< Farawa 16 >
1 To, Saira, matar Abram, ba tă haifa masa’ya’ya ba. Amma tana da wata baiwa mutuniyar Masar mai suna Hagar,
Ahora Sarai, la esposa de Abram, no le había dado hijos; y ella tenía una sierva, una mujer de Egipto que se llamaba Agar.
2 saboda haka sai ta ce wa Abram, “Ubangiji ya hana mini haihuwar’ya’ya. Tafi ka kwana da baiwata; wataƙila in sami iyali ta wurinta.” Abram kuwa ya yarda da abin da Saira ta faɗa.
Y Sarai dijo a Abram: Mira, el Señor no me ha dejado tener hijos; ve a mi sierva, porque puedo tener una familia a través de ella. Y Abram hizo lo que Sarai dijo.
3 Saboda haka bayan Abram ya yi zama a Kan’ana shekaru goma, Saira matarsa ta ɗauki Hagar baiwarta ta ba wa mijinta tă zama matarsa.
Después de vivir Abram diez años en la tierra de Canaán, Sara tomó a Agar, su sierva egipcia, y se la dio a Abram por su mujer.
4 Abram kuwa ya kwana da Hagar, ta kuma yi ciki. Sa’ad da Hagar ta gane tana da ciki, sai ta fara rena uwargijiyarta.
Y tuvo relaciones con Agar y ella engendró, y cuando vio que estaba encinta, ya no sentía respeto por la esposa de su amo.
5 Sai Saira ta ce wa Abram, “Kai ne da alhakin wahalan nan da nake sha. Na sa baiwata a hannunka, yanzu da ta sani tana da ciki, sai ta fara rena ni. Bari Ubangiji yă shari’anta tsakanina da kai.”
Y Sarai dijo a Abram: Que mi mal esté contigo; te di mi sierva por tu mujer, y cuando ella vio que estaba encinta, ya no me respetó; que el Señor sea juez entre los dos. tu y yo.
6 Abram ya ce, “Baiwarki tana a hannunki? Ki yi da ita yadda kika ga ya fi kyau.” Sai Saira ta wulaƙanta Hagar; saboda haka ta gudu daga gare ta.
Y dijo Abram: La mujer está en tu poder; haz con ella lo que te parezca mejor. Y Sarai fue cruel con ella, por lo que huyó de ella.
7 Mala’ikan Ubangiji ya sami Hagar kusa da maɓulɓula a jeji, ita ce maɓulɓular da take gefen hanya zuwa Shur.
Y vino a ella un ángel del Señor junto a una fuente de agua en el desierto, junto a la fuente, en el camino a Shur.
8 Ya kuma ce mata, “Hagar, baiwar Saira, daga ina kika fito, kuma ina za ki?” Ta amsa ta ce, “Ina gudu ne daga wurin uwargijiyata Saira.”
Y él dijo: Agar, sierva de Sarai, ¿de dónde vienes y adónde vas? Y ella dijo: me estoy escapando de Sarai, la esposa de mi amo.
9 Sai mala’ikan Ubangiji ya ce mata, “Koma wurin uwargijiyarki Saira, ki yi mata biyayya.”
Y el ángel le dijo: Ve, y ponte bajo su autoridad.
10 Mala’ikan ya ƙara da cewa, “Zan ƙara zuriyarki har su yi yawan da ba wanda zai iya lasafta su.”
Y el ángel del Señor dijo: Tu descendencia aumentará mucho que no se podrá contar.
11 Mala’ikan Ubangiji ya kuma ce mata, “Ga shi kina da ciki za ki kuwa haifi ɗa. Za ki ba shi suna Ishmayel, gama Ubangiji ya ga wahalarki.
Y el ángel del SEÑOR dijo: He aquí que has concebido, y darás a luz un hijo, al cual pondrás el nombre de Ismael, porque los oídos del Señor estaban abiertos a tu aflicción.
12 Zai zama mutum mai halin jakin jeji. Hannunsa zai yi gāba da kowa, hannun kowa kuma zai yi gāba da shi. Zai yi zama gāba ga dukan’yan’uwansa.”
Y será como asno de montaña entre los hombres; su mano estará contra cada hombre y la mano de cada hombre contra él, y él mantendrá su lugar contra todos sus hermanos.
13 Sai ta ba wa Ubangiji wanda ya yi magana da ita, wannan suna. “Kai Allah ne wanda yake ganina,” gama ta ce, “Yanzu na ga wanda yake ganina.”
Y al Señor que hablaba con ella le dio este nombre: Tú eres un Dios que se ve; porque ella dijo: ¿acaso no he visto en la tierra baldía una visión de Dios y aún estoy viva?
14 Shi ya sa ake kira rijiyar Beyer-Lahai-Royi tana nan har yanzu, tsakanin Kadesh da Bered.
Así que esa fuente fue nombrada, Fuente de Vida y Visión: está entre Cades y Bered.
15 Haka fa Hagar ta haifa wa Abram ɗa, Abram kuwa ya ba da suna Ishmayel ga ɗan da ta haifa.
Y Agar dio a luz un hijo, el hijo de Abram, a quien Abram dio el nombre de Ismael.
16 Abram yana da shekaru 86 sa’ad da Hagar ta haifa masa Ishmayel.
Abram tenía ochenta y seis años cuando Agar dio a luz a Ismael.