< Farawa 19 >

1 Mala’ikun nan biyu suka iso Sodom da yamma. Lot kuwa yana zama a hanyar shiga birnin. Da ya gan su, sai ya tashi don yă tarye su, ya kuma rusuna da fuskarsa har ƙasa.
De to Engle kom nu til Sodoma ved Aftenstid. Lot sad i Sodomas Port, og da han fik Øje på dem, stod han op og gik dem i Møde, bøjede sig til Jorden
2 Ya ce, “Ranku yă daɗe, ina roƙonku ku ratsa zuwa gidan bawanku. Ku wanke ƙafafunku, ku kwana, sa’an nan ku kama hanyarku da sassafe.” Suka ce, “A’a, za mu kwana a dandali.”
og sagde: "Kære Herrer, tag dog ind og overnat i eders Træls Hus og tvæt eders Fødder; i Morgen tidlig kan I drage videre!" Men de sagde: "Nej, vi vil overnatte på Gaden."
3 Amma ya nace musu ƙwarai, sai suka tafi tare da shi, suka kuma shiga gidansa. Ya shirya musu abinci, ya gasa burodi marasa yisti, suka ci.
Da nødte han dem stærkt, og de tog ind i hans Hus; derpå tilberedte han dem et Måltid og bagte usyrede Kager, og de spiste.
4 Kafin suka shiga barci, sai ga dukan mutane, ƙanana da manya daga kowane ɓangare na birnin Sodom, suka kewaye gidan.
Men endnu før de havde lagt sig, stimlede Byens Folk, Indbyggerne i Sodoma, sammen omkring Huset, både gamle og unge, alle uden Undtagelse,
5 Suka kira Lot, suka ce, “Ina mutanen da suka zo wurinka a daren nan? Fito mana da su waje domin mu kwana da su.”
og de råbte til Lot: "Hvor er de Mænd, der kom til dig i Nat Kom herud med dem, for at vi kan stille vor Lyst på dem!"
6 Lot ya fita daga cikin gida, ya rufe ƙofar a bayansa. Ya je wurin mutanen
Da gik Lot ud til dem i Porten, men Døren lukkede han efter sig.
7 ya ce musu, “A’a, abokaina kada ku yi wannan mummunan abu.
Og han sagde: "Gør dog ikke noget ondt, mine Brødre!
8 Duba, ina da’ya’ya mata biyu waɗanda ba su taɓa sanin namiji ba, bari in kawo muku su ku yi kome da kuke so da su. Amma kada ku taɓa waɗannan mutane, gama su baƙina ne kuma dole in tsare su.”
Se, jeg har to Døtre, der ikke har kendt Mand; dem vil jeg bringe ud til eder, og med dem kan I gøre, hvad I lyster; men disse Mænd må I ikke gøre noget, siden de nu engang er kommet ind under mit Tags Skygge!"
9 Sai mutanen birnin suka amsa, “Ba mu wuri! Wannan mutum ya zo nan kamar baƙo, ga shi yanzu yana so yă zama alƙali! Za mu wulaƙanta ka fiye da su.” Suka ci gaba da matsa wa Lot lamba, suka matsa kusa domin su fasa ƙofar.
Men de sagde: "Bort med dig! Her er den ene Mand kommet og bor som fremmed, og nu vil han spille Dommer! Kom, lad os handle værre med ham end med dem!" Og de trængte ind på Manden, på Lot, og nærmede sig Døren for at sprænge den.
10 Amma mutanen da suke ciki suka miƙa hannunsu, suka ja Lot zuwa cikin gida, suka rufe ƙofar.
Da rakte Mændene Hånden ud og trak Lot ind til sig og lukkede Døren;
11 Sai suka bugi mutanen da suke a bakin ƙofar gidan da makanta, ƙanana da manya duka, har suka gajiyar da kansu, suna lalluba inda ƙofar take.
men Mændene uden for Porten til Huset slog de med Blindhed, både store og små, så de forgæves søgte at finde Porten.
12 Mutanen nan biyun suka ce wa Lot, “Kana da wani a nan, ko surukai, ko’ya’ya maza ko mata, ko kuwa wani dai a cikin birni wanda yake naka? Ka fitar da su daga nan,
Derpå sagde Mændene til Lot: "Hvem der ellers hører dig til her, dine Svigersønner, dine Sønner og Døtre, alle, som hører dig til i Byen, må du føre bort fra dette Sted;
13 gama za mu hallaka wannan wuri. Kukan da aka yi ga Ubangiji game da mutanen birnin nan ya yi yawa sosai, ya sa har ya aiko mu domin mu hallaka birnin.”
thi vi står i Begreb med at ødelægge Stedet her, fordi Skriget over dem er blevet så stort for HERREN, at HERREN har sendt os for at ødelægge dem."
14 Saboda haka Lot ya tafi ya yi magana da surukansa waɗanda suka yi alkawari za su aure’ya’yansa mata. Ya ce, “Ku yi sauri ku fita daga wannan wuri, gama Ubangiji yana gab da hallaka birnin.” Amma surukansa suka ɗauka wasa yake yi.
Da gik Lot ud og sagde til sine Svigersønner, der skulde ægte hans Døtre: "Stå op, gå bort herfra, thi HERREN vil ødelægge Byen!" Men hans Svigersønner troede, at han drev Spøg med dem.
15 Gari na wayewa, sai mala’ikun nan suka ƙarfafa Lot suna cewa, “Yi sauri! Ka ɗauki matarka da’ya’yanka biyu mata waɗanda suke a nan, don kada a shafe ku sa’ad da ake hukunta birnin.”
Da Morgenen så gryede, skyndede Englene på Lot og sagde: "Tag din Hustru og dine to Døtre, som bor hos dig, og drag bort, for at du ikke skal rives bort ved Byens Syndeslkyld!"
16 Da yana jan jiki, sai mutanen suka kama hannunsa da hannuwan matarsa da na’ya’yansa biyu mata, suka kai su bayan birni, gama Ubangiji ya nuna musu jinƙai.
Og da han tøvede, greb Mændene ham, hans Hustru og hans to Døtre ved Hånden, thi HERREN vilde skåne ham, og de førte ham bort og bragte ham i Sikkerhed uden for Byen.
17 Da suka fitar da su, sai ɗaya daga cikin mala’ikun ya ce, “Ku gudu domin ranku; kada ku duba baya, kada kuma ku tsaya ko’ina cikin kwarin! Ku gudu zuwa cikin duwatsu, don kada a hallaka ku!”
Og idet de førte dem uden for Byen, sagde de: "Det gælder dit Liv! Se dig ikke tilbage og stands ikke nogensteds i Jordanegnen, men red dig op i Bjergene, for at du ikke skal omkomme!"
18 Amma Lot ya ce musu, “A’a, ranka yă daɗe, ka yi haƙuri!
Men Lot sagde til dem: "Ak nej, Herre!
19 Bawanku ya riga ya sami tagomashi daga gare ku, kun kuma nuna mini alheri mai yawa. Ba zan iya in gudu zuwa duwatsu ba, wannan masifa za tă same ni, zan kuma mutu.
Din Træl har jo fundet Nåde for dine Øjne, og du har vist mig stor Godhed og frelst mit Liv; men jeg kan ikke nå op i Bjergene og undfly Ulykken; den indhenter mig så jeg mister Livet.
20 Ga ɗan gari can ya fi kusa inda zan gudu in fake. Bari in gudu zuwa can, in tsirar da raina.”
Se, den By der er nær nok til at jeg kan flygte derhen; den betyder jo ikke stort, lad mig redde mig derhen, den betyder jo ikke stort, og mit Liv er frelst!"
21 Sai ya ce masa, “Na yarda da abin da ka ce, ba zan hallakar da garin da ka ambata ba.
Da svarede han: "Også i det Stykke har jeg bønhørt dig; jeg vil ikke ødelægge den By, du nævner;
22 Gaggauta, ka gudu zuwa can, ba zan yi kome ba sai ka isa can.” (Domin haka ne ake kira garin Zowar.)
men red dig hurtigt derhen, thi jeg kan intet gøre, før du når derhen!" Derfor kaldte man Byen Zoar.
23 A lokacin da Lot ya isa Zowar, rana ta hau.
Da Solen steg op over Landet og Lot var nået til Zoar,
24 Sai Ubangiji ya yi ta zuba kibiritu a bisa Sodom da Gomorra daga sama.
lod HERREN Svovl og Ild regne over Sodoma og Gomorra fra HERREN, fra Himmelen;
25 Haka ya hallakar da waɗannan birane da kuma kwarinsu gaba ɗaya, haɗe da dukan waɗanda suke zama a biranen, da kuma dukan shuke-shuke da suke cikin ƙasar.
og han ødelagde disse Byer og hele Jordanegnen og alle Byernes Indbyggere og Landets Afgrøde.
26 Amma matar Lot ta waiwaya baya, ta kuma zama ginshiƙin gishiri.
Men hans Hustru, som gik efter ham, så sig tilbage og blev til en Saltstøtte.
27 Da sassafe kashegari, Ibrahim ya tashi ya koma wurin da dā ya tsaya a gaban Ubangiji.
Næste Morgen, da Abraham gik hen til det Sted, hvor han havde stået hos HERREN,
28 Ya duba ta wajen Sodom da Gomorra, da wajen dukan filayen ƙasar, sai ya ga hayaƙi baƙin ƙirin yana tashi daga ƙasar kamar hayaƙi daga matoya.
og vendte sit Blik mod Sodoma og Gomorra og hele Jordanegnen. så han Røg stige til Vejrs fra Landet som Røgen fra en Smelteovn.
29 Saboda haka sa’ad da Allah ya hallaka waɗannan biranen kwarin, ya tuna da Ibrahim, ya kuma fitar da Lot daga masifar da ta hallaka biranen da Lot ya zauna.
Da Gud tilintetgjorde Jordanegnens Byer, kom han Abraham i Hu og førte Lot ud af Ødelæggelsen, som han lod komme over de Byer, Lot boede i.
30 Lot da’ya’yansa biyu mata suka bar Zowar suka kuma zauna a cikin duwatsu, gama ya ji tsoro yă zauna a Zowar. Shi da’ya’yansa biyu mata suka zauna a ciki wani kogo.
Men Lot drog op fra Zoar og slog sig ned i Bjergene med sine Døtre, thi han turde ikke blive i Zoar; og han boede i en Hule med sine to Døtre.
31 Wata rana’yarsa babba ta ce wa ƙanuwarta, “Mahaifinmu ya tsufa, kuma babu wani mutum kusa a nan da zai yi mana ciki mu haifi’ya’ya; yadda al’ada take a ko’ina a duniya.
Da sagde den ældste til den yngste: "Vor Fader er gammel, og der findes ingen Mænd her i Landet, som kunde komme til os på vanlig Vis.
32 Bari mu sa mahaifinmu yă sha ruwan inabi, sa’an nan sai mu kwana da shi, don kada zuriyar mahaifinmu ta ƙare.”
Kom, lad os give vor Fader Vin at drikke og ligge hos ham for at få Afkom ved vor Fader!"
33 A wannan dare, suka sa mahaifinsu ya sha ruwan inabi,’yar farin ta shiga ta kwana da shi. Shi kuwa bai san sa’ad da ta kwanta ko sa’ad da ta tashi ba.
De gav ham da Vin at drikke samme Nat; og den ældste lagde sig hos sin Fader, og han sansede hverken, at hun lagde sig, eller at hun stod op.
34 Kashegari,’yar farin ta ce wa ƙanuwar, “Jiya da dare na kwana da mahaifina. Bari mu sa yă sha ruwan inabi kuma yau da dare, ke ma ki shiga ki kwana da shi, domin kada zuriyar mahaifinmu ta ƙare.”
Næste Dag sagde den ældste til den yngste: "Jeg lå i Går Nat hos min Fader; nu vil vi også give ham Vin at drikke i Nat, og gå du så ind og læg dig hos ham, for at vi kan få Afkom ved vor Fader!"
35 Sai suka sa mahaifinsu ya sha ruwan inabi, a wannan dare ma, ƙanuwar ta shiga ta kwana da shi. Bai kuwa san sa’ad da ta kwanta ko sa’ad da ta tashi ba.
Så gav de atter den Nat deres Fader Vin at drikke, og den yngste lagde sig hos ham, og han sansede hverken, at hun lagde sig, eller at hun stod op.
36 Ta haka’ya’yan Lot biyu mata duk suka yi ciki daga mahaifinsu.
Således blev begge Lots Døtre frugtsommelige ved deres Fader;
37 ’Yar farin ta haifi ɗa, ta kuma ba shi suna Mowab, shi ne mahaifin Mowabawa a yau.
og den ældste fødte en Søn, som hun kaldte Moab; han er Moabs Stamfader den Dag i Dag.
38 ’Yar ƙaramar ma ta haifi ɗa, ta kuwa ba shi suna Ben-Ammi, shi ne mahaifin Ammonawa a yau.
Ligeså fødte den yngste en Søn, som hun kaldte Ben Ammi; han er Ammoniternes Stamfader den Dag i Dag.

< Farawa 19 >