< Farawa 12 >

1 Ubangiji ya ce wa Abram, “Tashi ka bar ƙasarka, da mutanenka, da iyalin mahaifinka, ka tafi ƙasar da zan nuna maka.
Then the LORde sayd vnto Abra Gett the out of thy contre and from thy kynred and out of thy fathers house into a londe which I wyll shewe the.
2 “Zan mai da kai al’umma mai girma, zan kuma albarkace ka; zan sa sunanka yă zama mai girma, ka kuma zama sanadin albarka.
And I wyll make of the a myghtie people and wyll blesse the and make thy name grete that thou mayst be a blessinge.
3 Zan albarkaci duk wanda ya albarkace ka, in kuma la’anci duk wanda ya la’anta ka, dukan mutanen duniya za su sami albarka ta wurinka.”
And I wyll blesse the that blesse the ad curse the that curse the. And in the shall be blessed all the generations of the erth.
4 Saboda haka Abram ya tashi yadda Ubangiji ya faɗa masa; Lot ma ya tafi tare da shi. Abram yana da shekaru 75, sa’ad da ya tashi daga Haran.
And Abram wet as the LORde badd hym and Lot went wyth him. Abram was. lxxv. yere olde when he went out of Haran.
5 Abram ya ɗauki matarsa Saira da Lot ɗan ɗan’uwansa, da dukan mallakar da suka tattara, da kuma mutanen da suka samu a Haran, suka kama hanya zuwa ƙasar Kan’ana.
And Abram toke Sarai his wyfe ad Lot his brothers sonne wyth all their goodes which they had goten and soulles which they had begoten in Haran. And they departed to goo in to the lade of Chanaan. And when they were come in to the lande of Chanaan
6 Abram ya ratsa ƙasar har zuwa wurin babban itace na More a Shekem. A lokacin Kan’aniyawa suna a ƙasar.
Abram went furth in to the lade tyll he came vnto a place called Sychem and vnto the oke of More. And the Canaanytes dwelled then in the lande.
7 Ubangiji ya bayyana ga Abram ya ce, “Ga zuriyarka ne zan ba da wannan ƙasa.” Saboda haka Abram ya gina bagade a can ga Ubangiji, wanda ya bayyana gare shi.
Then the LORde apeared vnto Abram ad sayd: vnto thy seed wyll I geue thys lade. And he buylded an aultere there vnto the LORDE which apeared to hym.
8 Daga can, ya ci gaba zuwa wajen tuddai a gabashin Betel ya kafa tentinsa, Betel yana yamma, Ai, kuma a gabas. A can ya gina bagade ga Ubangiji ya kuma kira bisa sunan Ubangiji.
Then departed he thence vnto a mountayne that lyeth on the east syde of BETHEL and pytched hys tente: BETHEL beynge on the west syde and Ay on the east: And he buylded there an aulter vnto the LORde and called on the name of ye LORde.
9 Sa’an nan Abram ya tashi ya ci gaba da tafiya zuwa wajen Negeb.
And than Abram departed and toke his iourney southwarde
10 To, a lokacin, an yi yunwa a ƙasar, sai Abram ya gangara zuwa Masar don yă zauna a can na ɗan lokaci, domin yunwa ta yi tsanani.
After thys there came a derth in the lande. And Abram went doune in to Egipte to soiourne there for the derth was sore in the lande.
11 Yayinda yana gab da shiga Masar, sai ya ce wa matarsa Saira, “Na sani ke kyakkyawar mace ce.
And when he was come nye for to entre in to Egipte he sayd vnto sarai his wife. Beholde I knowe that thou art a fayre woman to loke apo.
12 Sa’ad da Masarawa suka ganki, za su ce, ‘Wannan matarsa ce.’ Za su kuwa kashe ni, su bar ki da rai.
It wyll come to passe therfore whe the Egiptians see the that they wyll say: she is his wyfe. And so shall they sley me and save the.
13 Saboda haka ki ce ke’yar’uwata ce, domin ta dalilinki a mutunta ni, a kuma bar ni da rai.”
saye I praye the therfore that thou art my sister that I maye fare the better by reason of the and that my soule maye lyue for thy sake.
14 Sa’ad da Abram ya isa Masar, Masarawa suka ga cewa Saira kyakkyawa mace ce ƙwarai.
As soone as he came in to Egipte the Egiptias sawe the woman that she was very fayre.
15 Sa’ad da fadawan Fir’auna suka gan ta kuwa, sai suka yabe ta wajen Fir’auna, aka kuwa kawo ta cikin fadarsa.
And Pharaos lordes sawe hir also and praysed hir vnto Pharao: So that she was taken in to Pharaos house
16 Ya mutunta Abram sosai saboda ita, Abram kuwa ya mallaki tumaki da shanu, da jakuna maza da mata, da bayi maza da mata, da kuma raƙuma.
which entreated Abram well for hir sake so that he had shepe oxsen ad he asses men seruantes mayde seruates she asses and camels.
17 Amma Ubangiji ya wahalar da Fir’auna da gidansa da cututtuka masu zafi saboda Saira, matar Abram.
But God plaged Pharao and his house wyth grete plages because of Sarai Abrams wyfe.
18 Saboda haka Fir’auna ya kira Abram ya ce, “Me ke nan ka yi mini? Me ya sa ba ka faɗa mini cewa ita matarka ce ba?
Then Pharao called Abram and sayd: why hast thou thus dealt with me? Wherfore toldest thou me not that she was thy wyfe?
19 Don me ka ruɗe ni cewa, ‘Ita’yar’uwata ce,’ har na ɗauke ta tă zama matata? To, ga matarka. Ɗauke ta ka tafi.”
Why saydest thou that she was thy sister and causedest me to take hyr to my wyfe? But now loo there is the wife take hir ad be walkynge.
20 Sa’an nan Fir’auna ya yi wa mutanensa umarni a kan Abram, suka kuwa sallame shi tare da matarsa da kuma dukan abin da yake da shi.
Pharao also gaue a charge vnto his men over Abram to leade hym out wyth his wyfe and all that he had.

< Farawa 12 >