< Farawa 18 >

1 Ubangiji ya bayyana ga Ibrahim kusa da manyan itatuwan Mamre yayinda yake zaune a mashigin tentinsa da tsakar rana.
Og Herren aabenbaredes for ham i Mamre Lund, og han sad i sit Telts Dør, der Dagen var hed.
2 Da Ibrahim ya ɗaga ido, sai ya ga mutum uku suna tsaye kusa da shi. Sa’ad da ya gan su, sai ya tashi nan da nan daga mashigin tentinsa, ya tarye su, ya rusuna har ƙasa.
Og han opløftede sine Øjne og saa, og se, tre Mænd stode for ham; og der han saa dem, løb han dem i Møde fra Teltets Dør og bøjede sig til Jorden.
3 Ya ce, “Ranka yă daɗe, in na sami tagomashi daga gare ku kada ku wuce bawanku.
Og han sagde: Min Herre! Kære, dersom jeg har fundet Naade for dine Øjne, da gak ikke din Tjener forbi!
4 Bari a kawo ruwa ku wanke ƙafafunku, ku huta a ƙarƙashin wannan itace.
Kære, lad hente lidt Vand, og toer eders Fødder, og hviler eder under Træet!
5 Bari in samo muku wani abu ku ci don ku wartsake, sa’an nan ku ci gaba da tafiyarku; da yake kun biyo wurin bawanku.” Suka ce, “To, sai ka yi abin da ka ce.”
Og jeg vil hente en Mundfuld Brød, og vederkvæger eders Hjerte, siden kunne I gaa længere; thi derfor gik I forbi eders Tjener; og de sagde: Gør saaledes, som du har sagt.
6 Saboda haka Ibrahim ya ruga zuwa wurin Saratu a cikin tenti ya ce, “Yi sauri, ki shirya mudu uku na gari mai laushi, ki cuɗa shi, ki yi burodi.”
Og Abraham skyndte sig til Teltet, til Sara, og sagde: Tag hastig tre Maader Hvedemel, ælt og bag Kager!
7 Sa’an nan Ibrahim ya yi gudu zuwa garkensa, ya zaɓi ɗan maraƙi ya ba wa bawansa, bawansa kuma ya yi sauri ya gyara shi.
Og Abraham løb til Kvæget og hentede en blød og god Kalv, og han gav Drengen den, og han skyndte sig at tilberede den.
8 Sa’an nan Ibrahim ya ɗauko dambu da madara da naman ɗan maraƙin da aka gyara, ya kawo a gabansu. Yayinda suke ci, ya tsaya a gindin itace kusa da su.
Og han tog Fløde og Mælk og Kalven, som han havde ladet tilberede, og satte for dem, og han stod hos dem under Træet, og de aade.
9 Sai suka ce masa, “Ina Saratu matarka?” Ibrahim ya ce, “Tana can cikin tenti.”
Og de sagde til ham: Hvor er Sara, din Hustru? og han svarede: Se, i Teltet.
10 Sa’an nan ɗayansu ya ce, “Lalle zan komo wurinka war haka shekara mai zuwa. Saratu matarka kuwa za tă haifi ɗa.” Saratu kuwa tana a bayansu tana ji daga mashigin tenti.
Og han sagde: Jeg vil visseligen komme til dig igen ved denne Aarsens Tid, og se, Sara, din Hustru, skal have en Søn; og Sara hørte det i Teltets Dør, og den var bag ham.
11 Ibrahim da Saratu dai sun riga sun tsufa sosai. Saratu kuma ta wuce shekarun haihuwa.
Og Abraham og Sara vare gamle, vel ved Alder, det gik ikke mere Sara efter Kvinders Vis.
12 Saboda haka Saratu ta yi dariya da ta yi tunani a zuci tana cewa, “Bayan ƙarfina ya ƙare, maigidana kuma ya tsufa, yanzu zan sami wannan jin daɗi?”
Og Sara lo ved sig selv og sagde: Skulde jeg lade mig lyste, efter at jeg er bleven gammel, og min Herre er gammel!
13 Sai Ubangiji ya ce wa Ibrahim, “Me ya ba Saratu dariya har da ta ce, ‘Har zan iya haifi ɗa duk ta tsufata yanzu?’
Da sagde Herren til, Abraham: Hvorfor lo Sara og sagde: monne jeg og visseligen skal føde, og jeg er gammel!
14 Akwai abin zai gagari Ubangiji? Zan komo wurinka a ƙayyadadden lokacin nan shekara mai zuwa kuma Saratu za tă haifi ɗa.”
Skulde nogen Ting være underlig for Herren? til den bestemte Tid vil jeg komme til dig igen, ved denne Aarsens Tid, og Sara skal have en Søn.
15 Saratu ta ji tsoro, don haka sai ta yi ƙarya ta ce, “Ban yi dariya ba.” Ya ce, “A’a, kin yi dariya.”
Og Sara nægtede og sagde: Jeg lo ikke; thi hun frygtede; men han sagde: Nej, thi du lo.
16 Sai mutanen suka tashi suka nufi Sodom, Ibrahim kuwa ya yi musu rakiya, ya yi bankwana da su.
Saa stode Mændene op derfra og vendte sig imod Sodoma, og Abraham gik med dem for at ledsage dem.
17 Sai Ubangiji ya ce, “Zan ɓoye wa Ibrahim abin da nake shirin yi?
Da sagde Herren: Skulde jeg dølge for Abraham det, jeg gør?
18 Lalle Ibrahim zai zama al’umma mai girma da kuma mai iko, kuma ta wurinsa dukan al’umman duniya za su sami albarka.
efterdi Abraham skal visseligen vorde et stort og stærkt Folk, og alle Folk paa Jorden skulle velsignes i ham.
19 Saboda na zaɓe shi don yă umarci’ya’yansa da iyalinsa a bayansa su kiyaye hanyoyin Ubangiji, ta wurin yin abin da yake daidai da kuma yin adalci, domin Ubangiji ya aikata abin da ya yi wa Ibrahim alkawari.”
Thi jeg kender ham, at han skal byde sine Børn og sit Hus efter sig, at de skulle bevare Herrens Vej i at gøre Retfærdighed og Dom, paa det at Herren skal lade det komme over Abraham, som han har lovet ham.
20 Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Kuka a kan Sodom da Gomorra ta yi yawa, zunubinsu kuma ya yi muni sosai,
Og Herren sagde: Efterdi Skriget i Sodoma og Gomorra er stort, og efterdi deres Synd er meget svar,
21 zan gangara in ga ko abin da suka yi ya yi muni kamar yadda kukan ya zo gare ni, zan bincike.”
da vil jeg nu fare ned og se, om de have gjort ganske efter det Skrig, som er kommet for mig, eller hvis ikke, saa vil jeg vide det.
22 Sai mutanen suka juya suka nufi wajen Sodom amma Ibrahim ya ci gaba da kasance a gaban Ubangiji.
Og Mændene vendte deres Ansigt derfra og gik til Sodoma; men Abraham blev endnu staaende for Herrens Aasyn.
23 Sai Ibrahim ya matso wurinsa ya ce, “Za ka hallaka masu adalci tare da masu mugunta?
Og Abraham traadte frem og sagde: Vil du da ødelægge den retfærdige med den ugudelige?
24 Me zai faru in akwai mutum hamshin masu adalci a cikin birnin? Ashe, za ka hallaka shi, ba za ka cece wurin saboda mutane hamsin nan masu adalcin da suke a cikinsa ba?
Der maatte maaske være halvtredsindstyve retfærdige i Staden; vil du og ødelægge og ej spare det Sted for de halvtredsindstyve retfærdiges Skyld, som kunde være derinde?
25 Tabbatacce ba za ka taɓa aikata irin wannan abu ba, ka kashe masu adalci tare da masu mugunta, ka ɗauka masu adalci da masu mugunta daidai? Tabbatacce ba za ka taɓa aikata irin wannan abu ba! Mai hukuncin dukan duniya ba zai aikata gaskiya ba?”
Det være langt fra dig at gøre efter denne Vis, at ihjelslaa den retfærdige med den ugudelige, at den retfærdige skulde være ligesom den ugudelige, det være langt fra dig; den, som dømmer den ganske Jord, skulde han ikke gøre Ret?
26 Ubangiji ce, “In na sami mutum hamshin masu adalci a cikin birnin Sodom, zan bar dukan birnin saboda su.”
Da sagde Herren: Dersom jeg finder halvtredsindstyve retfærdige udi Sodoma Stad, da vil jeg spare hele Stedet for deres Skyld.
27 Sai Ibrahim ya ƙara cewa, “Yanzu da na yi karambani har na yi magana da Ubangiji, ko da yake ni ba kome ba ne illa turɓaya da toka,
Og Abraham svarede og sagde: Se nu, jeg har begyndt at tale til Herren, og jeg er Støv og Aske.
28 in yawan masu adalci sun kāsa hamshin da mutum biyar fa? Za ka hallaka dukan birnin saboda rashin mutum biyar ɗin?” Ya ce, “In na sami mutum arba’in da biyar a wurin, ba zan hallaka shi ba.”
Der maatte maaske fattes fem i de halvtredsindstyve retfærdige, vilde du ødelægge hele Staden for de fems Skyld? Og han sagde: Jeg vil ikke ødelægge den, om jeg finder fem og fyrretyve der.
29 Ya sāke cewa, “In mutum arba’in kaɗai aka samu a can fa?” Ya ce, “Saboda mutum arba’in ɗin, ba zan aikata ba.”
Og han blev endnu ved at tale til ham og sagde: Der maatte maaske findes fyrretyve; og han sagde: Jeg vil ikke gøre det for de fyrretyves Skyld.
30 Sai ya ce, “Kada Ubangiji ya yi fushi, amma bari in ƙara magana. A ce mutum talatin kaɗai aka samu a can fa?” Ya ce, “Ba zan aikata ba, in na sami mutum talatin a can.”
Og han sagde: Herren blive dog ikke vred, saa vil jeg tale: der kunde maaske findes tredive; og han sagde: Jeg vil ikke gøre det, om jeg finder tredive der.
31 Ibrahim ya ce, “Yanzu fa da na yi karambani har na yi magana da Ubangiji, in ashirin kaɗai aka samu a can fa?” Ya ce, “Saboda ashirin ɗin, ba zan hallaka shi ba.”
Og han sagde: Se nu, jeg har begyndt at tale til Herren, der maatte maaske findes tyve; og han sagde: Jeg vil ikke ødelægge den for de tyves Skyld.
32 Sa’an nan Ibrahim ya ce, “Kada Ubangiji yă yi fushi, amma bari in ƙara magana sau ɗaya tak. In aka sami mutum goma kaɗai a can fa?” Ubangiji ya ce, “Saboda goma nan, ba zan hallaka shi ba.”
Og han sagde: Herren blive dog ikke vred, saa vil jeg tale alene denne Gang: der maatte maaske findes ti; og han sagde: Jeg vil ikke ødelægge den for de tis Skyld.
33 Sa’ad da Ubangiji ya gama magana da Ibrahim, ya tafi, Ibrahim kuma ya koma gida.
Og Herren gik bort, der han havde udtalt med Abraham, og Abraham vendte om til sit Sted.

< Farawa 18 >