< Farawa 13 >

1 Saboda haka Abram ya haura daga Masar zuwa Negeb tare da matarsa, da dukan abin da yake da shi tare da Lot.
Abram monta donc de l’Égypte, lui, sa femme et tout ce qu’il avait, et Lot avec lui, vers la région australe.
2 Abram ya azurta ƙwarai da dabbobi, da azurfa, da kuma zinariya.
Or Abram était très riche en possession d’or et d’argent.
3 Daga Negeb, ya ci gaba da tafiyarsa a wurare dabam-dabam har ya kai tsakanin Betel da Ai, a inda dā ya kafa tentinsa na fari
Il s’en retourna par le même chemin qu’il était venu, du midi à Béthel, jusqu’au lieu où auparavant il avait planté sa tente, entre Béthel et Haï;
4 da kuma inda dā ya gina bagade. A can Abram ya kira bisa sunan Ubangiji.
Au lieu où il avait fait d’abord un autel, et il invoqua là le nom du Seigneur.
5 Lot wanda yake tafiya tare da Abram, shi ma yana da garken shanu da tumaki da kuma tentuna.
Mais Lot qui était avec Abram, avait aussi des troupeaux de brebis et de gros bétail, et des tentes.
6 Wannan ya sa har ƙasar ba tă ishe su yayinda suke zama tare ba, saboda mallakarsu ta yi yawa har ba za su iya zama tare ba.
Et ce pays ne leur permettait pas de demeurer ensemble; car leurs biens étaient nombreux, et ils ne pouvaient habiter en commun.
7 Rikici kuma ya tashi tsakanin masu kiwon dabbobin Abram da na Lot. Mazaunan ƙasar, a lokacin kuwa Kan’aniyawa da Ferizziyawa ne.
De là il s’éleva une querelle entre les pasteurs des troupeaux d’Abram et de Lot. Or en ce temps-là les Chananéens et les Phéréséens habitaient en ce pays.
8 Saboda haka Abram ya ce wa Lot, “Kada mu bar rikici yă shiga tsakaninmu, ko kuma tsakanin masu kiwon dabbobinka da nawa, gama mu’yan’uwa ne.
Abram dit donc à Lot: Je te prie, qu’il n’y ait pas de débat entre moi et toi, ni entre mes pasteurs et tes pasteurs; car nous sommes frères.
9 Ba ga dukan ƙasar tana gabanka ba? Bari mu rabu. In ka yi hagu sai ni in yi dama. In ka yi dama, sai ni in yi hagu.”
Voici que tout le pays est devant toi: sépare-toi de moi, je te conjure; si tu vas à gauche, j’irai à droite, et si tu choisis la droite, je prendrai la gauche.
10 Lot ya ɗaga idanunsa sama ya dubi kwarin Urdun, sai ya ga kwarin yana da ciyawa mai kyau ƙwarai sai ka ce lambun Ubangiji, kamar ƙasar Masar, wajajen Zowar. (Wannan fa kafin Ubangiji yă hallaka Sodom da Gomorra.)
C’est pourquoi Lot, les yeux levés, vit toute la contrée qui s’étendait le long du Jourdain, et qui, avant que le Seigneur eût détruit Sodome et Gomorrhe, était toute arrosée, comme le paradis du Seigneur, et comme l’Égypte, en venant vers Ségor.
11 Saboda haka sai Lot ya zaɓar wa kansa dukan kwarin Urdun, ya tashi ya nufi wajen gabas. Haka fa suka rabu da juna.
Lot choisit pour lui les environs du Jourdain, et s’éloigna de l’orient: c’est ainsi qu’ils se séparèrent l’un de l’autre.
12 Abram ya zauna a ƙasar Kan’ana, yayinda Lot ya zauna cikin biranen kwari, ya kafa tentunansa kusa da Sodom.
Abram habita dans la terre de Chanaan, et Lot demeura dans les villes qui étaient aux environs du Jourdain, et il habita dans Sodome.
13 Mutanen Sodom kuwa mugaye ne, sun aikata zunubi ƙwarai ga Ubangiji.
Or les habitants de Sodome étaient très méchants, et très grands pécheurs devant le Seigneur.
14 Bayan Lot ya rabu da Abram, sai Ubangiji ya ce wa Abram, “Ɗaga idanunka daga inda kake, ka dubi arewa da kudu, gabas da yamma.
Et le Seigneur dit à Abram, après que Lot fut séparé de lui: Lève les yeux et regarde du lieu où tu es maintenant, vers l’aquilon et le midi, vers l’orient et l’occident.
15 Dukan ƙasar da kake gani zan ba ka, kai da zuriyarka har abada.
Tout le pays que tu aperçois, je te le donnerai, à toi et à ta postérité pour toujours.
16 Zan sa zuriyarka tă yi yawa kamar ƙurar ƙasa, har in wani yana iya ƙidaya ƙurar, to, za a iya ƙidaya zuriyarka.
Je ferai ta postérité comme la poussière de la terre; si quelqu’un d’entre les hommes peut nombrer la poussière de la terre, il pourra aussi nombrer ta postérité.
17 Tafi, ka ratsa tsawo da fāɗin ƙasar, gama zan ba ka ita.”
Lève-toi, et parcours le pays en sa longueur et en sa largeur, parce que c’est à toi que je le dois donner.
18 Saboda haka Abram ya cire tentunansa, ya zo ya zauna kusa da manyan itatuwan Mamre a Hebron, inda ya gina bagade ga Ubangiji.
Levant donc sa tente, Abram vint et habita près de la vallée de Mambré, qui est en Hébron, et il bâtit là un autel au Seigneur.

< Farawa 13 >