< Farawa 11 >
1 To, a lokacin, yaren mutanen duniya ɗaya ne, maganarsu kuma ɗaya ce.
Die ganze Erde aber hatte eine Sprache und einerlei Worte.
2 Yayinda mutane suke ta yin ƙaura zuwa gabas, sai suka sami fili a Shinar, suka zauna a can.
Als sie von Osten herzogen, fanden sie im Lande Sinear eine Ebene und ließen sich darin nieder.
3 Suka ce wa juna, “Ku zo, mu yi tubula, mu gasa su sosai.” Suka yi amfani da tubula a maimakon duwatsu, kwalta kuma a maimakon laka.
Und sie sprachen zueinander: "Auf! Laßt uns Luftziegel streichen und Backsteine brennen!" Und der Ziegel diente ihnen als Baustein; das Erdpech aber hatte ihnen als Mörtel gedient.
4 Sa’an nan suka ce, “Ku zo, mu gina wa kanmu birni da hasumiyar da za tă kai har sammai, domin mu yi wa kanmu suna, don kada mu warwatsu ko’ina a doron ƙasa.”
Sie sprachen: "Auf! Bauen wir uns eine Stadt und einen Turm mit einer Spitze bis zum Himmel, und machen wir uns eine Wohnstatt, daß wir uns nicht über die ganze Erde zerstreuen!"
5 Sai Ubangiji ya sauko don yă ga birni da kuma hasumiyar da mutanen suke gini.
Der Herr aber stieg herab, die Stadt und den Turm zu beschauen, den die Menschenkinder gebaut.
6 Ubangiji ya ce, “Ga su, su jama’a ɗaya ce, su duka kuwa harshensu guda ne. Wannan kuwa masomi ne kawai na abin da za su iya yi, babu kuma abin da suka yi shirya yi da ba za su iya yi ba.
Da sprach der Herr: "Fürwahr! Ein Volk sind sie und haben alle dieselbe Sprache, und dies ist nur der Anfang ihres Tuns, und fortan wäre ihnen nichts verwehrt, was immer sie nur planen.
7 Zo, mu sauka, mu rikitar da harshensu don kada su fahimci juna.”
Auf nun! Wir wollen jetzt hinab und ihre Sprache mischen, daß keiner je des anderen Sprache mehr verstehe."
8 Saboda haka Ubangiji ya watsar da su daga wurin zuwa ko’ina a doron ƙasa, suka kuwa daina gina birnin.
So zerstreute sie der Herr von dort über die ganze Erde, und sie mußten es lassen, die Stadt auszubauen.
9 Shi ya sa aka kira birnin Babel, domin a can ne Ubangiji ya rikitar da harshen dukan duniya. Daga can Ubangiji ya watsar da su ko’ina a doron ƙasa.
Darum nennt man sie Babel; denn dort hat der Herr die Sprache der ganzen Erde gemischt, und von dort hat der Herr sie über die ganze Erde zerstreut.
10 Wannan shi ne labarin Shem. Shekara biyu bayan ambaliya, sa’ad da Shem ya yi shekara 100, sai ya haifi Arfakshad.
Dies ist die Geschlechterfolge Sems: Als Sem 100 Jahre alt war, zeugte er Arpaksad, zwei Jahre nach der Flut.
11 Bayan ya haifi Arfakshad, Shem ya yi shekara 500, ya haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
Und Sem lebte nach Arpaksads Zeugung 500 Jahre und zeugte noch Söhne und Töchter.
12 Sa’ad da Arfakshad ya yi shekara 35, sai ya haifi Shela.
Und Arpaksad war 35 Jahre alt; da zeugte er Selach.
13 Bayan ya haifi Shela kuwa, Arfakshad ya yi shekara 403, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
Und Arpaksad lebte nach Selachs Zeugung 403 Jahre und zeugte noch Söhne und Töchter.
14 Sa’ad da Shela ya yi shekaru 30, sai ya haifi Eber.
Und Selach war 30 Jahre alt; da zeugte er Eber.
15 Bayan ya haifi Eber, Shela ya yi shekara 403, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
Und Selach lebte nach Ebers Zeugung 403 Jahre und zeugte noch Söhne und Töchter.
16 Sa’ad da Eber ya yi shekaru 34, sai ya haifi Feleg.
Und Eber war 34 Jahre alt, da zeugte er Peleg.
17 Bayan ya haifi Feleg, Eber ya yi shekara 430, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
Und Eber lebte nach Pelegs Zeugung 430 Jahre und zeugte noch Söhne und Töchter.
18 Sa’ad da Feleg ya yi shekaru 30, sai ya haifi Reyu.
Und Peleg war 30 Jahre alt; da zeugte er Rëu.
19 Bayan ya haifi Reyu, Feleg ya yi shekara 209, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
Und Peleg lebte nach Rëus Zeugung 209 Jahre und zeugte noch Söhne und Töchter.
20 Sa’ad da Reyu ya yi shekaru 32, sai ya haifi Serug.
Und Rëu war 32 Jahre alt; da zeugte er Serug.
21 Bayan ya haifi Serug, Reyu ya yi shekara 207, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
Und Rëu lebte nach Serugs Zeugung 207 Jahre und zeugte noch Söhne und Töchter.
22 Sa’ad da Serug ya yi shekaru 30, sai ya haifi Nahor.
Und Serug war 30 Jahre alt; da zeugte er Nachor.
23 Bayan ya haifi Nahor, Serug ya yi shekara 200, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
Und Serug lebte nach Nachors Zeugung 200 Jahre und zeugte noch Söhne und Töchter.
24 Sa’ad da Nahor ya yi shekaru 29, sai ya haifi Tera.
Und Nachor war 29 Jahre alt; da zeugte er Terach.
25 Bayan ya haifi Tera, Nahor ya yi shekara 119, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
Und Nachor lebte nach Terachs Zeugung 119 Jahre und zeugte noch Söhne und Töchter.
26 Bayan Tera ya yi shekaru 70, sai ya haifi Abram, Nahor da Haran.
Und Terach war 70 Jahre alt; da zeugte er Abram, Nachor und Haran.
27 Wannan ita ce zuriyar Tera. Tera ya haifi Abram, Nahor da Haran. Haran kuma ya haifi Lot.
Dies ist die Geschlechterfolge Terachs: Terach zeugte Abram, Nachor und Haran, und Haran zeugte Lot.
28 Yayinda mahaifinsa Tera yana da rai, Haran ya rasu a Ur ta Kaldiyawa, a ƙasar haihuwarsa.
Es starb aber Haran zu Lebzeiten seines Vaters Terach, in seinem Geburtslande zu Ur Kasdim.
29 Abram da Nahor suka yi aure. Sunan matar Abram, Saira ne, sunan matar Nahor kuwa Milka; ita’yar Haran ce, mahaifin Milka da Iska.
Abram und Nachor nahmen sich dann Weiber; Abrams Weib hieß Sarai und Nachors Weib Milka, die Tochter Harans, des Vaters von Milka und Iska.
30 Saira kuwa bakararriya ce, ba ta da yara.
Sarai aber war unfruchtbar; sie hatte nie ein Kind geboren.
31 Tera ya ɗauki ɗansa Abraham, jikansa Lot ɗan Haran, da surukarsa Saira, matar Abram, tare kuwa suka bar Ur ta Kaldiyawa, don su tafi Kan’ana. Amma sa’ad da suka zo Haran sai suka zauna a can.
Und Terach nahm seinen Sohn Abram und seinen Enkel Lot, den Sohn Harans, und seine Schwiegertochter Sarai, das Weib seines Sohnes Abram, und sie zogen mit ihm aus Ur Kasdim, ins Land Kanaan zu wandern. So kamen sie bis Charan; hier aber ließen sie sich nieder.
32 Tera yi shekaru 205, ya kuma mutu a Haran.
Die Tage Terachs beliefen sich auf 205 Jahre; dann starb Terach zu Charan.