< Farawa 14 >
1 A zamanin Amrafel sarkin Shinar, shi da Ariyok sarkin Ellasar, Kedorlayomer sarkin Elam, da kuma Tidal sarkin Goyim
At that time Amraphel was king of Shinar, and he allied himself with Arioch, king of Ellasar, Chedorlaomer, king of Elam, and Tidal, king of Goiim.
2 suka tafi don su yaƙi Bera sarkin Sodom, Birsha sarkin Gomorra, Shinab sarkin Adma, Shemeber sarkin Zeboyim, da kuma sarkin Bela (wato, Zowar).
They attacked Bera, king of Sodom, Birsha, king of Gomorrah, Shinab, king of Admah, Shemeber, king of Zeboiim, and the king of Bela (otherwise known as Zoar).
3 Dukan waɗannan sarakuna na bayan nan suka haɗa kai a Kwarin Siddim (Teku Gishiri).
All these in the second group joined forces in the Valley of Siddim (the Dead Sea valley).
4 Shekara goma sha biyu suna bauta wa Kedorlayomer, amma a shekara ta sha uku sai suka yi tawaye.
They had been under the rule of Chedorlaomer for twelve years, but in the thirteenth year they rebelled against him.
5 A shekara ta goma sha huɗu, Kedorlayomer da sarakunan da suka haɗa kai da shi suka tafi suka cinye Refahiyawa a Ashterot Karnayim, Zuziyawa a Ham, Emawa a Shabe Kiriyatayim,
In the fourteenth year Chedorlaomer invaded, along with the kings in his alliance. They defeated the Rephaites in Ashteroth-karnaim, the Zuzites in Ham, the Emites in Shaveh-kiriathaim,
6 da Horiyawa a ƙasar tudun Seyir har zuwa El Faran kusa da hamada.
and the Horites in their hill country of Seir, all the way to El-paran, near the desert.
7 Sa’an nan suka juya suka tafi En Mishfat (wato, Kadesh), suka cinye dukan ƙasar Amalekawa, da kuma Amoriyawa waɗanda suke zaune a Hazazon Tamar.
Then they swung back through and attacked En-mishpat (otherwise known as Kadesh) and conquered the whole country belonging to the Amalekites, as well as the Amorites who lived in Hazazon-tamar.
8 Sai sarkin Sodom, sarkin Gomorra, sarkin Adma, sarkin Zeboyim da sarkin Bela (wato, Zowar), suka fita suka ja dāgā a Kwarin Siddim
Then the king of Sodom, the king of Gomorrah, the king of Admah, the king of Zeboiim, and the king of Bela (otherwise known as Zoar) marched out and prepared for battle in the Valley of Siddim.
9 gāba da Kedorlayomer sarkin Elam, Tidal sarkin Goyim, Amrafel sarkin Shinar da Ariyok sarkin Ellasar; sarakuna huɗu gāba da biyar.
They fought Chedorlaomer, king of Elam, Tidal, king of Goiim, Amraphel, king of Shinar, and Arioch, king of Ellasar—four kings on one side against five on the other.
10 Kwarin Siddim kuwa ya cika da ramummukan kwalta, sa’ad da sarakunan Sodom da Gomorra suka gudu kuwa, waɗansu mutane suka fāɗa cikin ramummukan kwaltan, sauran kuwa suka gudu zuwa tuddai.
There were many tar pits in the Valley of Siddim, and as the defeated kings of Sodom and Gomorrah ran away, some of their men fell into them while the rest ran to the hills.
11 Sarakunan nan huɗu suka washe dukan kayayyakin Sodom da Gomorra, da kuma dukan abincinsu, sa’an nan suka tafi.
The invaders took from Sodom and Gomorrah all their possessions and food and left.
12 Suka kuma kama Lot ɗan ɗan’uwan Abram, wanda yake zaune a Sodom, da kayayyakinsa, suka yi tafiyarsu.
They also captured Lot, Abram's nephew, and his possessions, because he was living in Sodom.
13 Sai wani wanda ya tsira, ya zo ya faɗa wa Abram mutumin Ibraniyawa. Abram kuwa yana zama kusa da manyan itatuwan Mamre, Mamre mutumin Amoriyawa ne ɗan’uwan Eshkol da Aner, su kuwa abokan Abram ne.
But one of those captured escaped and went and told Abram the Hebrew what had happened. Abram was living by the oaks of Mamre the Amorite, whose brothers were Eshcol and Aner. All of them were Abram's allies.
14 Da Abram ya ji cewa an kama danginsa, sai ya tara horarrun mutane 318, da aka haifa a gidansa, ya bi sawun sarakunan da suka tafi da Lot, har Dan.
When Abram found out that his nephew had been captured, he called together 318 fighting men who had been born in his household and chased after them all the way to Dan.
15 Da dad dare, Abram ya rarraba mutanensa don su fāɗa wa sarakunan nan, ya ɗibge su, ya kore su har zuwa Hoba, arewa da Damaskus.
There he divided his men into groups and attacked at night, defeating the enemy and chasing them as far as Hobah, north of Damascus.
16 Ya washe su da kuma dukan kayayyakinsu, ya kuma dawo da Lot danginsa da mallakarsa, tare da mata da sauran mutane.
Abram recovered all that had been taken, including Lot and his possessions, and also brought back the women and others who had been captured.
17 Bayan Abram ya dawo daga cin Kedorlayomer da sarakunan da suka haɗa kai da shi a yaƙi, sai sarkin Sodom ya fito don yă tarye Abram a Kwarin Shabe (wato, Kwarin Sarki).
When Abram returned after defeating Chedorlaomer and his allies, the king of Sodom came out to meet him at the Valley of Shaveh (or Valley of the King).
18 Sai Melkizedek sarkin Salem ya kawo burodi da ruwan inabi. Shi firist ne na Allah Mafi Ɗaukaka,
Melchizedek, king of Salem, brought out bread and wine. He was a priest of the Most High God.
19 ya albarkaci Abram yana cewa, “Allah Mafi Ɗaukaka Mahaliccin sama da ƙasa yă albarkace Abram.
He blessed Abram, telling him, “May Abram be blessed by the Most High God, Creator of heaven and earth.
20 Kuma albarka ta tabbata ga Allah Mafi Ɗaukaka wanda ya ba da maƙiyanka a hannunka.” Sa’an nan Abram ya ba shi kashi ɗaya bisa goma na kome.
May the Most High God be praised, who handed your enemies over to you.” Then Abram gave Melchizedek one tenth of everything.
21 Sarkin Sodom ya ce wa Abram, “Ka ba ni mutanena da ka ƙwace daga hannun sarakunan nan kawai, ka riƙe kayayyakin don kanka.”
The king of Sodom told Abram, “Let me have the people back, and you can keep everything else for yourself.”
22 Amma Abram ya ce, wa sarkin Sodom, “Na ɗaga hannu ga Ubangiji Allah Mafi Ɗaukaka, Mahaliccin sama da ƙasa, na riga na rantse
But Abram replied to the king of Sodom, “I raise my hand, making a solemn promise to the Lord, the Most High God, Creator of heaven and earth,
23 cewa ba zan karɓi kome da yake naka ba, ko zare ko maɗaurin takalma, don kada ka ce, ‘Na azurta Abram.’
that I refuse to take anything belonging to you, not a single thread or a sandal strap. Otherwise you might claim, ‘It was me who made Abram rich!’
24 Ba zan karɓi kome ba, sai dai abin da mutanena suka ci da kuma rabon mutanen da suka tafi tare da ni, ga Aner, Eshkol, da Mamre. Bari su ɗauki rabonsu.”
I won't take anything except what my men have eaten, and the share for those who accompanied me—Aner, Eshcol, and Mamre. Let them have their share.”