< Farawa 13 >

1 Saboda haka Abram ya haura daga Masar zuwa Negeb tare da matarsa, da dukan abin da yake da shi tare da Lot.
So Abram left Egypt and went back into the Negev along with Sarai, Lot, and everyone with them, as well as all their possessions.
2 Abram ya azurta ƙwarai da dabbobi, da azurfa, da kuma zinariya.
Abram was very rich, having many herds of livestock and a great deal of silver and gold.
3 Daga Negeb, ya ci gaba da tafiyarsa a wurare dabam-dabam har ya kai tsakanin Betel da Ai, a inda dā ya kafa tentinsa na fari
He left the Negev and traveled in stages to Bethel, back to the place where he'd camped before, between Bethel and Ai.
4 da kuma inda dā ya gina bagade. A can Abram ya kira bisa sunan Ubangiji.
This was where he'd first built an altar. He worshiped the Lord there as he had done previously.
5 Lot wanda yake tafiya tare da Abram, shi ma yana da garken shanu da tumaki da kuma tentuna.
Lot, who was traveling with Abram, also had many flocks, herds, and tents,
6 Wannan ya sa har ƙasar ba tă ishe su yayinda suke zama tare ba, saboda mallakarsu ta yi yawa har ba za su iya zama tare ba.
so much so that the available land couldn't support both of them—they had so much livestock they couldn't stay together anymore.
7 Rikici kuma ya tashi tsakanin masu kiwon dabbobin Abram da na Lot. Mazaunan ƙasar, a lokacin kuwa Kan’aniyawa da Ferizziyawa ne.
Abram's and Lot's herdsmen were arguing, and in addition the Canaanites and Perizzites were also living in the land at that time.
8 Saboda haka Abram ya ce wa Lot, “Kada mu bar rikici yă shiga tsakaninmu, ko kuma tsakanin masu kiwon dabbobinka da nawa, gama mu’yan’uwa ne.
So Abram said to Lot, “Please don't let's have arguments between us, or between our herdsmen, because we're family.
9 Ba ga dukan ƙasar tana gabanka ba? Bari mu rabu. In ka yi hagu sai ni in yi dama. In ka yi dama, sai ni in yi hagu.”
You see all this land that's available right in front of you? We have to split up. If you choose to go to the left, I'll go to the right. If you choose to go to the right, I'll go to the left.”
10 Lot ya ɗaga idanunsa sama ya dubi kwarin Urdun, sai ya ga kwarin yana da ciyawa mai kyau ƙwarai sai ka ce lambun Ubangiji, kamar ƙasar Masar, wajajen Zowar. (Wannan fa kafin Ubangiji yă hallaka Sodom da Gomorra.)
Lot looked over the whole Jordan valley towards Zoar, and saw that it was well-watered, looking like the Garden of Eden, like the land of Egypt. (This was before the Lord destroyed Sodom and Gomorrah.)
11 Saboda haka sai Lot ya zaɓar wa kansa dukan kwarin Urdun, ya tashi ya nufi wajen gabas. Haka fa suka rabu da juna.
So Lot chose the whole Jordan valley and went east, and the two separated from each other.
12 Abram ya zauna a ƙasar Kan’ana, yayinda Lot ya zauna cikin biranen kwari, ya kafa tentunansa kusa da Sodom.
Abram went to live in the land of Canaan, while Lot settled down among the towns in the valley, setting up his tents near Sodom.
13 Mutanen Sodom kuwa mugaye ne, sun aikata zunubi ƙwarai ga Ubangiji.
(The people of Sodom were very wicked, committing terrible sins that offended the Lord.)
14 Bayan Lot ya rabu da Abram, sai Ubangiji ya ce wa Abram, “Ɗaga idanunka daga inda kake, ka dubi arewa da kudu, gabas da yamma.
After separating from Lot, the Lord told Abram, “Look around you from where you're standing, to the north, south, east, and west.
15 Dukan ƙasar da kake gani zan ba ka, kai da zuriyarka har abada.
I'm giving all this land you see to you and your descendants forever.
16 Zan sa zuriyarka tă yi yawa kamar ƙurar ƙasa, har in wani yana iya ƙidaya ƙurar, to, za a iya ƙidaya zuriyarka.
You will have so many descendants that they'll be like the dust of the earth. If anyone could count dust then they could count the number of your descendants!
17 Tafi, ka ratsa tsawo da fāɗin ƙasar, gama zan ba ka ita.”
Go and walk through the whole land in all directions because I'm giving it to you.”
18 Saboda haka Abram ya cire tentunansa, ya zo ya zauna kusa da manyan itatuwan Mamre a Hebron, inda ya gina bagade ga Ubangiji.
So Abram went to live at Hebron, setting up his tents among the oaks at Mamre, where he built an altar to the Lord.

< Farawa 13 >