< Farawa 12 >
1 Ubangiji ya ce wa Abram, “Tashi ka bar ƙasarka, da mutanenka, da iyalin mahaifinka, ka tafi ƙasar da zan nuna maka.
Now the LORD had said to Abram, Depart from thy country, and from thy kindred, and from thy father’s house, to a land that I will show thee:
2 “Zan mai da kai al’umma mai girma, zan kuma albarkace ka; zan sa sunanka yă zama mai girma, ka kuma zama sanadin albarka.
And I will make of thee a great nation, and I will bless thee, and make thy name great; and thou shalt be a blessing:
3 Zan albarkaci duk wanda ya albarkace ka, in kuma la’anci duk wanda ya la’anta ka, dukan mutanen duniya za su sami albarka ta wurinka.”
And I will bless them that bless thee, and curse him that curseth thee: and in thee shall all families of the earth be blessed.
4 Saboda haka Abram ya tashi yadda Ubangiji ya faɗa masa; Lot ma ya tafi tare da shi. Abram yana da shekaru 75, sa’ad da ya tashi daga Haran.
So Abram departed, as the LORD had spoken to him; and Lot went with him: and Abram was seventy and five years old when he departed from Haran.
5 Abram ya ɗauki matarsa Saira da Lot ɗan ɗan’uwansa, da dukan mallakar da suka tattara, da kuma mutanen da suka samu a Haran, suka kama hanya zuwa ƙasar Kan’ana.
And Abram took Sarai his wife, and Lot his brother’s son, and all their substance that they had gathered, and the souls that they had gotten in Haran; and they went to go forth into the land of Canaan; and into the land of Canaan they came.
6 Abram ya ratsa ƙasar har zuwa wurin babban itace na More a Shekem. A lokacin Kan’aniyawa suna a ƙasar.
And Abram passed through the land to the place of Sichem, to the plain of Moreh. And the Canaanite was then in the land.
7 Ubangiji ya bayyana ga Abram ya ce, “Ga zuriyarka ne zan ba da wannan ƙasa.” Saboda haka Abram ya gina bagade a can ga Ubangiji, wanda ya bayyana gare shi.
And the LORD appeared to Abram, and said, To thy seed will I give this land: and there he built an altar to the LORD, who appeared to him.
8 Daga can, ya ci gaba zuwa wajen tuddai a gabashin Betel ya kafa tentinsa, Betel yana yamma, Ai, kuma a gabas. A can ya gina bagade ga Ubangiji ya kuma kira bisa sunan Ubangiji.
And he departed from there to a mountain on the east of Bethel, and pitched his tent, having Bethel on the west, and Ai on the east: and there he built an altar to the LORD, and called upon the name of the LORD.
9 Sa’an nan Abram ya tashi ya ci gaba da tafiya zuwa wajen Negeb.
And Abram journeyed, going on still toward the south.
10 To, a lokacin, an yi yunwa a ƙasar, sai Abram ya gangara zuwa Masar don yă zauna a can na ɗan lokaci, domin yunwa ta yi tsanani.
And there was a famine in the land: and Abram went down into Egypt to dwell there; for the famine was grievous in the land.
11 Yayinda yana gab da shiga Masar, sai ya ce wa matarsa Saira, “Na sani ke kyakkyawar mace ce.
And it came to pass, when he had come near to enter into Egypt, that he said to Sarai his wife, Behold now, I know that thou art a fair woman to look upon:
12 Sa’ad da Masarawa suka ganki, za su ce, ‘Wannan matarsa ce.’ Za su kuwa kashe ni, su bar ki da rai.
Therefore it shall come to pass, when the Egyptians shall see thee, that they shall say, This is his wife: and they will kill me, but they will save thee alive.
13 Saboda haka ki ce ke’yar’uwata ce, domin ta dalilinki a mutunta ni, a kuma bar ni da rai.”
Say, I pray thee, thou art my sister: that it may be well with me for thy sake; and my soul shall live because of thee.
14 Sa’ad da Abram ya isa Masar, Masarawa suka ga cewa Saira kyakkyawa mace ce ƙwarai.
And it came to pass, that, when Abram had come into Egypt, the Egyptians beheld the woman that she was very fair.
15 Sa’ad da fadawan Fir’auna suka gan ta kuwa, sai suka yabe ta wajen Fir’auna, aka kuwa kawo ta cikin fadarsa.
The princes also of Pharaoh saw her, and commended her before Pharaoh: and the woman was taken into Pharaoh’s house.
16 Ya mutunta Abram sosai saboda ita, Abram kuwa ya mallaki tumaki da shanu, da jakuna maza da mata, da bayi maza da mata, da kuma raƙuma.
And he treated Abram well for her sake: and he had sheep, and oxen, and male donkeys, and male and female servants, and female donkeys, and camels.
17 Amma Ubangiji ya wahalar da Fir’auna da gidansa da cututtuka masu zafi saboda Saira, matar Abram.
And the LORD afflicted Pharaoh and his house with great plagues because of Sarai Abram’s wife.
18 Saboda haka Fir’auna ya kira Abram ya ce, “Me ke nan ka yi mini? Me ya sa ba ka faɗa mini cewa ita matarka ce ba?
And Pharaoh called Abram, and said, What is this that thou hast done to me? why didst thou not tell me that she is thy wife?
19 Don me ka ruɗe ni cewa, ‘Ita’yar’uwata ce,’ har na ɗauke ta tă zama matata? To, ga matarka. Ɗauke ta ka tafi.”
Why saidst thou, She is my sister? so I might have taken her to me for a wife: now therefore behold thy wife, take her, and go thy way.
20 Sa’an nan Fir’auna ya yi wa mutanensa umarni a kan Abram, suka kuwa sallame shi tare da matarsa da kuma dukan abin da yake da shi.
And Pharaoh commanded his men concerning him: and they sent him away, and his wife, and all that he had.