< Farawa 11 >
1 To, a lokacin, yaren mutanen duniya ɗaya ne, maganarsu kuma ɗaya ce.
Et toute la terre avait une seule langue et les mêmes paroles.
2 Yayinda mutane suke ta yin ƙaura zuwa gabas, sai suka sami fili a Shinar, suka zauna a can.
Et il arriva que lorsqu’ils partirent de l’orient, ils trouvèrent une plaine dans le pays de Shinhar; et ils y habitèrent.
3 Suka ce wa juna, “Ku zo, mu yi tubula, mu gasa su sosai.” Suka yi amfani da tubula a maimakon duwatsu, kwalta kuma a maimakon laka.
Et ils se dirent l’un à l’autre: Allons, faisons des briques, et cuisons-les au feu. Et ils avaient la brique pour pierre, et ils avaient le bitume pour mortier.
4 Sa’an nan suka ce, “Ku zo, mu gina wa kanmu birni da hasumiyar da za tă kai har sammai, domin mu yi wa kanmu suna, don kada mu warwatsu ko’ina a doron ƙasa.”
Et ils dirent: Allons, bâtissons-nous une ville, et une tour dont le sommet [atteigne] jusqu’aux cieux; et faisons-nous un nom, de peur que nous ne soyons dispersés sur la face de toute la terre.
5 Sai Ubangiji ya sauko don yă ga birni da kuma hasumiyar da mutanen suke gini.
Et l’Éternel descendit pour voir la ville et la tour que bâtissaient les fils des hommes.
6 Ubangiji ya ce, “Ga su, su jama’a ɗaya ce, su duka kuwa harshensu guda ne. Wannan kuwa masomi ne kawai na abin da za su iya yi, babu kuma abin da suka yi shirya yi da ba za su iya yi ba.
Et l’Éternel dit: Voici, c’est un seul peuple, et ils n’ont, eux tous, qu’un seul langage, et ils ont commencé à faire ceci; et maintenant ils ne seront empêchés en rien de ce qu’ils pensent faire.
7 Zo, mu sauka, mu rikitar da harshensu don kada su fahimci juna.”
Allons, descendons, et confondons là leur langage, afin qu’ils n’entendent pas le langage l’un de l’autre.
8 Saboda haka Ubangiji ya watsar da su daga wurin zuwa ko’ina a doron ƙasa, suka kuwa daina gina birnin.
Et l’Éternel les dispersa de là sur la face de toute la terre; et ils cessèrent de bâtir la ville.
9 Shi ya sa aka kira birnin Babel, domin a can ne Ubangiji ya rikitar da harshen dukan duniya. Daga can Ubangiji ya watsar da su ko’ina a doron ƙasa.
C’est pourquoi on appela son nom Babel, car là l’Éternel confondit le langage de toute la terre; et de là l’Éternel les dispersa sur la face de toute la terre.
10 Wannan shi ne labarin Shem. Shekara biyu bayan ambaliya, sa’ad da Shem ya yi shekara 100, sai ya haifi Arfakshad.
Ce sont ici les générations de Sem: Sem était âgé de 100 ans, et il engendra Arpacshad, deux ans après le déluge.
11 Bayan ya haifi Arfakshad, Shem ya yi shekara 500, ya haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
Et Sem, après qu’il eut engendré Arpacshad, vécut 500 ans; et il engendra des fils et des filles.
12 Sa’ad da Arfakshad ya yi shekara 35, sai ya haifi Shela.
Et Arpacshad vécut 35 ans, et engendra Shélakh.
13 Bayan ya haifi Shela kuwa, Arfakshad ya yi shekara 403, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
Et Arpacshad, après qu’il eut engendré Shélakh, vécut 403 ans; et il engendra des fils et des filles.
14 Sa’ad da Shela ya yi shekaru 30, sai ya haifi Eber.
Et Shélakh vécut 30 ans, et engendra Héber.
15 Bayan ya haifi Eber, Shela ya yi shekara 403, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
Et Shélakh, après qu’il eut engendré Héber, vécut 403 ans; et il engendra des fils et des filles.
16 Sa’ad da Eber ya yi shekaru 34, sai ya haifi Feleg.
Et Héber vécut 34 ans, et engendra Péleg.
17 Bayan ya haifi Feleg, Eber ya yi shekara 430, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
Et Héber, après qu’il eut engendré Péleg, vécut 430 ans; et il engendra des fils et des filles.
18 Sa’ad da Feleg ya yi shekaru 30, sai ya haifi Reyu.
Et Péleg vécut 30 ans, et engendra Rehu.
19 Bayan ya haifi Reyu, Feleg ya yi shekara 209, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
Et Péleg, après qu’il eut engendré Rehu, vécut 209 ans; et il engendra des fils et des filles.
20 Sa’ad da Reyu ya yi shekaru 32, sai ya haifi Serug.
Et Rehu vécut 32 ans, et engendra Serug.
21 Bayan ya haifi Serug, Reyu ya yi shekara 207, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
Et Rehu, après qu’il eut engendré Serug, vécut 207 ans; et il engendra des fils et des filles.
22 Sa’ad da Serug ya yi shekaru 30, sai ya haifi Nahor.
Et Serug vécut 30 ans, et engendra Nakhor.
23 Bayan ya haifi Nahor, Serug ya yi shekara 200, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
Et Serug, après qu’il eut engendré Nakhor, vécut 200 ans; et il engendra des fils et des filles.
24 Sa’ad da Nahor ya yi shekaru 29, sai ya haifi Tera.
Et Nakhor vécut 29 ans, et engendra Térakh.
25 Bayan ya haifi Tera, Nahor ya yi shekara 119, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
Et Nakhor, après qu’il eut engendré Térakh, vécut 119 ans; et il engendra des fils et des filles.
26 Bayan Tera ya yi shekaru 70, sai ya haifi Abram, Nahor da Haran.
Et Térakh vécut 70 ans, et engendra Abram, Nakhor, et Haran.
27 Wannan ita ce zuriyar Tera. Tera ya haifi Abram, Nahor da Haran. Haran kuma ya haifi Lot.
Et ce sont ici les générations de Térakh: Térakh engendra Abram, Nakhor, et Haran. Et Haran engendra Lot.
28 Yayinda mahaifinsa Tera yana da rai, Haran ya rasu a Ur ta Kaldiyawa, a ƙasar haihuwarsa.
Et Haran mourut en la présence de Térakh, son père, au pays de sa naissance, à Ur des Chaldéens.
29 Abram da Nahor suka yi aure. Sunan matar Abram, Saira ne, sunan matar Nahor kuwa Milka; ita’yar Haran ce, mahaifin Milka da Iska.
– Et Abram et Nakhor prirent des femmes: le nom de la femme d’Abram était Saraï, et le nom de la femme de Nakhor, Milca, fille de Haran, père de Milca et père de Jisca.
30 Saira kuwa bakararriya ce, ba ta da yara.
Et Saraï était stérile, elle n’avait pas d’enfants.
31 Tera ya ɗauki ɗansa Abraham, jikansa Lot ɗan Haran, da surukarsa Saira, matar Abram, tare kuwa suka bar Ur ta Kaldiyawa, don su tafi Kan’ana. Amma sa’ad da suka zo Haran sai suka zauna a can.
Et Térakh prit Abram son fils, et Lot, fils de Haran, fils de son fils, et Saraï, sa belle-fille, femme d’Abram, son fils; et ils sortirent ensemble d’Ur des Chaldéens pour aller au pays de Canaan; et ils vinrent jusqu’à Charan, et habitèrent là.
32 Tera yi shekaru 205, ya kuma mutu a Haran.
Et les jours de Térakh furent 205 ans; et Térakh mourut à Charan.