< Farawa 11 >

1 To, a lokacin, yaren mutanen duniya ɗaya ne, maganarsu kuma ɗaya ce.
En ese tiempo se hablaba en todo el mundo un solo idioma y todos usaban palabras con el mismo significado.
2 Yayinda mutane suke ta yin ƙaura zuwa gabas, sai suka sami fili a Shinar, suka zauna a can.
Al trasladarse hacia el oriente, descubrieron una llanura en la región del Sinar y se asentaron allí.
3 Suka ce wa juna, “Ku zo, mu yi tubula, mu gasa su sosai.” Suka yi amfani da tubula a maimakon duwatsu, kwalta kuma a maimakon laka.
Y se dijeron unos a otros: “Vengan, juntemos ladrillos y cocinémoslos con fuego”. (Usaron ladrillo en lugar de piedra, y alquitrán en lugar de cemento).
4 Sa’an nan suka ce, “Ku zo, mu gina wa kanmu birni da hasumiyar da za tă kai har sammai, domin mu yi wa kanmu suna, don kada mu warwatsu ko’ina a doron ƙasa.”
Y entonces dijeron: “Construyamos ahora una ciudad para nosotros mismos con una torre cuya cúspide llegue hasta el cielo. Así lograremos tener una gran reputación y no andaremos dispersos por todo el mundo”.
5 Sai Ubangiji ya sauko don yă ga birni da kuma hasumiyar da mutanen suke gini.
Pero el Señor descendió para mirar la ciudad y la torre que estas personas estaban construyendo.
6 Ubangiji ya ce, “Ga su, su jama’a ɗaya ce, su duka kuwa harshensu guda ne. Wannan kuwa masomi ne kawai na abin da za su iya yi, babu kuma abin da suka yi shirya yi da ba za su iya yi ba.
Y el Señor dijo: “Miren cómo estas personas están unidas y hablando el mismo idioma. ¡Si pueden lograr todo esto tan solo comenzando, nada les será imposible si se fijan un propósito!
7 Zo, mu sauka, mu rikitar da harshensu don kada su fahimci juna.”
Necesitamos bajar allí y confundir su idioma para que no puedan entender lo que se dicen unos a otros”.
8 Saboda haka Ubangiji ya watsar da su daga wurin zuwa ko’ina a doron ƙasa, suka kuwa daina gina birnin.
Y entonces el Señor los expulsó de allí e hizo que se dispersaran por todo el mundo, y dejaron de construir la ciudad.
9 Shi ya sa aka kira birnin Babel, domin a can ne Ubangiji ya rikitar da harshen dukan duniya. Daga can Ubangiji ya watsar da su ko’ina a doron ƙasa.
Por eso la ciudad fue llamada Babel, porque el Señor confundió el idioma que se hablaba en el mundo.
10 Wannan shi ne labarin Shem. Shekara biyu bayan ambaliya, sa’ad da Shem ya yi shekara 100, sai ya haifi Arfakshad.
La siguiente es la genealogía de Sem. Cuando Sem tuvo 100 años, nació su hijo Arfaxad. Esto sucedió dos años después del diluvio.
11 Bayan ya haifi Arfakshad, Shem ya yi shekara 500, ya haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
Después del nacimiento de Arfaxad, Sem vivió 500 años más y tuvo más hijos e hijas.
12 Sa’ad da Arfakshad ya yi shekara 35, sai ya haifi Shela.
Cuando Arfaxad tuvo 35 años, nació su hijo Selaj.
13 Bayan ya haifi Shela kuwa, Arfakshad ya yi shekara 403, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
Después del nacimiento de Selaj, Arfaxad vivió 403 años más y tuvo más hijos e hijas.
14 Sa’ad da Shela ya yi shekaru 30, sai ya haifi Eber.
Cuando Selaj tuvo 30 años, nació su hijo Éber.
15 Bayan ya haifi Eber, Shela ya yi shekara 403, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
Después del nacimiento de Éber, Selaj vivió 403 años más y tuvo más hijos e hijas.
16 Sa’ad da Eber ya yi shekaru 34, sai ya haifi Feleg.
Cuando Éber tuvo 34 años, nació su hijo Peleg.
17 Bayan ya haifi Feleg, Eber ya yi shekara 430, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
Después del nacimiento de Peleg, Éber vivió 430 años más y tuvo más hijos e hijas.
18 Sa’ad da Feleg ya yi shekaru 30, sai ya haifi Reyu.
Cuando Peleg tuvo 30 años, nació su hijo Reú.
19 Bayan ya haifi Reyu, Feleg ya yi shekara 209, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
Después del nacimiento de Reú, Peleg vivió 209 años más y tuvo más hijos e hijas.
20 Sa’ad da Reyu ya yi shekaru 32, sai ya haifi Serug.
Cuando Reú tuvo 32 años, nació su hijo Serug.
21 Bayan ya haifi Serug, Reyu ya yi shekara 207, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
Después del nacimiento de Serug, Reú vivió 207 años más, y tuvo más hijos e hijas.
22 Sa’ad da Serug ya yi shekaru 30, sai ya haifi Nahor.
Cuando Serug tuvo 30 años, nació su hijo Nacor.
23 Bayan ya haifi Nahor, Serug ya yi shekara 200, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
Después del nacimiento de Nacor, Serug vivió 200 años más y tuvo más hijos e hijas.
24 Sa’ad da Nahor ya yi shekaru 29, sai ya haifi Tera.
Cuando Nacor tuvo 29 años, nació su hijo Téraj.
25 Bayan ya haifi Tera, Nahor ya yi shekara 119, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
Después del nacimiento de Téraj, Nacor vivió 119 años más, y tuvo más hijos e hijas.
26 Bayan Tera ya yi shekaru 70, sai ya haifi Abram, Nahor da Haran.
Cuando Téraj tuvi 70 años, nacieron sus hijos Abram, Nacor y Harán.
27 Wannan ita ce zuriyar Tera. Tera ya haifi Abram, Nahor da Haran. Haran kuma ya haifi Lot.
Esta es la genealogía de Téraj. Téraj fue el padre de Abram, Nacor y Harán. Harán fue el padre de Lot.
28 Yayinda mahaifinsa Tera yana da rai, Haran ya rasu a Ur ta Kaldiyawa, a ƙasar haihuwarsa.
Sin embargo, Harán murió cuando si padre Téraj aún vivía en Ur de los caldeos, la tierra donde nació.
29 Abram da Nahor suka yi aure. Sunan matar Abram, Saira ne, sunan matar Nahor kuwa Milka; ita’yar Haran ce, mahaifin Milka da Iska.
Tanto Abram como Nacor se casaron. La esposa de Abram se llamaba Sarai, y la esposa de Nacor se llamaba Milca. (Milca era hija de Harán, quien era padre tanto de Milca como de Jiscá).
30 Saira kuwa bakararriya ce, ba ta da yara.
Sarai no podia quedar embarazada, por lo tanto no tenía hijos.
31 Tera ya ɗauki ɗansa Abraham, jikansa Lot ɗan Haran, da surukarsa Saira, matar Abram, tare kuwa suka bar Ur ta Kaldiyawa, don su tafi Kan’ana. Amma sa’ad da suka zo Haran sai suka zauna a can.
Téraj tomó a su hijo Abram, a su nieto Lot, (quien era el hijo de Arám), a su nuera Sarai, (que era la esposa de su hijo Abram), y se fue de Ur de los caldeos para mudarse a Canaán. Llegaron hasta Harán y se quedaron a vivir allí.
32 Tera yi shekaru 205, ya kuma mutu a Haran.
Téraj vivió 205 años y murió en Harán.

< Farawa 11 >