< Farawa 18 >
1 Ubangiji ya bayyana ga Ibrahim kusa da manyan itatuwan Mamre yayinda yake zaune a mashigin tentinsa da tsakar rana.
And Yahweh appeared unto him among the oaks of Mamre, —as, he, was sitting at the opening of the tent in the heat of the day.
2 Da Ibrahim ya ɗaga ido, sai ya ga mutum uku suna tsaye kusa da shi. Sa’ad da ya gan su, sai ya tashi nan da nan daga mashigin tentinsa, ya tarye su, ya rusuna har ƙasa.
And he lifted up his eyes and looked, and lo! three men, standing over against him, —so he looked and ran to meet them from the opening of the tent, and bowed himself to the earth;
3 Ya ce, “Ranka yă daɗe, in na sami tagomashi daga gare ku kada ku wuce bawanku.
and said, —O My Lord! if, I pray thee, I have found favour in thine eyes, do not I pray thee pass on from thy servant.
4 Bari a kawo ruwa ku wanke ƙafafunku, ku huta a ƙarƙashin wannan itace.
Let there be fetched, I pray thee a little water, and bathe ye your feet, —and rest yourselves under the tree.
5 Bari in samo muku wani abu ku ci don ku wartsake, sa’an nan ku ci gaba da tafiyarku; da yake kun biyo wurin bawanku.” Suka ce, “To, sai ka yi abin da ka ce.”
And let me fetch a morsel of bread, and stay ye your heart, Afterwards, ye may pass on, For on this account, have ye passed by, over against your servant. And they said, Thus, shalt thou do as thou hast spoken.
6 Saboda haka Ibrahim ya ruga zuwa wurin Saratu a cikin tenti ya ce, “Yi sauri, ki shirya mudu uku na gari mai laushi, ki cuɗa shi, ki yi burodi.”
So Abraham hastened towards the tent unto Sarah, —and said, Hasten thou three measures of fine meal, knead it, and make hearth-cakes.
7 Sa’an nan Ibrahim ya yi gudu zuwa garkensa, ya zaɓi ɗan maraƙi ya ba wa bawansa, bawansa kuma ya yi sauri ya gyara shi.
And unto the herd, ran Abraham, —and took a calf tender and good and gave unto the young man, and he hastened to make it ready.
8 Sa’an nan Ibrahim ya ɗauko dambu da madara da naman ɗan maraƙin da aka gyara, ya kawo a gabansu. Yayinda suke ci, ya tsaya a gindin itace kusa da su.
And he took butter and milk and the calf that he had made ready, and set before them, —while, he, was standing near them under the tree, they did eat.
9 Sai suka ce masa, “Ina Saratu matarka?” Ibrahim ya ce, “Tana can cikin tenti.”
And they said unto him, As to Sarah thy wife… And he said Lo! [she is] in the tent.
10 Sa’an nan ɗayansu ya ce, “Lalle zan komo wurinka war haka shekara mai zuwa. Saratu matarka kuwa za tă haifi ɗa.” Saratu kuwa tana a bayansu tana ji daga mashigin tenti.
And he said, I will, surely return, unto thee at the quickening season, —and lo! a son for Sarah thy wife. Now Sarah, was hearkening at the opening of the tent, it, being behind him.
11 Ibrahim da Saratu dai sun riga sun tsufa sosai. Saratu kuma ta wuce shekarun haihuwa.
But Abraham and Sarah, were old, far gone in days, —it had ceased to be with Sarah after the manner of women.
12 Saboda haka Saratu ta yi dariya da ta yi tunani a zuci tana cewa, “Bayan ƙarfina ya ƙare, maigidana kuma ya tsufa, yanzu zan sami wannan jin daɗi?”
So then Sarah laughed within herself, saying: After I am past age, hath there come to me pleasure, my lord, also being old?
13 Sai Ubangiji ya ce wa Ibrahim, “Me ya ba Saratu dariya har da ta ce, ‘Har zan iya haifi ɗa duk ta tsufata yanzu?’
And Yahweh said unto Abraham, —Wherefore now did Sarah laugh saying. Can it really and truly be that I should bear, seeing that I have become old?
14 Akwai abin zai gagari Ubangiji? Zan komo wurinka a ƙayyadadden lokacin nan shekara mai zuwa kuma Saratu za tă haifi ɗa.”
Is anything, too wonderful for Yahweh? At the appointed time, I will return unto thee, at the quickening season and Sarah, shall have a son.
15 Saratu ta ji tsoro, don haka sai ta yi ƙarya ta ce, “Ban yi dariya ba.” Ya ce, “A’a, kin yi dariya.”
And Sarah denied, saying, I laughed not, For she was afraid. And he said—Nay! but thou didst laugh!
16 Sai mutanen suka tashi suka nufi Sodom, Ibrahim kuwa ya yi musu rakiya, ya yi bankwana da su.
And the men rose up from thence, and looked out over the face of Sodom, —Abraham also going with them to set them on their way.
17 Sai Ubangiji ya ce, “Zan ɓoye wa Ibrahim abin da nake shirin yi?
Now, Yahweh, had said, —Am I going to hide from Abraham what I do,
18 Lalle Ibrahim zai zama al’umma mai girma da kuma mai iko, kuma ta wurinsa dukan al’umman duniya za su sami albarka.
when, Abraham, shall surely become, a great and mighty nation, —and all the nations of the earth, shall be blessed in him?
19 Saboda na zaɓe shi don yă umarci’ya’yansa da iyalinsa a bayansa su kiyaye hanyoyin Ubangiji, ta wurin yin abin da yake daidai da kuma yin adalci, domin Ubangiji ya aikata abin da ya yi wa Ibrahim alkawari.”
For I have become his intimate friend, To the end that he may command his sons and his house after him, so shall they keep the way of Yahweh, by doing righteousness and justice. To the end that Yahweh may bring in for Abraham, what he hath spoken concerning him.
20 Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Kuka a kan Sodom da Gomorra ta yi yawa, zunubinsu kuma ya yi muni sosai,
So Yahweh said, The outcry of Sodom and Gomorrah, because it hath become great, —And their sin, because it hath become exceeding grievous,
21 zan gangara in ga ko abin da suka yi ya yi muni kamar yadda kukan ya zo gare ni, zan bincike.”
Let me go down, pray, and let me behold, whether according to their outcry which hath come in unto me, they have done altogether, And if not. I must know!
22 Sai mutanen suka juya suka nufi wajen Sodom amma Ibrahim ya ci gaba da kasance a gaban Ubangiji.
And the men turned from thence, and went their way, towards Sodom, —but, Yahweh was yet standing before Abraham.
23 Sai Ibrahim ya matso wurinsa ya ce, “Za ka hallaka masu adalci tare da masu mugunta?
So then Abraham drew near and said, Wilt thou really sweep away, the righteous with the lawless?
24 Me zai faru in akwai mutum hamshin masu adalci a cikin birnin? Ashe, za ka hallaka shi, ba za ka cece wurin saboda mutane hamsin nan masu adalcin da suke a cikinsa ba?
Peradventure there are fifty righteous, in the midst of the city, Wilt thou really sweep away, and not spare the place, for the sake of the fifty righteous which are therein?
25 Tabbatacce ba za ka taɓa aikata irin wannan abu ba, ka kashe masu adalci tare da masu mugunta, ka ɗauka masu adalci da masu mugunta daidai? Tabbatacce ba za ka taɓa aikata irin wannan abu ba! Mai hukuncin dukan duniya ba zai aikata gaskiya ba?”
Far be it from thee! to do after this manner. to put to death the righteous with the lawless! Then should righteous and lawless be alike, Far be it from thee! Shall, the Judge of all the earth not do justice?
26 Ubangiji ce, “In na sami mutum hamshin masu adalci a cikin birnin Sodom, zan bar dukan birnin saboda su.”
And Yahweh said, If I find in Sodom fifty righteous in the midst of the city, then will I spare all the place for their sake.
27 Sai Ibrahim ya ƙara cewa, “Yanzu da na yi karambani har na yi magana da Ubangiji, ko da yake ni ba kome ba ne illa turɓaya da toka,
And Abraham responded and said, —Behold I pray thee I have ventured to speak unto My Lord, though I am dust and ashes:
28 in yawan masu adalci sun kāsa hamshin da mutum biyar fa? Za ka hallaka dukan birnin saboda rashin mutum biyar ɗin?” Ya ce, “In na sami mutum arba’in da biyar a wurin, ba zan hallaka shi ba.”
Peradventure there may lack, of the fifty righteous, five, Wilt thou destroy for five all the city? And he said, I will not destroy, if I find there forty and five.
29 Ya sāke cewa, “In mutum arba’in kaɗai aka samu a can fa?” Ya ce, “Saboda mutum arba’in ɗin, ba zan aikata ba.”
And he added, yet once more, to speak unto him, and said, Peradventure there may be found there—forty. And he said—I will not do it, for the sake of the forty.
30 Sai ya ce, “Kada Ubangiji ya yi fushi, amma bari in ƙara magana. A ce mutum talatin kaɗai aka samu a can fa?” Ya ce, “Ba zan aikata ba, in na sami mutum talatin a can.”
And he said Let it not, I pray thee, be vexing to My Lord, but let me speak, Peradventure there may be found there—thirty And he said, I will not to it, if I find there—thirty.
31 Ibrahim ya ce, “Yanzu fa da na yi karambani har na yi magana da Ubangiji, in ashirin kaɗai aka samu a can fa?” Ya ce, “Saboda ashirin ɗin, ba zan hallaka shi ba.”
And he said Behold, I pray thee, I have ventured to speak unto My Lord, Peradventure there may be found there—twenty. And he said I will not destroy it, for the sake of the twenty.
32 Sa’an nan Ibrahim ya ce, “Kada Ubangiji yă yi fushi, amma bari in ƙara magana sau ɗaya tak. In aka sami mutum goma kaɗai a can fa?” Ubangiji ya ce, “Saboda goma nan, ba zan hallaka shi ba.”
And he said, Let it not, I pray thee, be vexing to My Lord, but let me speak only this once, Peradventure there may be found there—ten. And he said, I will not destroy [it], for the sake of the ten!
33 Sa’ad da Ubangiji ya gama magana da Ibrahim, ya tafi, Ibrahim kuma ya koma gida.
And Yahweh went his way, when he had made an end. of speaking unto Abraham, —Abraham, also returned to his place.