< Farawa 13 >

1 Saboda haka Abram ya haura daga Masar zuwa Negeb tare da matarsa, da dukan abin da yake da shi tare da Lot.
So Abram and Sarai left Egypt, and they took along all his possessions, and Lot went with them to the Negev [Desert].
2 Abram ya azurta ƙwarai da dabbobi, da azurfa, da kuma zinariya.
Abram was very rich. He owned a lot of livestock, silver and gold.
3 Daga Negeb, ya ci gaba da tafiyarsa a wurare dabam-dabam har ya kai tsakanin Betel da Ai, a inda dā ya kafa tentinsa na fari
They continued traveling from place to place from the Negev [Desert] toward Bethel [town] to the place between Bethel and Ai where they had previously set up their tents,
4 da kuma inda dā ya gina bagade. A can Abram ya kira bisa sunan Ubangiji.
and where Abram had made a stone altar and worshiped Yahweh.
5 Lot wanda yake tafiya tare da Abram, shi ma yana da garken shanu da tumaki da kuma tentuna.
Lot, who was traveling with Abram, also had flocks of sheep and goats and herds of cattle, and tents.
6 Wannan ya sa har ƙasar ba tă ishe su yayinda suke zama tare ba, saboda mallakarsu ta yi yawa har ba za su iya zama tare ba.
But they had so many animals that they could not all stay in the same area. There was not enough land to provide water and food for all their animals.
7 Rikici kuma ya tashi tsakanin masu kiwon dabbobin Abram da na Lot. Mazaunan ƙasar, a lokacin kuwa Kan’aniyawa da Ferizziyawa ne.
Furthermore, the descendants of Canaan and Perizzi were also living in that area, and the land really belonged to them. And the men who took care of Abram’s animals started quarreling with the men who took care of Lot’s animals.
8 Saboda haka Abram ya ce wa Lot, “Kada mu bar rikici yă shiga tsakaninmu, ko kuma tsakanin masu kiwon dabbobinka da nawa, gama mu’yan’uwa ne.
So Abram said to Lot, “Since we are close relatives, it is not good for us two to quarrel, or for the men who take care of your animals to quarrel with the men who take care of my animals.
9 Ba ga dukan ƙasar tana gabanka ba? Bari mu rabu. In ka yi hagu sai ni in yi dama. In ka yi dama, sai ni in yi hagu.”
There is plenty of land for both of us. So we should separate. You can choose whatever part you want [RHQ]. If you want the area over there, I will stay here. If you want the area here, I will go over there.”
10 Lot ya ɗaga idanunsa sama ya dubi kwarin Urdun, sai ya ga kwarin yana da ciyawa mai kyau ƙwarai sai ka ce lambun Ubangiji, kamar ƙasar Masar, wajajen Zowar. (Wannan fa kafin Ubangiji yă hallaka Sodom da Gomorra.)
Lot looked around toward Zoar [town], and saw that there was plenty of water all over the plain near the Jordan [River]. It was like the park/garden in Eden, and like the land in Egypt. [That was before Yahweh destroyed [the cities of] Sodom and Gomorrah which were on that plain.]
11 Saboda haka sai Lot ya zaɓar wa kansa dukan kwarin Urdun, ya tashi ya nufi wajen gabas. Haka fa suka rabu da juna.
So Lot chose the land in the plain of the Jordan [River]. He left his uncle, Abram, and moved east.
12 Abram ya zauna a ƙasar Kan’ana, yayinda Lot ya zauna cikin biranen kwari, ya kafa tentunansa kusa da Sodom.
Abram stayed in the Canaan area, and Lot started to live near the cities in the plain of the Jordan [River], and he set up his tents near Sodom [city].
13 Mutanen Sodom kuwa mugaye ne, sun aikata zunubi ƙwarai ga Ubangiji.
[You need to know that] people who lived there were extremely wicked.
14 Bayan Lot ya rabu da Abram, sai Ubangiji ya ce wa Abram, “Ɗaga idanunka daga inda kake, ka dubi arewa da kudu, gabas da yamma.
After Abram and Lot separated, Yahweh said to Abram, “Look around at this whole area where you are. Look north and south, look east and west.
15 Dukan ƙasar da kake gani zan ba ka, kai da zuriyarka har abada.
I will give to you and your descendants all the land that you see; I will give it to you forever.
16 Zan sa zuriyarka tă yi yawa kamar ƙurar ƙasa, har in wani yana iya ƙidaya ƙurar, to, za a iya ƙidaya zuriyarka.
I will cause your descendants to be as numerous as particles of dust! [It will be easier] to count the particles of dust than it will be to count your descendants [HYP].
17 Tafi, ka ratsa tsawo da fāɗin ƙasar, gama zan ba ka ita.”
Walk through the land in every direction, because I am going to give it all to you.”
18 Saboda haka Abram ya cire tentunansa, ya zo ya zauna kusa da manyan itatuwan Mamre a Hebron, inda ya gina bagade ga Ubangiji.
So Abram [and his men] took down their tents and moved to Hebron and started to live by the huge trees [at the town] Mamre. He placed a stone altar there to [make sacrifices to] Yahweh.

< Farawa 13 >