< Farawa 14 >
1 A zamanin Amrafel sarkin Shinar, shi da Ariyok sarkin Ellasar, Kedorlayomer sarkin Elam, da kuma Tidal sarkin Goyim
And in the dayes of Amraphel King of Shinar, Arioch King of Ellasar, Chedor-laomer King of Elam, and Tidal king of the nations:
2 suka tafi don su yaƙi Bera sarkin Sodom, Birsha sarkin Gomorra, Shinab sarkin Adma, Shemeber sarkin Zeboyim, da kuma sarkin Bela (wato, Zowar).
These men made warre with Bera King of Sodom, and with Birsha King of Gomorah, Shinab King of Admah, and Shemeber King of Zeboiim, and the King of Bela, which is Zoar.
3 Dukan waɗannan sarakuna na bayan nan suka haɗa kai a Kwarin Siddim (Teku Gishiri).
All these ioyned together in the vale of Siddim, which is the salt Sea.
4 Shekara goma sha biyu suna bauta wa Kedorlayomer, amma a shekara ta sha uku sai suka yi tawaye.
Twelue yeere were they subiect to Chedor-laomer, but in the thirteenth yeere they rebelled.
5 A shekara ta goma sha huɗu, Kedorlayomer da sarakunan da suka haɗa kai da shi suka tafi suka cinye Refahiyawa a Ashterot Karnayim, Zuziyawa a Ham, Emawa a Shabe Kiriyatayim,
And in the fourteenth yeere came Chedor-laomer, and the Kings that were with him, and smote the Rephaims in Ashteroth Karnaim, and the Zuzims in Ham, and the Emims in Shaueh Kiriathaim,
6 da Horiyawa a ƙasar tudun Seyir har zuwa El Faran kusa da hamada.
And the Horites in their mount Seir, vnto the plaine of Paran, which is by the wildernesse.
7 Sa’an nan suka juya suka tafi En Mishfat (wato, Kadesh), suka cinye dukan ƙasar Amalekawa, da kuma Amoriyawa waɗanda suke zaune a Hazazon Tamar.
And they returned and came to En-mishpat, which is Kadesh, and smote all the countrey of the Amalekites, and also the Amorites that dwelled in Hazezon-tamar.
8 Sai sarkin Sodom, sarkin Gomorra, sarkin Adma, sarkin Zeboyim da sarkin Bela (wato, Zowar), suka fita suka ja dāgā a Kwarin Siddim
Then went out the King of Sodom, and the King of Gomorah, and the King of Admah, and the King of Zeboiim, and the King of Bela, which is Zoar: and they ioyned battell with them in the vale of Siddim:
9 gāba da Kedorlayomer sarkin Elam, Tidal sarkin Goyim, Amrafel sarkin Shinar da Ariyok sarkin Ellasar; sarakuna huɗu gāba da biyar.
To wit, with Chedor-laomer king of Elam, and Tidal king of nations, and Amraphel king of Shinar, and Arioch king of Ellasar: foure Kings against fiue.
10 Kwarin Siddim kuwa ya cika da ramummukan kwalta, sa’ad da sarakunan Sodom da Gomorra suka gudu kuwa, waɗansu mutane suka fāɗa cikin ramummukan kwaltan, sauran kuwa suka gudu zuwa tuddai.
Now the vale of Siddim was full of slime pits, and the Kings of Sodom and Gomorah fled and fell there: and ye residue fled to the mountaine.
11 Sarakunan nan huɗu suka washe dukan kayayyakin Sodom da Gomorra, da kuma dukan abincinsu, sa’an nan suka tafi.
Then they tooke all the substance of Sodom and Gomorah, and al their vitailes and went their way.
12 Suka kuma kama Lot ɗan ɗan’uwan Abram, wanda yake zaune a Sodom, da kayayyakinsa, suka yi tafiyarsu.
They tooke Lot also Abrams brothers sonne and his substance (for he dwelt at Sodom) and departed.
13 Sai wani wanda ya tsira, ya zo ya faɗa wa Abram mutumin Ibraniyawa. Abram kuwa yana zama kusa da manyan itatuwan Mamre, Mamre mutumin Amoriyawa ne ɗan’uwan Eshkol da Aner, su kuwa abokan Abram ne.
Then came one that had escaped, and told Abram the Ebrew, which dwelt in the plaine of Mamre ye Amorite, brother of Eshcol, and brother of Aner, which were confederat with Abram.
14 Da Abram ya ji cewa an kama danginsa, sai ya tara horarrun mutane 318, da aka haifa a gidansa, ya bi sawun sarakunan da suka tafi da Lot, har Dan.
When Abram heard that his brother was taken, he brought forth of them that were borne and brought vp in his house, three hundreth and eighteene, and pursued them vnto Dan.
15 Da dad dare, Abram ya rarraba mutanensa don su fāɗa wa sarakunan nan, ya ɗibge su, ya kore su har zuwa Hoba, arewa da Damaskus.
Then he, and his seruants deuided them selues against them by night, and smote them and pursued them vnto Hobah, which is on the left side of Damascus,
16 Ya washe su da kuma dukan kayayyakinsu, ya kuma dawo da Lot danginsa da mallakarsa, tare da mata da sauran mutane.
And he recouered all the substance, and also brought againe his brother Lot, and his goods, and the women also and the people.
17 Bayan Abram ya dawo daga cin Kedorlayomer da sarakunan da suka haɗa kai da shi a yaƙi, sai sarkin Sodom ya fito don yă tarye Abram a Kwarin Shabe (wato, Kwarin Sarki).
After that he returned from the slaughter of Chedor-laomer, and of the Kings that were with him, came the King of Sodom foorth to meete him in the valley of Shaueh, which is the Kings dale.
18 Sai Melkizedek sarkin Salem ya kawo burodi da ruwan inabi. Shi firist ne na Allah Mafi Ɗaukaka,
And Melchi-zedek King of Shalem brought foorth bread and wine: and he was a Priest of the most high God.
19 ya albarkaci Abram yana cewa, “Allah Mafi Ɗaukaka Mahaliccin sama da ƙasa yă albarkace Abram.
Therefore he blessed him, saying, Blessed art thou, Abram, of God most high possessour of heauen and earth,
20 Kuma albarka ta tabbata ga Allah Mafi Ɗaukaka wanda ya ba da maƙiyanka a hannunka.” Sa’an nan Abram ya ba shi kashi ɗaya bisa goma na kome.
And blessed be the most high God, which hath deliuered thine enemies into thine hand. And Abram gaue him tythe of all.
21 Sarkin Sodom ya ce wa Abram, “Ka ba ni mutanena da ka ƙwace daga hannun sarakunan nan kawai, ka riƙe kayayyakin don kanka.”
Then the King of Sodom saide to Abram, Giue me the persons, and take the goodes to thy selfe.
22 Amma Abram ya ce, wa sarkin Sodom, “Na ɗaga hannu ga Ubangiji Allah Mafi Ɗaukaka, Mahaliccin sama da ƙasa, na riga na rantse
And Abram said to the King of Sodom, I haue lift vp mine hand vnto the Lord the most hie God possessor of heauen and earth,
23 cewa ba zan karɓi kome da yake naka ba, ko zare ko maɗaurin takalma, don kada ka ce, ‘Na azurta Abram.’
That I will not take of all that is thine, so much as a threde or shoolatchet, lest thou shouldest say, I haue made Abram riche,
24 Ba zan karɓi kome ba, sai dai abin da mutanena suka ci da kuma rabon mutanen da suka tafi tare da ni, ga Aner, Eshkol, da Mamre. Bari su ɗauki rabonsu.”
Saue onely that, which the yong men haue eaten, and the partes of the men which went with me, Aner, Eshcol, and Mamre: let them take their partes.