< Farawa 12 >
1 Ubangiji ya ce wa Abram, “Tashi ka bar ƙasarka, da mutanenka, da iyalin mahaifinka, ka tafi ƙasar da zan nuna maka.
Now Jehovah said to Abram, Get thee out of thy country, and from thy kindred, and from thy father's house, to the land that I will show thee.
2 “Zan mai da kai al’umma mai girma, zan kuma albarkace ka; zan sa sunanka yă zama mai girma, ka kuma zama sanadin albarka.
And I will make of thee a great nation, and I will bless thee, and make thy name great, and be thou a blessing.
3 Zan albarkaci duk wanda ya albarkace ka, in kuma la’anci duk wanda ya la’anta ka, dukan mutanen duniya za su sami albarka ta wurinka.”
And I will bless those who bless thee, and he who curses thee I will curse. And in thee shall all the families of the earth be blessed.
4 Saboda haka Abram ya tashi yadda Ubangiji ya faɗa masa; Lot ma ya tafi tare da shi. Abram yana da shekaru 75, sa’ad da ya tashi daga Haran.
So Abram went as Jehovah had spoken to him, and Lot went with him. And Abram was seventy-five years old when he departed out of Haran.
5 Abram ya ɗauki matarsa Saira da Lot ɗan ɗan’uwansa, da dukan mallakar da suka tattara, da kuma mutanen da suka samu a Haran, suka kama hanya zuwa ƙasar Kan’ana.
And Abram took Sarai his wife, and Lot his brother's son, and all their substance that they had gathered, and the souls that they had gotten in Haran, and they went forth to go into the land of Canaan. And they came into the land of Canaan.
6 Abram ya ratsa ƙasar har zuwa wurin babban itace na More a Shekem. A lokacin Kan’aniyawa suna a ƙasar.
And Abram passed through the land to the place of Shechem, to the oak of Moreh. And the Canaanite was then in the land.
7 Ubangiji ya bayyana ga Abram ya ce, “Ga zuriyarka ne zan ba da wannan ƙasa.” Saboda haka Abram ya gina bagade a can ga Ubangiji, wanda ya bayyana gare shi.
And Jehovah appeared to Abram, and said, I will give this land to thy seed. And there he built an altar to Jehovah, who appeared to him.
8 Daga can, ya ci gaba zuwa wajen tuddai a gabashin Betel ya kafa tentinsa, Betel yana yamma, Ai, kuma a gabas. A can ya gina bagade ga Ubangiji ya kuma kira bisa sunan Ubangiji.
And he moved from there to the mountain on the east of Bethel, and pitched his tent, having Bethel on the west, and Ai on the east. And there he built an altar to Jehovah, and called upon the name of Jehovah.
9 Sa’an nan Abram ya tashi ya ci gaba da tafiya zuwa wajen Negeb.
And Abram journeyed, going on still toward the South.
10 To, a lokacin, an yi yunwa a ƙasar, sai Abram ya gangara zuwa Masar don yă zauna a can na ɗan lokaci, domin yunwa ta yi tsanani.
And there was a famine in the land. And Abram went down into Egypt to sojourn there, for the famine was severe in the land.
11 Yayinda yana gab da shiga Masar, sai ya ce wa matarsa Saira, “Na sani ke kyakkyawar mace ce.
And it came to pass, when he came near to enter into Egypt, that he said to Sarai his wife, Behold now, I know that thou are a fair woman to look upon.
12 Sa’ad da Masarawa suka ganki, za su ce, ‘Wannan matarsa ce.’ Za su kuwa kashe ni, su bar ki da rai.
And it shall come to pass, when the Egyptians shall see thee, that they shall say, This is his wife. And they will kill me, but they will save thee alive.
13 Saboda haka ki ce ke’yar’uwata ce, domin ta dalilinki a mutunta ni, a kuma bar ni da rai.”
Say, I pray thee, thou are my sister, that it may be well with me for thy sake, and that my soul may live because of thee.
14 Sa’ad da Abram ya isa Masar, Masarawa suka ga cewa Saira kyakkyawa mace ce ƙwarai.
And it came to pass, that, when Abram came into Egypt, the Egyptians beheld the woman that she was very fair.
15 Sa’ad da fadawan Fir’auna suka gan ta kuwa, sai suka yabe ta wajen Fir’auna, aka kuwa kawo ta cikin fadarsa.
And the princes of Pharaoh saw her, and praised her to Pharaoh. And the woman was taken into Pharaoh's house.
16 Ya mutunta Abram sosai saboda ita, Abram kuwa ya mallaki tumaki da shanu, da jakuna maza da mata, da bayi maza da mata, da kuma raƙuma.
And he dealt well with Abram for her sake. And he had sheep, and oxen, and he-donkeys, and men-servants, and maid-servants, and she-donkeys, and camels.
17 Amma Ubangiji ya wahalar da Fir’auna da gidansa da cututtuka masu zafi saboda Saira, matar Abram.
And Jehovah plagued Pharaoh and his house with great plagues because of Sarai, Abram's wife.
18 Saboda haka Fir’auna ya kira Abram ya ce, “Me ke nan ka yi mini? Me ya sa ba ka faɗa mini cewa ita matarka ce ba?
And Pharaoh called Abram, and said, What is this that thou have done to me? Why did thou not tell me that she was thy wife?
19 Don me ka ruɗe ni cewa, ‘Ita’yar’uwata ce,’ har na ɗauke ta tă zama matata? To, ga matarka. Ɗauke ta ka tafi.”
Why did thou say, She is my sister, so that I took her to be my wife? Now therefore behold thy wife. Take her, and go thy way.
20 Sa’an nan Fir’auna ya yi wa mutanensa umarni a kan Abram, suka kuwa sallame shi tare da matarsa da kuma dukan abin da yake da shi.
And Pharaoh gave men command concerning him. And they brought him on the way, and his wife, and all that he had.