< Farawa 15 >

1 Bayan wannan, maganar Ubangiji ta zo wa Abram cikin mafarki cewa, “Kada ka ji tsoro, Abram. Ni ne garkuwarka, kuma ladanka zai zama mai girma.”
Some time later, Abram had a vision in which Yahweh spoke to him and said, “Do not be afraid of (anything/your enemies). I will protect you [MTY], and I will give a great reward.”
2 Amma Abram ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, mene ne za ka ba ni, ganin cewa ba na haihuwa, wanda kuma zai gāji gādon gidana shi ne Eliyezer mutumin Damaskus?”
But Abram replied, “Yahweh God, how can you give me what I truly want, because I have no children, and the one who will be like a son and inherit all my possessions is my servant Eliezer from Damascus!”
3 Abram ya kuma ce, “Ga shi ba ka ba ni ɗa ba, don haka bawan da aka haifa a gidana ne zai zama magājina.”
Abram added, “You have not given me any children, so think about this: A servant in my household will inherit all I own!”
4 Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo gare shi cewa, “Wannan mutum ba zai zama magājinka ba, ɗa da yake zuwa daga jikinka ne zai zama magājinka.”
Yahweh replied, “No! He will not be the one who will inherit it. Instead, you yourself will be the father of the one who will inherit everything you own.”
5 Sai Ubangiji ya fito da kai shi waje ya ce, “Ka dubi sammai ka kuma ƙirga taurari, in har za ka iya ƙirga su.” Sa’an nan ya ce masa, “Haka zuriyarka za tă zama.”
Then Yahweh took Abram outside [of his tent] and said, “Look up at the sky! Can you count the stars? No, you cannot count them because there are so many of them, and your descendants will be as numerous as the stars.”
6 Abram ya gaskata, Ubangiji kuma ya lasafta shi adalci ga Abram.
Abram believed that what Yahweh said would happen. And because of that, Yahweh considered that Abram was righteous.
7 Ubangiji ya kuma ce wa Abram, “Ni ne Ubangiji wanda ya fitar da kai daga Ur na Kaldiyawa, domin in ba ka wannan ƙasa ka mallake ta.”
Yahweh also said to him, “I am Yahweh. I am the one who brought you from Ur in Chaldea land. I brought you here to give you this land to possess.”
8 Amma Abram ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, yaya zan san cewa zan mallake ta?”
But Abram replied, “Yahweh God, how can I know for sure that this land will belong to me?”
9 Saboda haka Allah ya ce masa, “Kawo mini karsana, akuya, da kuma rago kowanne yă kasance shi shekara uku ne, da kurciya da kuma ɗan tattabara.”
God said to him, “Bring a three-year-old heifer and a three-year-old goat to me, and a dove and a pigeon.”
10 Abram ya kawo waɗannan duka a gaban Allah, ya raba kowannensu a tsakiya, ya ajiye su gab da juna, amma bai tsaga tsuntsayen a tsaka ba.
So Abram brought all of them and killed them and cut each of the animals in half. He arranged the halves of each one, side by side. But he did not cut the pigeon and dove in half.
11 Sai tsuntsaye masu cin nama suka sauko a kan gawawwakin, amma Abram ya kore su.
Birds that eat dead flesh came down to eat the carcasses, but Abram shooed them away.
12 Yayinda rana tana fāɗuwa, sai Abram ya yi barci mai zurfi, sai wani duhu mai kauri mai kuma bantsoro ya rufe shi.
As the sun was going down, Abram fell sound asleep, and suddenly everything around him became dark and frightening.
13 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Abram, “Ka sani tabbatacce cewa shekaru ɗari huɗu, zuriyarka za tă zama baƙi a ƙasar da ba tasu ba, za a mai da su bayi, a kuma wulaƙanta su.
Then God said to Abram, “I want you to know that your descendants will become foreigners living in a land that does not belong to them. They will become slaves of the owners of that land. The owners of the land will mistreat them for 400 years.
14 Amma zan hukunta al’ummar da suka yi bauta kamar bayi, daga baya kuma za su fita da mallaka mai yawa.
But then I will punish the people of that country that made them become slaves, and then your descendants will leave that country, taking many possessions with them.
15 Amma kai za ka koma wurin kakanninka cikin salama a kuma binne ka da kyakkyawan tsufa.
But as for you, you will die [EUP] peacefully when you are very old.
16 A tsara ta huɗu zuriyarka za tă komo nan, saboda zunubin Amoriyawa bai riga ya cika ba.”
After your descendants have been slaves for 400 years, they will return here, and take control of this land and defeat the Amor people-group. Those people will, because those people have not yet sinned enough to deserve to be punished now.”
17 Sa’ad da rana ta fāɗi, aka kuwa yi duhu, sai wata tukunya mai hayaƙi, mai harshen wuta mai ci, ta bayyana, ta kuma wuce tsakanin abubuwan nan da aka tsaga.
When the sun had set and it had become dark, [unexpectedly] a blazing torch and a clay pot containing burning coals from which smoke was rising appeared and went between the halves of the animals.
18 A wannan rana, Ubangiji ya yi alkawari da Abram ya ce, “Ga zuriyarka na ba da wannan ƙasa, daga kogin Masar zuwa babban kogi, Yuferites ke nan,
And on that day Yahweh made an agreement with Abram. Yahweh told him, “I will give to your descendants all the land between the river that is on the eastern border of Egypt to the south, and north to the huge Euphrates River.
19 ƙasar Keniyawa, Kenizziyawa, Kadmoniyawa,
That is the land where the Ken, the Keniz, the Kidmon,
20 Hittiyawa, Ferizziyawa, Refahiyawa,
the Heth, the Periz, the Repha,
21 Amoriyawa, Kan’aniyawa, Girgashiyawa da kuma Yebusiyawa.”
the Amor, the Canaan, the Girgash, and the Tebus people-groups live.”

< Farawa 15 >