< Farawa 18 >
1 Ubangiji ya bayyana ga Ibrahim kusa da manyan itatuwan Mamre yayinda yake zaune a mashigin tentinsa da tsakar rana.
После му се јави Господ у равници мамријској кад сеђаше на вратима пред шатором својим у подне.
2 Da Ibrahim ya ɗaga ido, sai ya ga mutum uku suna tsaye kusa da shi. Sa’ad da ya gan su, sai ya tashi nan da nan daga mashigin tentinsa, ya tarye su, ya rusuna har ƙasa.
Подигавши очи своје погледа, и гле, три човека стајаху према њему. И угледавши их потрча им у сусрет испред врата шатора свог, и поклони се до земље;
3 Ya ce, “Ranka yă daɗe, in na sami tagomashi daga gare ku kada ku wuce bawanku.
И рече: Господе, ако сам нашао милост пред Тобом, немој проћи слуге свог.
4 Bari a kawo ruwa ku wanke ƙafafunku, ku huta a ƙarƙashin wannan itace.
Да вам донесем мало воде и оперите ноге, те се наслоните мало под овим дрветом.
5 Bari in samo muku wani abu ku ci don ku wartsake, sa’an nan ku ci gaba da tafiyarku; da yake kun biyo wurin bawanku.” Suka ce, “To, sai ka yi abin da ka ce.”
И изнећу мало хлеба, те поткрепите срце своје, па онда пођите, кад идете поред слуге свог. И рекоше: Учини шта си казао.
6 Saboda haka Ibrahim ya ruga zuwa wurin Saratu a cikin tenti ya ce, “Yi sauri, ki shirya mudu uku na gari mai laushi, ki cuɗa shi, ki yi burodi.”
И Аврам отрча у шатор к Сари, и рече: Брже замеси три копање белог брашна и испеци погаче.
7 Sa’an nan Ibrahim ya yi gudu zuwa garkensa, ya zaɓi ɗan maraƙi ya ba wa bawansa, bawansa kuma ya yi sauri ya gyara shi.
Па отрча ка говедима и ухвати теле младо и добро, и даде га момку да га брже зготови.
8 Sa’an nan Ibrahim ya ɗauko dambu da madara da naman ɗan maraƙin da aka gyara, ya kawo a gabansu. Yayinda suke ci, ya tsaya a gindin itace kusa da su.
Па онда изнесе масла и млека и теле које беше зготовио, и постави им, а сам стајаше пред њима под дрветом докле јеђаху.
9 Sai suka ce masa, “Ina Saratu matarka?” Ibrahim ya ce, “Tana can cikin tenti.”
И они му рекоше: Где је Сара жена твоја? А он рече: Ено је под шатором.
10 Sa’an nan ɗayansu ya ce, “Lalle zan komo wurinka war haka shekara mai zuwa. Saratu matarka kuwa za tă haifi ɗa.” Saratu kuwa tana a bayansu tana ji daga mashigin tenti.
А један између њих рече: Догодине у ово доба опет ћу доћи к теби, а Сара ће жена твоја имати сина. А Сара слушаше на вратима од шатора иза њега.
11 Ibrahim da Saratu dai sun riga sun tsufa sosai. Saratu kuma ta wuce shekarun haihuwa.
А Аврам и Сара беху стари и временити, и у Саре беше престало шта бива у жена.
12 Saboda haka Saratu ta yi dariya da ta yi tunani a zuci tana cewa, “Bayan ƙarfina ya ƙare, maigidana kuma ya tsufa, yanzu zan sami wannan jin daɗi?”
Зато се насмеја Сара у себи говорећи: Пошто сам остарела, сад ли ће ми доћи радост? А и господар ми је стар.
13 Sai Ubangiji ya ce wa Ibrahim, “Me ya ba Saratu dariya har da ta ce, ‘Har zan iya haifi ɗa duk ta tsufata yanzu?’
Тада рече Господ Авраму: Што се смеје Сара говорећи: Истина ли је да ћу родити кад сам остарела?
14 Akwai abin zai gagari Ubangiji? Zan komo wurinka a ƙayyadadden lokacin nan shekara mai zuwa kuma Saratu za tă haifi ɗa.”
Има ли шта тешко Господу? Догодине у ово доба опет ћу доћи к теби, а Сара ће имати сина.
15 Saratu ta ji tsoro, don haka sai ta yi ƙarya ta ce, “Ban yi dariya ba.” Ya ce, “A’a, kin yi dariya.”
А Сара удари у бах говорећи: Нисам се смејала. Јер се уплаши. Али Он рече: Није истина, него си се смејала.
16 Sai mutanen suka tashi suka nufi Sodom, Ibrahim kuwa ya yi musu rakiya, ya yi bankwana da su.
Потом усташе људи оданде, и пођоше пут Содома; а Аврам пође с њима да их испрати.
17 Sai Ubangiji ya ce, “Zan ɓoye wa Ibrahim abin da nake shirin yi?
А Господ рече: Како бих тајио од Аврама шта ћу учинити,
18 Lalle Ibrahim zai zama al’umma mai girma da kuma mai iko, kuma ta wurinsa dukan al’umman duniya za su sami albarka.
Кад ће од Аврама постати велик и силан народ, и у њему ће се благословити сви народи на земљи?
19 Saboda na zaɓe shi don yă umarci’ya’yansa da iyalinsa a bayansa su kiyaye hanyoyin Ubangiji, ta wurin yin abin da yake daidai da kuma yin adalci, domin Ubangiji ya aikata abin da ya yi wa Ibrahim alkawari.”
Јер знам да ће заповедити синовима својим и дому свом након себе да се држе путева Господњих и да чине што је право и добро, да би Господ навршио на Авраму шта му је обећао.
20 Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Kuka a kan Sodom da Gomorra ta yi yawa, zunubinsu kuma ya yi muni sosai,
И рече Господ: Вика је у Содому и Гомору велика, и грех је њихов грдан.
21 zan gangara in ga ko abin da suka yi ya yi muni kamar yadda kukan ya zo gare ni, zan bincike.”
Зато ћу сићи да видим еда ли све чине као што вика дође преда ме; ако ли није тако, да знам.
22 Sai mutanen suka juya suka nufi wajen Sodom amma Ibrahim ya ci gaba da kasance a gaban Ubangiji.
И људи окренувши се пођоше пут Содома; али Аврам још стајаше пред Господом,
23 Sai Ibrahim ya matso wurinsa ya ce, “Za ka hallaka masu adalci tare da masu mugunta?
И приступив Аврам рече: Хоћеш ли погубити и праведног с неправедним?
24 Me zai faru in akwai mutum hamshin masu adalci a cikin birnin? Ashe, za ka hallaka shi, ba za ka cece wurin saboda mutane hamsin nan masu adalcin da suke a cikinsa ba?
Може бити да има педесет праведника у граду; хоћеш ли и њих погубити, и нећеш опростити месту за оних педесет праведника што су у њему?
25 Tabbatacce ba za ka taɓa aikata irin wannan abu ba, ka kashe masu adalci tare da masu mugunta, ka ɗauka masu adalci da masu mugunta daidai? Tabbatacce ba za ka taɓa aikata irin wannan abu ba! Mai hukuncin dukan duniya ba zai aikata gaskiya ba?”
Немој то чинити, ни губити праведника с неправедником, да буде праведнику као и неправеднику; немој; еда ли судија целе земље неће судити право?
26 Ubangiji ce, “In na sami mutum hamshin masu adalci a cikin birnin Sodom, zan bar dukan birnin saboda su.”
И рече Господ: Ако нађем у Содому педесет праведника у граду, опростићу целом месту њих ради.
27 Sai Ibrahim ya ƙara cewa, “Yanzu da na yi karambani har na yi magana da Ubangiji, ko da yake ni ba kome ba ne illa turɓaya da toka,
А Аврам одговори и рече: Гле, сада бих проговорио Господу, ако и јесам прах и пепео.
28 in yawan masu adalci sun kāsa hamshin da mutum biyar fa? Za ka hallaka dukan birnin saboda rashin mutum biyar ɗin?” Ya ce, “In na sami mutum arba’in da biyar a wurin, ba zan hallaka shi ba.”
Може бити праведника педесет мање пет, хоћеш ли за оних пет потрти сав град? Одговори: Нећу, ако нађем четрдесет и пет.
29 Ya sāke cewa, “In mutum arba’in kaɗai aka samu a can fa?” Ya ce, “Saboda mutum arba’in ɗin, ba zan aikata ba.”
И стаде даље говорити, и рече: Може бити да ће се наћи четрдесет. Рече: Нећу ради оних четрдесет.
30 Sai ya ce, “Kada Ubangiji ya yi fushi, amma bari in ƙara magana. A ce mutum talatin kaɗai aka samu a can fa?” Ya ce, “Ba zan aikata ba, in na sami mutum talatin a can.”
Потом рече: Немој се гневити, Господе, што ћу рећи; може бити да ће се наћи тридесет. И рече: Нећу, ако нађем тридесет.
31 Ibrahim ya ce, “Yanzu fa da na yi karambani har na yi magana da Ubangiji, in ashirin kaɗai aka samu a can fa?” Ya ce, “Saboda ashirin ɗin, ba zan hallaka shi ba.”
Опет рече: Гле сада бих проговорио Господу; може бити да ће се наћи двадесет. Рече: Нећу их погубити за оних двадесет.
32 Sa’an nan Ibrahim ya ce, “Kada Ubangiji yă yi fushi, amma bari in ƙara magana sau ɗaya tak. In aka sami mutum goma kaɗai a can fa?” Ubangiji ya ce, “Saboda goma nan, ba zan hallaka shi ba.”
Најпосле рече: Немој се гневити, Господе, што ћу још једном проговорити; може бити да ће се наћи десет. Рече: Нећу их погубити ради оних десет.
33 Sa’ad da Ubangiji ya gama magana da Ibrahim, ya tafi, Ibrahim kuma ya koma gida.
И Господ отиде свршивши разговор са Аврамом; а Аврам се врати на своје место.