< Farawa 17 >

1 Sa’ad da Abram ya yi shekaru 99, sai Ubangiji ya bayyana a gare shi ya ce, ni “Ni ne Allah Maɗaukaki, ka yi tafiya a gabana ka kuma zama marar abin zargi.
Když pak Abram byl v devadesáti devíti letech, ukázal se mu Hospodin, a řekl jemu: Já jsem Bůh silný všemohoucí; chodiž ustavičně přede mnou a budiž dokonalým.
2 Zan tabbatar da alkawarina tsakanina da kai, zan kuma ƙara zuriyarka ta yi yawa.”
A učiním smlouvu svou mezi sebou a tebou a rozmnožím tě náramně velmi.
3 Abram ya rusuna da fuskarsa har ƙasa, Allah kuma ya ce masa,
Padl pak Abram na tvář svou; i mluvil Bůh s ním, řka:
4 “Gare ni kam, wannan shi ne alkawarina da kai, za ka zama mahaifin al’ummai masu yawa.
Jáť jsem, aj, smlouva má s tebou, a budeš otcem národů mnohých.
5 Ba za a ƙara kiranka Abram ba; sunanka zai zama Ibrahim, gama na mai da kai uban al’ummai masu yawa.
Aniž více slouti bude jméno tvé Abram, ale bude jméno tvé Abraham; nebo otcem mnohých národů učinil jsem tě.
6 Zan sa ka azurta sosai, zan yi al’ummai daga cikinka, sarakuna kuma za su fito daga cikinka,
A učiním, abys se rozplodil náramně velmi, a rozšířím tě v národy; i králové z tebe vyjdou.
7 zan kafa alkawarina kamar madawwamin alkawari tsakanina da kai da kuma zuriyarka bayanka har tsararraki masu zuwa, in zama Allahnka da kuma Allahn zuriyarka a bayanka.
Utvrdím také smlouvu svou mezi sebou a tebou, i mezi semenem tvým po tobě, po rodech jejich, za smlouvu věčnou, totiž abych byl Bohem tvým i semene tvého po tobě.
8 Dukan ƙasar Kan’ana inda kake baƙo a yanzu, zan ba da ita a matsayin madawwamiyar mallaka gare ka da kuma zuriyarka a bayanka, zan kuma zama Allahnsu.”
Nadto dám tobě i semeni tvému po tobě zemi, v nížto obýváš pohostinu, všecku zemi Kananejskou k vládařství věčnému; a budu jejich Bohem.
9 Sa’an nan Allah ya ce wa Ibrahim. “Kai fa, sai ka kiyaye alkawarina, kai da zuriyarka bayanka, har tsararraki masu zuwa.
Řekl ještě Bůh Abrahamovi: Ty pak ostříhati budeš smlouvy mé, ty i símě tvé po tobě, po rodech svých.
10 Wannan shi ne alkawarina da kai da kuma zuriyarka a bayanka, alkawarin da za ka kiyaye ke nan. Kowane namiji a cikinku kuwa za a yi masa kaciya.
Tatoť jest smlouva má mezi mnou a mezi vámi, i mezi semenem tvým po tobě, kteréž ostříhati budete: Aby obřezán byl mezi vámi každý pohlaví mužského.
11 Za ku yi kaciya, za tă kuma zama alamar alkawari tsakanina da kai.
Obřežete pak tělo hanby své; a to bude znamením smlouvy mezi mnou a mezi vámi.
12 Daga yanzu duk namijin da aka haifa a cikinku za a yi masa kaciya a rana ta takwas har dukan zamananku, ko haifaffen gida ne, ko sayayye da kuɗi daga kowane baƙo wanda ba na zuriyarku ba.
Každý tedy pohlaví mužského osmého dne obřezán bude mezi vámi po rodech vašich, doma narozený i koupený za stříbro, z kterých by koli cizozemců byl, jenž není z semene tvého.
13 Ko haifaffe a gidanka ko an sayo da kuɗi, dole a yi musu kaciya. Alkawarina cikin jikinku zai kasance madawwamin alkawari.
Konečně ať jest obřezán narozený v domě tvém, i koupený za peníze tvé; a budeť smlouva má na těle vašem za smlouvu věčnou.
14 Kowane namijin da ba a yi masa kaciya a jiki ba, za a fid da shi daga cikin mutanensa; domin ya karya alkawarina.”
Neobřezaný pak pacholík, kterýž by neobřezal těla neobřízky své, vyhlazena zajisté bude duše ta z lidu svého; nebo smlouvu mou zrušil.
15 Allah ya kuma ce wa Ibrahim, “Game da Saira matarka kuwa, ba za ka ƙara kiranta Saira ba, sunanta zai zama Saratu.
Řekl také Bůh Abrahamovi: Sarai manželce své nebudeš říkati Sarai, ale Sára bude jméno její.
16 Zan sa mata albarka, ban da haka ma, zan ba ka ɗa ta wurinta, zan sa mata albarka, za tă kuwa zama mahaifiyar al’ummai; sarakunan mutane za su fito daga gare ta.”
Nebo požehnám jí a dámť z ní syna; požehnámť jí, a bude v národy; králové národů z ní vyjdou.
17 Ibrahim ya rusuna da fuskarsa har ƙasa, ya yi dariya, ya ce wa kansa, “Za a haifi ɗa wa mutum mai shekaru ɗari? Saratu za tă haifi ɗa tana da shekaru tasa’in?”
Tedy padl Abraham na tvář svou, a zasmáv se, řekl v srdci svém: Zdali stoletému narodí se syn? A zdali Sára v devadesáti letech porodí?
18 Ibrahim ya kuma ce wa Allah, “Me zai hana a dai bar Ishmayel kawai yă gāji alkawarin nan da ka yi mini.”
I řekl Abraham Bohu: Ó byť jen Izmael živ byl před tebou!
19 Sai Allah ya ce, “Duk da haka dai, matarka Saratu za tă haifi maka ɗa; za ka kuma kira shi Ishaku. A kansa zan tabbatar da madawwamin alkawarina, da kuma ga zuriyarsa da za su zo bayansa.
Jemužto řekl Bůh: Nýbrž Sára manželka tvá porodí tobě syna, a nazůveš jméno jeho Izák; i utvrdím smlouvu svou s ním za smlouvu věčnou, i s semenem jeho po něm.
20 Game da Ishmayel kuwa, na ji ka. Tabbatacce zan albarkace shi, zan sa yă azurta, zai kuma ƙaru ƙwarai. Zai zama mahaifin masu mulki goma sha biyu, zan kuma maishe shi babban al’umma!
Také o Izmaele uslyšel jsem tě; a aj, požehnám jemu, a učiním to, aby se rozplodil, a rozmnožím ho náramně velmi; dvanáctero knížat zplodí, a rozšířím jej v národ veliký.
21 Amma dai zan kafa alkawarina da Ishaku wanda Saratu za tă haifa maka war haka shekara mai zuwa.”
Ale smlouvu svou utvrdím s Izákem, kteréhožť porodí Sára po roce, při tomto času.
22 Da ya gama magana da Ibrahim, sai Allah ya tashi daga gare shi.
A když dokonal Bůh řeč svou s ním, vstoupil od Abrahama.
23 A wannan rana, Ibrahim ya ɗauki ɗansa Ishmayel da dukan waɗanda aka haifa cikin gidansa, da waɗanda aka sayo da kuɗinsa, ya kuwa yi wa kowane namiji a cikin gidansa kaciya kamar yadda Allah ya faɗa masa.
Vzal tedy Abraham Izmaele syna svého, i všecky zrozené v domě svém, i všecky koupené za stříbro své, každého, kdož byl pohlaví mužského, z domácích svých, a obřezal tělo neobřízky jejich hned v ten den, jakž s ním Bůh mluvil.
24 Ibrahim yana da shekara tasa’in da tara sa’ad da aka yi masa kaciya,
A byl Abraham v devadesáti devíti letech, když obřezáno bylo tělo neobřízky jeho.
25 Ishmayel ɗansa kuma yana da shekara goma sha uku.
Izmael pak syn jeho byl v třinácti letech, když obřezáno bylo tělo neobřízky jeho.
26 Aka yi wa Ibrahim da ɗansa Ishmayel kaciya a rana ɗaya.
Jednoho a téhož dne obřezáni jsou, Abraham a Izmael syn jeho.
27 Aka yi wa kowane namiji a gidan Ibrahim kaciya, da waɗanda aka haifa a gidansa, da waɗanda aka sayo da kuɗi daga baƙo.
I všickni domácí jeho, doma zrození i za stříbro od cizozemce koupení, obřezáni jsou s ním.

< Farawa 17 >