< Farawa 19 >

1 Mala’ikun nan biyu suka iso Sodom da yamma. Lot kuwa yana zama a hanyar shiga birnin. Da ya gan su, sai ya tashi don yă tarye su, ya kuma rusuna da fuskarsa har ƙasa.
And there came. ij. angells to Sodome at euen. And Lot satt at the gate of the cyte. And Lot sawe the and rose vp agaynst them and he bowed hym selfe to he grounde with his face.
2 Ya ce, “Ranku yă daɗe, ina roƙonku ku ratsa zuwa gidan bawanku. Ku wanke ƙafafunku, ku kwana, sa’an nan ku kama hanyarku da sassafe.” Suka ce, “A’a, za mu kwana a dandali.”
And he sayde: Se lordes turne in I praye you in to youre servauntes house and tary all nyghte and wash youre fete and ryse vp early and go on youre wayes. And they sayde: nay but we will byde in the streates all nyghte.
3 Amma ya nace musu ƙwarai, sai suka tafi tare da shi, suka kuma shiga gidansa. Ya shirya musu abinci, ya gasa burodi marasa yisti, suka ci.
And he copelled them excedyngly. And they turned in vnto hym and entred in to his house and he made them a feaste and dyd bake swete cakes and they ate.
4 Kafin suka shiga barci, sai ga dukan mutane, ƙanana da manya daga kowane ɓangare na birnin Sodom, suka kewaye gidan.
But before they went to rest the men of the cyte of Sodome compassed the house rownde aboute both olde and yonge all the people from all quarters.
5 Suka kira Lot, suka ce, “Ina mutanen da suka zo wurinka a daren nan? Fito mana da su waje domin mu kwana da su.”
And they called vnto Lot and sayde vnto him: where are the men which came in to thy house to nyghte? brynge the out unto vs that we may do oure lust with them.
6 Lot ya fita daga cikin gida, ya rufe ƙofar a bayansa. Ya je wurin mutanen
And Lot went out at doores vnto them and shote the dore after him
7 ya ce musu, “A’a, abokaina kada ku yi wannan mummunan abu.
and sayde: nay for goddes sake brethren do not so wekedly.
8 Duba, ina da’ya’ya mata biyu waɗanda ba su taɓa sanin namiji ba, bari in kawo muku su ku yi kome da kuke so da su. Amma kada ku taɓa waɗannan mutane, gama su baƙina ne kuma dole in tsare su.”
Beholde I haue two doughters which haue knowne no man the will I brynge out vnto you: do with them as it semeth you good: Only vnto these men do nothynge for therfore came they vnder the shadowe of my rofe.
9 Sai mutanen birnin suka amsa, “Ba mu wuri! Wannan mutum ya zo nan kamar baƙo, ga shi yanzu yana so yă zama alƙali! Za mu wulaƙanta ka fiye da su.” Suka ci gaba da matsa wa Lot lamba, suka matsa kusa domin su fasa ƙofar.
And they sayde: come hither. And they sayde: camest thou not in to sogeorne and wilt thou be now a iudge? we will suerly deale worse with the than with themAnd as they preased fore vppon Lot and beganne to breake vp the doore
10 Amma mutanen da suke ciki suka miƙa hannunsu, suka ja Lot zuwa cikin gida, suka rufe ƙofar.
the men put forth their handes and pulled Lot in to the house to them and shott to the doore.
11 Sai suka bugi mutanen da suke a bakin ƙofar gidan da makanta, ƙanana da manya duka, har suka gajiyar da kansu, suna lalluba inda ƙofar take.
And the men that were at the doore of the house they smote with blyndnesse both small and greate: so that they coude not fynde the doore.
12 Mutanen nan biyun suka ce wa Lot, “Kana da wani a nan, ko surukai, ko’ya’ya maza ko mata, ko kuwa wani dai a cikin birni wanda yake naka? Ka fitar da su daga nan,
And the men sayde moreover vnto Lot: Yf thou have yet here any sonne in lawe or sonnes or doughters or what so euer thou hast in the cyte brynge it out of this place:
13 gama za mu hallaka wannan wuri. Kukan da aka yi ga Ubangiji game da mutanen birnin nan ya yi yawa sosai, ya sa har ya aiko mu domin mu hallaka birnin.”
for we must destroy this place because the crye of the is great before the LORde. Wherfore he hath sent vs to destroy it.
14 Saboda haka Lot ya tafi ya yi magana da surukansa waɗanda suka yi alkawari za su aure’ya’yansa mata. Ya ce, “Ku yi sauri ku fita daga wannan wuri, gama Ubangiji yana gab da hallaka birnin.” Amma surukansa suka ɗauka wasa yake yi.
And Lot went out and spake vnto his sonnes in lawe which shulde haue maried his doughters and sayde: stonde vpp and get yow out of this place for the LORde will destroy the cite. But he semed as though he had mocked vnto his sonnes in law.
15 Gari na wayewa, sai mala’ikun nan suka ƙarfafa Lot suna cewa, “Yi sauri! Ka ɗauki matarka da’ya’yanka biyu mata waɗanda suke a nan, don kada a shafe ku sa’ad da ake hukunta birnin.”
And as the mornynge arose the angells caused Lot to spede him saynge. Stonde vp take thy wyfe and thy two doughters and that that is at hande lest thou perish in the synne of the cyte.
16 Da yana jan jiki, sai mutanen suka kama hannunsa da hannuwan matarsa da na’ya’yansa biyu mata, suka kai su bayan birni, gama Ubangiji ya nuna musu jinƙai.
And as he prolonged the tyme the men caught both him his wife ad his two doughters by the handes because the LORde was mercyfull vnto him ad they brought him forth and sette him without the cyte.
17 Da suka fitar da su, sai ɗaya daga cikin mala’ikun ya ce, “Ku gudu domin ranku; kada ku duba baya, kada kuma ku tsaya ko’ina cikin kwarin! Ku gudu zuwa cikin duwatsu, don kada a hallaka ku!”
When they had brought them out they sayde: Saue thy lyfe and loke not behynde the nether tary thou in any place of the contre but saue thy selfe in the mountayne lest thou perisshe.
18 Amma Lot ya ce musu, “A’a, ranka yă daɗe, ka yi haƙuri!
Than sayde Lot vnto them: Oh nay my lorde:
19 Bawanku ya riga ya sami tagomashi daga gare ku, kun kuma nuna mini alheri mai yawa. Ba zan iya in gudu zuwa duwatsu ba, wannan masifa za tă same ni, zan kuma mutu.
beholde in as moch as thy servaunte hath fownde grace in thy syghte now make thi mercy great which thou shewest vnto me in savinge my lyfe. For I can not saue my selfe in the mountayns lest some misfortune fall vpon me and I dye.
20 Ga ɗan gari can ya fi kusa inda zan gudu in fake. Bari in gudu zuwa can, in tsirar da raina.”
Beholde here is a cyte by to flee vnto and it is a lytle one: let me saue my selfe therein: is it not a litle one that my soule may lyue?
21 Sai ya ce masa, “Na yarda da abin da ka ce, ba zan hallakar da garin da ka ambata ba.
And he sayde to him: se I haue receaved thy request as concernynge this thynge that I will nott overthrowe this cytie for the which thou hast spoken.
22 Gaggauta, ka gudu zuwa can, ba zan yi kome ba sai ka isa can.” (Domin haka ne ake kira garin Zowar.)
Haste the ad saue thy selfe there for I can do nothynge tyll thou be come in thyder. And therfore the name of the cyte is called Zoar.
23 A lokacin da Lot ya isa Zowar, rana ta hau.
And the sone was vppon the erth when Lot was entred in to Zoar.
24 Sai Ubangiji ya yi ta zuba kibiritu a bisa Sodom da Gomorra daga sama.
Than the LORde rayned vpon Sodome and Gomorra brymstone and fyre from the LORde out of heaven
25 Haka ya hallakar da waɗannan birane da kuma kwarinsu gaba ɗaya, haɗe da dukan waɗanda suke zama a biranen, da kuma dukan shuke-shuke da suke cikin ƙasar.
and overthrewe those cyteis and all the region and all that dwelled in the cytes and that that grewe vpon the erth.
26 Amma matar Lot ta waiwaya baya, ta kuma zama ginshiƙin gishiri.
And lots wyfe loked behynde her ad was turned in to a pillare of salte.
27 Da sassafe kashegari, Ibrahim ya tashi ya koma wurin da dā ya tsaya a gaban Ubangiji.
Abraham rose vp early and got him to the place where he stode before the LORde
28 Ya duba ta wajen Sodom da Gomorra, da wajen dukan filayen ƙasar, sai ya ga hayaƙi baƙin ƙirin yana tashi daga ƙasar kamar hayaƙi daga matoya.
and loked toward Sodome and Gomorra and toward all the londe of that contre. And as he loked: beholde the smoke of the contre arose as it had bene the smoke of a fornace.
29 Saboda haka sa’ad da Allah ya hallaka waɗannan biranen kwarin, ya tuna da Ibrahim, ya kuma fitar da Lot daga masifar da ta hallaka biranen da Lot ya zauna.
But yet whe God destroyed the cities of ye regio he thought a pon Abraha: and sent Lot out from the dager of the overthrowenge when he overthrewe the cyttes where Lot dwelled.
30 Lot da’ya’yansa biyu mata suka bar Zowar suka kuma zauna a cikin duwatsu, gama ya ji tsoro yă zauna a Zowar. Shi da’ya’yansa biyu mata suka zauna a ciki wani kogo.
And Lot departed out of Zoar and dwelled in the mountayns ad his. ij. doughters with him for he feared to tary in Zoar: he dweld therfore in a caue both he and his. ij. doughters also.
31 Wata rana’yarsa babba ta ce wa ƙanuwarta, “Mahaifinmu ya tsufa, kuma babu wani mutum kusa a nan da zai yi mana ciki mu haifi’ya’ya; yadda al’ada take a ko’ina a duniya.
Than sayde the elder vnto the yonger oure father is olde and there are no moo men in the erth to come in vnto vs after the maner of all the world.
32 Bari mu sa mahaifinmu yă sha ruwan inabi, sa’an nan sai mu kwana da shi, don kada zuriyar mahaifinmu ta ƙare.”
Come therfore let vs geue oure father wyne to dryncke and let vs lye with him that we may saue seed of oure father.
33 A wannan dare, suka sa mahaifinsu ya sha ruwan inabi,’yar farin ta shiga ta kwana da shi. Shi kuwa bai san sa’ad da ta kwanta ko sa’ad da ta tashi ba.
And they gaue their father wyne to drynke that same nyghte. And the elder doughter went and laye with her father. And he perceaued it not nether when she laye doune nether when she rose vp.
34 Kashegari,’yar farin ta ce wa ƙanuwar, “Jiya da dare na kwana da mahaifina. Bari mu sa yă sha ruwan inabi kuma yau da dare, ke ma ki shiga ki kwana da shi, domin kada zuriyar mahaifinmu ta ƙare.”
And on the morowe the elder sayde vnto the yonger: beholde yesternyghte laye I with my father. Let us geue hym wyne to drinke this nyghte also and goo thou and lye with him and let us saue seed of oure father.
35 Sai suka sa mahaifinsu ya sha ruwan inabi, a wannan dare ma, ƙanuwar ta shiga ta kwana da shi. Bai kuwa san sa’ad da ta kwanta ko sa’ad da ta tashi ba.
And they gaue their father wyne to drincke that nyghte also. And the yonger arose and laye with him. And he perceaved it not: nether when she laye downe nether when she rose vp.
36 Ta haka’ya’yan Lot biyu mata duk suka yi ciki daga mahaifinsu.
Thus were both the doughters of lot with childe by their father
37 ’Yar farin ta haifi ɗa, ta kuma ba shi suna Mowab, shi ne mahaifin Mowabawa a yau.
And the elder bare a sone and called hym Moab which is the father of the Moabytes vnto this daye.
38 ’Yar ƙaramar ma ta haifi ɗa, ta kuwa ba shi suna Ben-Ammi, shi ne mahaifin Ammonawa a yau.
And the yonger bare a sonne and called hym Ben Ammi which is the father of the childern of Ammon vnto this daye.

< Farawa 19 >