< Farawa 11 >

1 To, a lokacin, yaren mutanen duniya ɗaya ne, maganarsu kuma ɗaya ce.
Alors toute la terre avait un même langage, et une même parole.
2 Yayinda mutane suke ta yin ƙaura zuwa gabas, sai suka sami fili a Shinar, suka zauna a can.
Mais il arriva qu'étant partis d'Orient, ils trouvèrent une campagne au pays de Sinhar, où ils habitèrent.
3 Suka ce wa juna, “Ku zo, mu yi tubula, mu gasa su sosai.” Suka yi amfani da tubula a maimakon duwatsu, kwalta kuma a maimakon laka.
Et ils se dirent l'un à l'autre: Or ça, faisons des briques, et les cuisons très bien au feu. Ils eurent donc des briques au lieu de pierres, et le bitume leur fut au lieu de mortier.
4 Sa’an nan suka ce, “Ku zo, mu gina wa kanmu birni da hasumiyar da za tă kai har sammai, domin mu yi wa kanmu suna, don kada mu warwatsu ko’ina a doron ƙasa.”
Puis ils dirent: Or ça, bâtissons-nous une ville, et une tour de laquelle le sommet soit jusqu'aux cieux; et acquérons-nous de la réputation, de peur que nous ne soyons dispersés sur toute la terre.
5 Sai Ubangiji ya sauko don yă ga birni da kuma hasumiyar da mutanen suke gini.
Alors l'Eternel descendit pour voir la ville et la tour que les fils des hommes bâtissaient.
6 Ubangiji ya ce, “Ga su, su jama’a ɗaya ce, su duka kuwa harshensu guda ne. Wannan kuwa masomi ne kawai na abin da za su iya yi, babu kuma abin da suka yi shirya yi da ba za su iya yi ba.
Et l'Eternel dit: Voici, ce n'est qu'un seul et même peuple, ils ont un même langage, et ils commencent à travailler; et maintenant rien ne les empêchera d'exécuter ce qu'ils ont projeté.
7 Zo, mu sauka, mu rikitar da harshensu don kada su fahimci juna.”
Or ça, descendons, et confondons là leur langage, afin qu'ils n'entendent point le langage l'un de l'autre.
8 Saboda haka Ubangiji ya watsar da su daga wurin zuwa ko’ina a doron ƙasa, suka kuwa daina gina birnin.
Ainsi l'Eternel les dispersa de là par toute la terre, et ils cessèrent de bâtir la ville.
9 Shi ya sa aka kira birnin Babel, domin a can ne Ubangiji ya rikitar da harshen dukan duniya. Daga can Ubangiji ya watsar da su ko’ina a doron ƙasa.
C'est pourquoi son nom fut appelé Babel; car l'Eternel y confondit le langage de toute la terre, et de là il les dispersa sur toute la terre.
10 Wannan shi ne labarin Shem. Shekara biyu bayan ambaliya, sa’ad da Shem ya yi shekara 100, sai ya haifi Arfakshad.
C'est ici la postérité de Sem: Sem âgé de cent ans, engendra Arpacsad, deux ans après le déluge.
11 Bayan ya haifi Arfakshad, Shem ya yi shekara 500, ya haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
Et Sem après qu'il eut engendré Arpacsad, vécut cinq cents ans, et engendra des fils et des filles.
12 Sa’ad da Arfakshad ya yi shekara 35, sai ya haifi Shela.
Et Arpacsad vécut trente-cinq ans, et engendra Sélah.
13 Bayan ya haifi Shela kuwa, Arfakshad ya yi shekara 403, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
Et Arpacsad après qu'il eut engendré Sélah, vécut quatre cent trois ans, et engendra des fils et des filles.
14 Sa’ad da Shela ya yi shekaru 30, sai ya haifi Eber.
Et Sélah ayant vécu trente ans, engendra Héber.
15 Bayan ya haifi Eber, Shela ya yi shekara 403, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
Et Sélah après qu'il eut engendré Héber, vécut quatre cent trois ans, et engendra des fils et des filles.
16 Sa’ad da Eber ya yi shekaru 34, sai ya haifi Feleg.
Et Héber ayant vécu trente-quatre ans, engendra Péleg.
17 Bayan ya haifi Feleg, Eber ya yi shekara 430, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
Et Héber après qu'il eut engendré Péleg, vécut quatre cent trente ans, et engendra des fils et des filles.
18 Sa’ad da Feleg ya yi shekaru 30, sai ya haifi Reyu.
Et Péleg ayant vécu trente ans, engendra Réhu.
19 Bayan ya haifi Reyu, Feleg ya yi shekara 209, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
Et Péleg après qu'il eut engendré Réhu, vécut deux cent neuf ans, et engendra des fils et des filles.
20 Sa’ad da Reyu ya yi shekaru 32, sai ya haifi Serug.
Et Réhu ayant vécu trente-deux ans, engendra Sérug.
21 Bayan ya haifi Serug, Reyu ya yi shekara 207, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
Et Réhu après qu'il eut engendré Sérug, vécut deux cent sept ans, et engendra des fils et des filles.
22 Sa’ad da Serug ya yi shekaru 30, sai ya haifi Nahor.
Et Sérug ayant vécu trente ans, engendra Nacor.
23 Bayan ya haifi Nahor, Serug ya yi shekara 200, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
Et Sérug après qu'il eut engendré Nacor, vécut deux cents ans, et engendra des fils et des filles.
24 Sa’ad da Nahor ya yi shekaru 29, sai ya haifi Tera.
Et Nacor ayant vécu vingt-neuf ans, engendra Taré.
25 Bayan ya haifi Tera, Nahor ya yi shekara 119, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
Et Nacor après qu'il eut engendré Taré, vécut cent dix-neuf ans, et engendra des fils et des filles.
26 Bayan Tera ya yi shekaru 70, sai ya haifi Abram, Nahor da Haran.
Et Taré ayant vécu soixante-dix ans, engendra Abram, Nacor, et Haran.
27 Wannan ita ce zuriyar Tera. Tera ya haifi Abram, Nahor da Haran. Haran kuma ya haifi Lot.
Et c'est ici la postérité de Taré: Taré engendra Abram, Nacor, et Haran; et Haran engendra Lot.
28 Yayinda mahaifinsa Tera yana da rai, Haran ya rasu a Ur ta Kaldiyawa, a ƙasar haihuwarsa.
Et Haran mourut en la présence de son père, au pays de sa naissance, à Ur des Chaldéens.
29 Abram da Nahor suka yi aure. Sunan matar Abram, Saira ne, sunan matar Nahor kuwa Milka; ita’yar Haran ce, mahaifin Milka da Iska.
Et Abram et Nacor prirent chacun une femme. Le nom de la femme d'Abram fut Saraï; et le nom de la femme de Nacor fut Milca, fille de Haran, père de Milca et de Jisca.
30 Saira kuwa bakararriya ce, ba ta da yara.
Et Saraï était stérile, [et] n'avait point d'enfants.
31 Tera ya ɗauki ɗansa Abraham, jikansa Lot ɗan Haran, da surukarsa Saira, matar Abram, tare kuwa suka bar Ur ta Kaldiyawa, don su tafi Kan’ana. Amma sa’ad da suka zo Haran sai suka zauna a can.
Et Taré prit son fils Abram, et Lot fils de son fils, [qui était] fils de Haran, et Saraï sa belle-fille, femme d'Abram son fils, et ils sortirent ensemble d'Ur des Chaldéens pour aller au pays de Canaan, et ils vinrent jusqu'à Caran, et y demeurèrent.
32 Tera yi shekaru 205, ya kuma mutu a Haran.
Et les jours de Taré furent deux cent cinq ans; puis il mourut à Caran.

< Farawa 11 >