< Farawa 15 >

1 Bayan wannan, maganar Ubangiji ta zo wa Abram cikin mafarki cewa, “Kada ka ji tsoro, Abram. Ni ne garkuwarka, kuma ladanka zai zama mai girma.”
Ces choses s’étant ainsi passées, la parole du Seigneur se fit entendre à Abram dans une vision, disant: Abram, ne crains pas, je suis ton protecteur et ta récompense grande à l’infini.
2 Amma Abram ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, mene ne za ka ba ni, ganin cewa ba na haihuwa, wanda kuma zai gāji gādon gidana shi ne Eliyezer mutumin Damaskus?”
Et Abram dit: Seigneur Dieu, que me donnerez-vous? moi, je m’en irai sans enfants; car cet Eliézer de Damas est le fils de l’intendant de ma maison.
3 Abram ya kuma ce, “Ga shi ba ka ba ni ɗa ba, don haka bawan da aka haifa a gidana ne zai zama magājina.”
Et Abram ajouta: Pour moi, vous ne m’avez pas donné de postérité, aussi voilà que le serviteur né dans ma maison sera mon héritier.
4 Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo gare shi cewa, “Wannan mutum ba zai zama magājinka ba, ɗa da yake zuwa daga jikinka ne zai zama magājinka.”
Et aussitôt la parole du Seigneur se fit entendre à lui, disant: Celui-là ne sera pas ton héritier; mais celui qui sortira de tes entrailles, tu l’auras pour héritier.
5 Sai Ubangiji ya fito da kai shi waje ya ce, “Ka dubi sammai ka kuma ƙirga taurari, in har za ka iya ƙirga su.” Sa’an nan ya ce masa, “Haka zuriyarka za tă zama.”
Et il l’emmena dehors et lui dit: Regarde le ciel, et compte les étoiles, si tu peux. Et il ajouta: Ainsi sera ta postérité.
6 Abram ya gaskata, Ubangiji kuma ya lasafta shi adalci ga Abram.
Abram crut à Dieu, et ce lui fut imputé à justice.
7 Ubangiji ya kuma ce wa Abram, “Ni ne Ubangiji wanda ya fitar da kai daga Ur na Kaldiyawa, domin in ba ka wannan ƙasa ka mallake ta.”
Le Seigneur lui dit encore: Je suis le Seigneur qui t’ai fait sortir d’Ur des Chaldéens, pour te donner cette terre, afin que tu la possèdes.
8 Amma Abram ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, yaya zan san cewa zan mallake ta?”
Mais Abram demanda: Seigneur Dieu, d’où pourrai-je savoir que je dois la posséder?
9 Saboda haka Allah ya ce masa, “Kawo mini karsana, akuya, da kuma rago kowanne yă kasance shi shekara uku ne, da kurciya da kuma ɗan tattabara.”
Et répondant, le Seigneur: Prends, dit-il, une génisse de trois ans, une chèvre de trois ans, un bélier de trois ans, de même qu’une tourterelle et une colombe.
10 Abram ya kawo waɗannan duka a gaban Allah, ya raba kowannensu a tsakiya, ya ajiye su gab da juna, amma bai tsaga tsuntsayen a tsaka ba.
Abram prenant tous ces animaux, les divisa par la moitié, et plaça les deux parties vis-à-vis l’une de l’autre; mais les oiseaux, il ne les divisa point.
11 Sai tsuntsaye masu cin nama suka sauko a kan gawawwakin, amma Abram ya kore su.
Or les oiseaux descendirent sur les corps morts, et Abram les chassait.
12 Yayinda rana tana fāɗuwa, sai Abram ya yi barci mai zurfi, sai wani duhu mai kauri mai kuma bantsoro ya rufe shi.
Et comme le soleil se couchait, un profond sommeil s’empara d’Abram, et une terreur grande et sombre le saisit.
13 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Abram, “Ka sani tabbatacce cewa shekaru ɗari huɗu, zuriyarka za tă zama baƙi a ƙasar da ba tasu ba, za a mai da su bayi, a kuma wulaƙanta su.
Alors il lui fut dit: Sache dès à présent que ta postérité doit être étrangère dans un pays qui ne sera pas le sien; qu’on les réduira en servitude, et qu’on les opprimera durant quatre cents ans.
14 Amma zan hukunta al’ummar da suka yi bauta kamar bayi, daga baya kuma za su fita da mallaka mai yawa.
Mais la nation à laquelle ils seront assujettis, c’est moi qui la jugerai; et après ils sortiront avec de grandes richesses.
15 Amma kai za ka koma wurin kakanninka cikin salama a kuma binne ka da kyakkyawan tsufa.
Pour toi, tu iras en paix vers tes pères, enseveli dans une heureuse vieillesse.
16 A tsara ta huɗu zuriyarka za tă komo nan, saboda zunubin Amoriyawa bai riga ya cika ba.”
Ainsi à la quatrième génération, ils reviendront ici; car les iniquités des Amorrhéens ne sont pas parvenues à leur comble jusqu’au temps présent.
17 Sa’ad da rana ta fāɗi, aka kuwa yi duhu, sai wata tukunya mai hayaƙi, mai harshen wuta mai ci, ta bayyana, ta kuma wuce tsakanin abubuwan nan da aka tsaga.
Or, quand le soleil fut couché, il se fit une obscurité ténébreuse, et il parut un four qui fumait, et une lampe de feu qui passait au milieu des animaux divisés.
18 A wannan rana, Ubangiji ya yi alkawari da Abram ya ce, “Ga zuriyarka na ba da wannan ƙasa, daga kogin Masar zuwa babban kogi, Yuferites ke nan,
En ce jour-là le Seigneur fit une alliance avec Abram, disant: C’est à ta postérité que je donnerai ce pays, depuis le fleuve d’Égypte jusqu’au grand fleuve d’Euphrate;
19 ƙasar Keniyawa, Kenizziyawa, Kadmoniyawa,
Les Cinéens, les Généséens, les Cedmonéens,
20 Hittiyawa, Ferizziyawa, Refahiyawa,
Les Héthéens, les Phéréséens, et les Raphaïtes aussi.
21 Amoriyawa, Kan’aniyawa, Girgashiyawa da kuma Yebusiyawa.”
Les Armorrhéens, les Chananéens, les Gergéséens et les Jébuséens.

< Farawa 15 >