< Farawa 15 >

1 Bayan wannan, maganar Ubangiji ta zo wa Abram cikin mafarki cewa, “Kada ka ji tsoro, Abram. Ni ne garkuwarka, kuma ladanka zai zama mai girma.”
Efter at dette var sket, kom Herrens Ord til Abram i et Syn, og sagde: Frygt ikke, Abram, jeg er dit Skjold og din meget store Løn.
2 Amma Abram ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, mene ne za ka ba ni, ganin cewa ba na haihuwa, wanda kuma zai gāji gādon gidana shi ne Eliyezer mutumin Damaskus?”
Og Abram sagde: Herre, Herre, hvad vil du give mig? og jeg gaar hen uden Børn, og den, der forestaar mit Hus, er Elieser af Damaskus.
3 Abram ya kuma ce, “Ga shi ba ka ba ni ɗa ba, don haka bawan da aka haifa a gidana ne zai zama magājina.”
Og Abram sagde: Se, mig har du intet Afkom givet, og se, min vornede arver mig.
4 Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo gare shi cewa, “Wannan mutum ba zai zama magājinka ba, ɗa da yake zuwa daga jikinka ne zai zama magājinka.”
Og se, Herrens Ord skete til ham og sagde: Denne, han skal ikke arve dig; men den, som skal udkomme af dit Liv, han skal arve dig.
5 Sai Ubangiji ya fito da kai shi waje ya ce, “Ka dubi sammai ka kuma ƙirga taurari, in har za ka iya ƙirga su.” Sa’an nan ya ce masa, “Haka zuriyarka za tă zama.”
Og han førte ham udenfor og sagde: Kære, se til Himmelen, og tæl Stjernerne, om du kan tælle dem; og han sagde til ham: Saa skal dit Afkom vorde.
6 Abram ya gaskata, Ubangiji kuma ya lasafta shi adalci ga Abram.
Og han troede paa Herren, og han regnede ham det til Retfærdighed.
7 Ubangiji ya kuma ce wa Abram, “Ni ne Ubangiji wanda ya fitar da kai daga Ur na Kaldiyawa, domin in ba ka wannan ƙasa ka mallake ta.”
Og han sagde til ham: jeg er Herren, som udførte dig fra Ur i Kaldæa for at give dig dette Land til at eje det.
8 Amma Abram ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, yaya zan san cewa zan mallake ta?”
Da sagde han: Herre, Herre, hvorpaa skal jeg kende, at jeg skal eje det?
9 Saboda haka Allah ya ce masa, “Kawo mini karsana, akuya, da kuma rago kowanne yă kasance shi shekara uku ne, da kurciya da kuma ɗan tattabara.”
Og han sagde til ham: Tag mig en tre Aar gammel Kvie og en tre Aar gammel Ged og en tre Aar gammel Vædder og en Turteldue og en Dueunge.
10 Abram ya kawo waɗannan duka a gaban Allah, ya raba kowannensu a tsakiya, ya ajiye su gab da juna, amma bai tsaga tsuntsayen a tsaka ba.
Og han tog ham alt dette og delte det midt over og lagde den ene Del deraf tvært overfor den anden; men Fuglene delte han ikke.
11 Sai tsuntsaye masu cin nama suka sauko a kan gawawwakin, amma Abram ya kore su.
Og Rovfugle sloge ned paa de døde Kroppe; men Abram jog dem derfra.
12 Yayinda rana tana fāɗuwa, sai Abram ya yi barci mai zurfi, sai wani duhu mai kauri mai kuma bantsoro ya rufe shi.
Og det skete, der Solen vilde gaa ned, da faldt en dyb Søvn paa Abram, og se, der faldt Forfærdelse og stort Mørke over ham.
13 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Abram, “Ka sani tabbatacce cewa shekaru ɗari huɗu, zuriyarka za tă zama baƙi a ƙasar da ba tasu ba, za a mai da su bayi, a kuma wulaƙanta su.
Da sagde han til Abram: du skal visseligen vide, at dit Afkom skal være fremmed i et Land, som ikke er deres, og de skulle trælle for dem, der skulle plage dem, fire Hundrede Aar.
14 Amma zan hukunta al’ummar da suka yi bauta kamar bayi, daga baya kuma za su fita da mallaka mai yawa.
Men jeg vil ogsaa dømme det Folk, som de skulle tjene; og derefter skulle de udgaa med meget Gods.
15 Amma kai za ka koma wurin kakanninka cikin salama a kuma binne ka da kyakkyawan tsufa.
Men du skal fare til dine Fædre med Fred, og du skal blive begravet i en god Alderdom.
16 A tsara ta huɗu zuriyarka za tă komo nan, saboda zunubin Amoriyawa bai riga ya cika ba.”
Og i den fjerde Slægt skulle de komme hid igen; thi Amoritens Ondskab er endnu ikke fuld.
17 Sa’ad da rana ta fāɗi, aka kuwa yi duhu, sai wata tukunya mai hayaƙi, mai harshen wuta mai ci, ta bayyana, ta kuma wuce tsakanin abubuwan nan da aka tsaga.
Og det skete, der Solen var nedgangen, og der var stort Mørke, se, da var der en rygende Ovn og Ilds Blus, som for hen imellem disse Stykker.
18 A wannan rana, Ubangiji ya yi alkawari da Abram ya ce, “Ga zuriyarka na ba da wannan ƙasa, daga kogin Masar zuwa babban kogi, Yuferites ke nan,
Paa den samme Dag gjorde Herren en Pagt med Abram og sagde: Dit Afkom har jeg givet dette Land, fra Ægyptens Flod indtil den store Flod, den Flod Frat,
19 ƙasar Keniyawa, Kenizziyawa, Kadmoniyawa,
Keniter og Kenisiter og Kadmoniter
20 Hittiyawa, Ferizziyawa, Refahiyawa,
og Hethiter og Feresiter og Refaiter
21 Amoriyawa, Kan’aniyawa, Girgashiyawa da kuma Yebusiyawa.”
og Amoriter og Kananiter og Girgasiter og Jebusiter.

< Farawa 15 >