< Farawa 16 >

1 To, Saira, matar Abram, ba tă haifa masa’ya’ya ba. Amma tana da wata baiwa mutuniyar Masar mai suna Hagar,
Karısı Saray Avram'a çocuk verememişti. Saray'ın Hacer adında Mısırlı bir cariyesi vardı.
2 saboda haka sai ta ce wa Abram, “Ubangiji ya hana mini haihuwar’ya’ya. Tafi ka kwana da baiwata; wataƙila in sami iyali ta wurinta.” Abram kuwa ya yarda da abin da Saira ta faɗa.
Saray Avram'a, “RAB çocuk sahibi olmamı engelledi” dedi, “Lütfen, cariyemle yat. Belki bu yoldan bir çocuk sahibi olabilirim.” Avram Saray'ın sözünü dinledi.
3 Saboda haka bayan Abram ya yi zama a Kan’ana shekaru goma, Saira matarsa ta ɗauki Hagar baiwarta ta ba wa mijinta tă zama matarsa.
Saray Mısırlı cariyesi Hacer'i kocası Avram'a karı olarak verdi. Bu olay Avram Kenan'da on yıl yaşadıktan sonra oldu.
4 Abram kuwa ya kwana da Hagar, ta kuma yi ciki. Sa’ad da Hagar ta gane tana da ciki, sai ta fara rena uwargijiyarta.
Avram Hacer'le yattı, Hacer hamile kaldı. Hacer hamile olduğunu anlayınca, hanımını küçük görmeye başladı.
5 Sai Saira ta ce wa Abram, “Kai ne da alhakin wahalan nan da nake sha. Na sa baiwata a hannunka, yanzu da ta sani tana da ciki, sai ta fara rena ni. Bari Ubangiji yă shari’anta tsakanina da kai.”
Saray Avram'a, “Bu haksızlık senin yüzünden başıma geldi!” dedi, “Cariyemi koynuna soktum. Hamile olduğunu anlayınca beni küçük görmeye başladı. Seninle benim aramda RAB karar versin.”
6 Abram ya ce, “Baiwarki tana a hannunki? Ki yi da ita yadda kika ga ya fi kyau.” Sai Saira ta wulaƙanta Hagar; saboda haka ta gudu daga gare ta.
Avram, “Cariyen senin elinde” dedi, “Neyi uygun görürsen yap.” Böylece Saray cariyesine sert davranmaya başladı. Hacer onun yanından kaçtı.
7 Mala’ikan Ubangiji ya sami Hagar kusa da maɓulɓula a jeji, ita ce maɓulɓular da take gefen hanya zuwa Shur.
RAB'bin meleği Hacer'i çölde bir pınarın, Şur yolundaki pınarın başında buldu.
8 Ya kuma ce mata, “Hagar, baiwar Saira, daga ina kika fito, kuma ina za ki?” Ta amsa ta ce, “Ina gudu ne daga wurin uwargijiyata Saira.”
Ona, “Saray'ın cariyesi Hacer, nereden gelip nereye gidiyorsun?” diye sordu. Hacer, “Hanımım Saray'dan kaçıyorum” diye yanıtladı.
9 Sai mala’ikan Ubangiji ya ce mata, “Koma wurin uwargijiyarki Saira, ki yi mata biyayya.”
RAB'bin meleği, “Hanımına dön ve ona boyun eğ” dedi,
10 Mala’ikan ya ƙara da cewa, “Zan ƙara zuriyarki har su yi yawan da ba wanda zai iya lasafta su.”
“Senin soyunu öyle çoğaltacağım ki, kimse sayamayacak.
11 Mala’ikan Ubangiji ya kuma ce mata, “Ga shi kina da ciki za ki kuwa haifi ɗa. Za ki ba shi suna Ishmayel, gama Ubangiji ya ga wahalarki.
“İşte hamilesin, bir oğlun olacak, Adını İsmail koyacaksın. Çünkü RAB sıkıntı içindeki yakarışını işitti.
12 Zai zama mutum mai halin jakin jeji. Hannunsa zai yi gāba da kowa, hannun kowa kuma zai yi gāba da shi. Zai yi zama gāba ga dukan’yan’uwansa.”
Oğlun yaban eşeğine benzer bir adam olacak, O herkese, herkes de ona karşı çıkacak. Kardeşlerinin hepsiyle çekişme içinde yaşayacak.”
13 Sai ta ba wa Ubangiji wanda ya yi magana da ita, wannan suna. “Kai Allah ne wanda yake ganina,” gama ta ce, “Yanzu na ga wanda yake ganina.”
Hacer, “Beni gören Tanrı'yı gerçekten gördüm mü?” diyerek kendisiyle konuşan RAB'be “El-Roi” adını verdi.
14 Shi ya sa ake kira rijiyar Beyer-Lahai-Royi tana nan har yanzu, tsakanin Kadesh da Bered.
Bu yüzden Kadeş'le Beret arasındaki o kuyuya Beer-Lahay-Roi adı verildi.
15 Haka fa Hagar ta haifa wa Abram ɗa, Abram kuwa ya ba da suna Ishmayel ga ɗan da ta haifa.
Hacer Avram'a bir erkek çocuk doğurdu. Avram çocuğun adını İsmail koydu.
16 Abram yana da shekaru 86 sa’ad da Hagar ta haifa masa Ishmayel.
Hacer İsmail'i doğurduğunda, Avram seksen altı yaşındaydı.

< Farawa 16 >