< Farawa 15 >
1 Bayan wannan, maganar Ubangiji ta zo wa Abram cikin mafarki cewa, “Kada ka ji tsoro, Abram. Ni ne garkuwarka, kuma ladanka zai zama mai girma.”
Depois destas coisas a palavra de Javé veio a Abram em uma visão, dizendo: “Não tenha medo, Abram”. Eu sou seu escudo, sua recompensa excessivamente grande”.
2 Amma Abram ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, mene ne za ka ba ni, ganin cewa ba na haihuwa, wanda kuma zai gāji gādon gidana shi ne Eliyezer mutumin Damaskus?”
Abram disse: “Senhor Javé, o que o Senhor me dará, já que eu fico sem filhos, e aquele que herdará meus bens é Eliézer de Damasco”?
3 Abram ya kuma ce, “Ga shi ba ka ba ni ɗa ba, don haka bawan da aka haifa a gidana ne zai zama magājina.”
Abram disse: “Eis que não me deste filhos; e eis que um nascido em minha casa é meu herdeiro”.
4 Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo gare shi cewa, “Wannan mutum ba zai zama magājinka ba, ɗa da yake zuwa daga jikinka ne zai zama magājinka.”
Eis que a palavra de Javé veio a ele, dizendo: “Este homem não será seu herdeiro, mas aquele que sairá de seu próprio corpo será seu herdeiro”.
5 Sai Ubangiji ya fito da kai shi waje ya ce, “Ka dubi sammai ka kuma ƙirga taurari, in har za ka iya ƙirga su.” Sa’an nan ya ce masa, “Haka zuriyarka za tă zama.”
Yahweh o levou para fora, e disse: “Olhe agora em direção ao céu, e conte as estrelas, se você for capaz de contá-las”. Ele disse a Abram: “Assim será a sua descendência”.
6 Abram ya gaskata, Ubangiji kuma ya lasafta shi adalci ga Abram.
Ele acreditou em Yahweh, que lhe creditou isso por justiça.
7 Ubangiji ya kuma ce wa Abram, “Ni ne Ubangiji wanda ya fitar da kai daga Ur na Kaldiyawa, domin in ba ka wannan ƙasa ka mallake ta.”
Ele disse a Abram: “Eu sou Yahweh, que te tirei de Ur dos Caldeus, para te dar esta terra para herdá-la”.
8 Amma Abram ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, yaya zan san cewa zan mallake ta?”
Ele disse: “Senhor Yahweh, como saberei que vou herdá-lo?”
9 Saboda haka Allah ya ce masa, “Kawo mini karsana, akuya, da kuma rago kowanne yă kasance shi shekara uku ne, da kurciya da kuma ɗan tattabara.”
Ele lhe disse: “Traga-me uma novilha de três anos, uma cabra de três anos, um carneiro de três anos, uma rola e um pombo jovem”.
10 Abram ya kawo waɗannan duka a gaban Allah, ya raba kowannensu a tsakiya, ya ajiye su gab da juna, amma bai tsaga tsuntsayen a tsaka ba.
Ele lhe trouxe todas estas, e as dividiu no meio, e as colocou uma à outra; mas ele não dividiu as aves.
11 Sai tsuntsaye masu cin nama suka sauko a kan gawawwakin, amma Abram ya kore su.
As aves de rapina desceram sobre as carcaças, e Abram as expulsou.
12 Yayinda rana tana fāɗuwa, sai Abram ya yi barci mai zurfi, sai wani duhu mai kauri mai kuma bantsoro ya rufe shi.
Quando o sol estava se pondo, um sono profundo caiu sobre Abram. Agora o terror e a grande escuridão caíram sobre ele.
13 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Abram, “Ka sani tabbatacce cewa shekaru ɗari huɗu, zuriyarka za tă zama baƙi a ƙasar da ba tasu ba, za a mai da su bayi, a kuma wulaƙanta su.
Ele disse a Abram: “Saiba com certeza que seus descendentes viverão como estrangeiros em uma terra que não é deles, e os servirão”. Eles os afligirão por quatrocentos anos”.
14 Amma zan hukunta al’ummar da suka yi bauta kamar bayi, daga baya kuma za su fita da mallaka mai yawa.
Eu também julgarei aquela nação, a quem eles servirão. Depois, eles sairão com grande riqueza;
15 Amma kai za ka koma wurin kakanninka cikin salama a kuma binne ka da kyakkyawan tsufa.
mas vocês irão em paz para seus pais. Vocês serão enterrados numa boa velhice.
16 A tsara ta huɗu zuriyarka za tă komo nan, saboda zunubin Amoriyawa bai riga ya cika ba.”
Na quarta geração eles virão aqui novamente, pois a iniqüidade do amorreu ainda não está cheia”.
17 Sa’ad da rana ta fāɗi, aka kuwa yi duhu, sai wata tukunya mai hayaƙi, mai harshen wuta mai ci, ta bayyana, ta kuma wuce tsakanin abubuwan nan da aka tsaga.
Aconteceu que, quando o sol se pôs, e estava escuro, eis que um forno fumegante e uma tocha ardente passaram entre estas peças.
18 A wannan rana, Ubangiji ya yi alkawari da Abram ya ce, “Ga zuriyarka na ba da wannan ƙasa, daga kogin Masar zuwa babban kogi, Yuferites ke nan,
Naquele dia Javé fez um pacto com Abrão, dizendo: “Eu dei esta terra à sua prole, desde o rio do Egito até o grande rio, o rio Eufrates”:
19 ƙasar Keniyawa, Kenizziyawa, Kadmoniyawa,
a terra dos quenitas, dos quenizitas, dos kadmonitas,
20 Hittiyawa, Ferizziyawa, Refahiyawa,
os hititas, os perizitas, os refaim,
21 Amoriyawa, Kan’aniyawa, Girgashiyawa da kuma Yebusiyawa.”
os amoritas, os cananeus, os girgashitas, e os jebusitas”.