi, shi ne mahaifin Ammonawa a yau.
And the lesse douyter childide a sone, and clepide his name Amon, that is, the sone of my puple; he is the fadir of men of Amon til to day.

< Farawa 19 >