< Farawa 16 >
1 To, Saira, matar Abram, ba tă haifa masa’ya’ya ba. Amma tana da wata baiwa mutuniyar Masar mai suna Hagar,
Abramova žena Saraja nije mu rađala djece. A imaše ona sluškinju Egipćanku - zvala se Hagara.
2 saboda haka sai ta ce wa Abram, “Ubangiji ya hana mini haihuwar’ya’ya. Tafi ka kwana da baiwata; wataƙila in sami iyali ta wurinta.” Abram kuwa ya yarda da abin da Saira ta faɗa.
I reče Saraja Abramu: “Vidiš, Jahve me učinio nerotkinjom. Hajde k mojoj sluškinji, možda ću imati djece.” Abram posluša riječ Sarajinu.
3 Saboda haka bayan Abram ya yi zama a Kan’ana shekaru goma, Saira matarsa ta ɗauki Hagar baiwarta ta ba wa mijinta tă zama matarsa.
Tako, pošto je Abram proboravio deset godina u zemlji kanaanskoj, njegova žena Saraja uzme Hagaru, Egipćanku, sluškinju svoju, pa je dade svome mužu Abramu za ženu.
4 Abram kuwa ya kwana da Hagar, ta kuma yi ciki. Sa’ad da Hagar ta gane tana da ciki, sai ta fara rena uwargijiyarta.
Uđe on k Hagari te ona zače. A kad je vidjela da je začela, s prezirom je gledala na svoju gospodaricu.
5 Sai Saira ta ce wa Abram, “Kai ne da alhakin wahalan nan da nake sha. Na sa baiwata a hannunka, yanzu da ta sani tana da ciki, sai ta fara rena ni. Bari Ubangiji yă shari’anta tsakanina da kai.”
Tada reče Saraja Abramu: “Nepravda što se meni nanosi tvoja je krivnja! Prepustila sam svoju sluškinju tvome zagrljaju, ali otkako opazi da je zanijela, s prezirom na me gleda. Jahve sudio i meni i tebi!”
6 Abram ya ce, “Baiwarki tana a hannunki? Ki yi da ita yadda kika ga ya fi kyau.” Sai Saira ta wulaƙanta Hagar; saboda haka ta gudu daga gare ta.
Nato Abram odvrati Saraji: “Tvoja je sluškinja u tvojoj ruci: kako ti se čini da je dobro, tako prema njoj postupi!” Saraja postupi prema njoj tako loše da ona od nje pobježe.
7 Mala’ikan Ubangiji ya sami Hagar kusa da maɓulɓula a jeji, ita ce maɓulɓular da take gefen hanya zuwa Shur.
Anđeo Jahvin nađe je kod izvora u pustinji - uz vrelo što je na putu prema Šuru -
8 Ya kuma ce mata, “Hagar, baiwar Saira, daga ina kika fito, kuma ina za ki?” Ta amsa ta ce, “Ina gudu ne daga wurin uwargijiyata Saira.”
pa je zapita: “Hagaro, sluškinjo Sarajina, odakle dolaziš i kamo ideš?” “Bježim, evo, od svoje gospodarice Saraje”, odgovori ona.
9 Sai mala’ikan Ubangiji ya ce mata, “Koma wurin uwargijiyarki Saira, ki yi mata biyayya.”
Nato joj anđeo Jahvin reče: “Vrati se svojoj gospodarici i pokori joj se!”
10 Mala’ikan ya ƙara da cewa, “Zan ƙara zuriyarki har su yi yawan da ba wanda zai iya lasafta su.”
Još joj reče anđeo Jahvin: “Tvoje ću potomstvo silno umnožiti; od mnoštva se neće moći ni prebrojiti.”
11 Mala’ikan Ubangiji ya kuma ce mata, “Ga shi kina da ciki za ki kuwa haifi ɗa. Za ki ba shi suna Ishmayel, gama Ubangiji ya ga wahalarki.
Dalje joj je anđeo Jahvin rekao: “Gle, zanijela si i rodit ćeš sina. Nadjeni mu ime Jišmael, jer Jahve ču jad tvoj.
12 Zai zama mutum mai halin jakin jeji. Hannunsa zai yi gāba da kowa, hannun kowa kuma zai yi gāba da shi. Zai yi zama gāba ga dukan’yan’uwansa.”
On će biti kao divlje magare: ruka će se njegova dizati na svakoga i svačija ruka na njega; i pred licem sve mu braće on će stan sebi podići.”
13 Sai ta ba wa Ubangiji wanda ya yi magana da ita, wannan suna. “Kai Allah ne wanda yake ganina,” gama ta ce, “Yanzu na ga wanda yake ganina.”
A Jahvu koji joj govoraše nazva: “Ti si El Roi - Svevid Bog”, jer - reče ona - “vidjeh Boga i nakon viđenja - još živim!”
14 Shi ya sa ake kira rijiyar Beyer-Lahai-Royi tana nan har yanzu, tsakanin Kadesh da Bered.
Stoga se taj zdenac zove Beer Lahaj Roi - Zdenac životvornog Svevida, a eno ga između Kadeša i Bereda.
15 Haka fa Hagar ta haifa wa Abram ɗa, Abram kuwa ya ba da suna Ishmayel ga ɗan da ta haifa.
Rodi Hagara Abramu sina, a Abram sinu što mu ga rodi Hagara nadjene ime Jišmael.
16 Abram yana da shekaru 86 sa’ad da Hagar ta haifa masa Ishmayel.
Abramu je bilo osamdeset i šest godina kad mu je Hagara rodila Jišmaela.